- 
                        
                             سوره : 
                             Suratus Shu’ara 
                        
                    
- 
                        
                             جزء: 
                            19
                        
                    
- 
                        
                            عدد آيات : 
                             227 
                        
                    
- 
                        
                            شماره آيه : 
                            
                        
                    
 
            
         
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   1 
    
    
        
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                        
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   2 
    
    
        
            
                 تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ
                
                    Waxannan ayoyi ne na Littafi mabayyani
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   3 
    
    
        
            
                 لَعَلَّكَ بَٰخِعٞ نَّفۡسَكَ أَلَّا يَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ
                
                    Ko za ka kashe kanka ne don ba su zama muminai ba?
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   4 
    
    
        
            
                 إِن نَّشَأۡ نُنَزِّلۡ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةٗ فَظَلَّتۡ أَعۡنَٰقُهُمۡ لَهَا خَٰضِعِينَ
                
                    Da Mun ga dama da sai Mu saukar musu da aya daga sama sai wuyoyinsu su zamo masu qanqan da kai gare ta[1]
                
             
            
            
1-  Watau mu’ujizar da za ta tilasta musu su miqa wuya ko ba sa so.            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   5 
    
    
        
            
                 وَمَا يَأۡتِيهِم مِّن ذِكۡرٖ مِّنَ ٱلرَّحۡمَٰنِ مُحۡدَثٍ إِلَّا كَانُواْ عَنۡهُ مُعۡرِضِينَ
                
                    Kuma ba wani wa’azi sabo da zai zo musu daga (Allah) Mai rahama sai sun kasance masu bijire masa
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   6 
    
    
        
            
                 فَقَدۡ كَذَّبُواْ فَسَيَأۡتِيهِمۡ أَنۢبَـٰٓؤُاْ مَا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ
                
                    To haqiqa sun qaryata, ba da daxewa ba labaran aqibar abin da suke yi wa izgili za su zo musu
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   7 
    
    
        
            
                 أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَمۡ أَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجٖ كَرِيمٍ
                
                    Shin ba su yi duba zuwa ga qasa ba, (su ga) dangogin tsirrai masu kyau nawa ne Muka tsirar daga cikinta?
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   8 
    
    
        
            
                 إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
                
                    Lalle a game da wannan tabbas akwai aya (mai nuna cikar ikon Allah); kuma yawancinsu ba su zamanto masu imani ba
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   9 
    
    
        
            
                 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
                
                    Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi Mabuwayi ne, Mai rahama
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   10 
    
    
        
            
                 وَإِذۡ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئۡتِ ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ
                
                    Kuma (ka tuna) lokacin da Ubangijinka Ya kira Musa cewa: “Ka tafi wajen mutanen nan azzalumai
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   11 
    
    
        
            
                 قَوۡمَ فِرۡعَوۡنَۚ أَلَا يَتَّقُونَ
                
                    “(Watau) mutanen Fir’auna. Yanzu ba za su kiyaye dokokin Allah ba?”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   12 
    
    
        
            
                 قَالَ رَبِّ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ
                
                    (Musa) ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni ina tsoron su qaryata ni
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   13 
    
    
        
            
                 وَيَضِيقُ صَدۡرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرۡسِلۡ إِلَىٰ هَٰرُونَ
                
                    “Kuma qirjina yana quntata, kuma harshena ba ya sakuwa, sai Ka aika zuwa ga (xan’uwana) Haruna
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   14 
    
    
        
            
                 وَلَهُمۡ عَلَيَّ ذَنۢبٞ فَأَخَافُ أَن يَقۡتُلُونِ
                
                    “Ni kuma akwai wani laifi da na yi musu, sai nake tsoron su kashe ni.”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   15 
    
    
        
            
                 قَالَ كَلَّاۖ فَٱذۡهَبَا بِـَٔايَٰتِنَآۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسۡتَمِعُونَ
                
                    (Allah) Ya ce: “A’a; (ba abin da zai same ka), sai ku tafi (kai da xan’uwanka) da ayoyinmu; lalle Mu masu jin (komai da zai faru) ne tare da ku
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   16 
    
    
        
            
                 فَأۡتِيَا فِرۡعَوۡنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
                
                    “Ku je wajen Fir’auna sai ku faxa masa cewa: ‘Lalle mu manzannin Ubangijin talikai ne
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   17 
    
    
        
            
                 أَنۡ أَرۡسِلۡ مَعَنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ
                
                    “‘Cewa, ka sako mana da Banu-Isra’ila’.”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   18 
    
    
        
            
                 قَالَ أَلَمۡ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدٗا وَلَبِثۡتَ فِينَا مِنۡ عُمُرِكَ سِنِينَ
                
                    (Fir’auna) ya ce: “Yanzu ba mu muka raine ka a cikinmu tun kana jariri ba, kuma ka zauna ka yi wasu shekaru na rayuwarka a cikinmu?
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   19 
    
    
        
            
                 وَفَعَلۡتَ فَعۡلَتَكَ ٱلَّتِي فَعَلۡتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ
                
                    “Ka kuma aikata aika-aikarka da ka aikata[1] alhali kuwa kana daga masu butulce wa (ni’imata)?”
                
             
            
            
1-  Yana nufin kashe Baqibxe da ya yi lokacin da ya same shi yana faxa da Ba’isra’ile. Duba Suratul Qasas, ayat ta 15.            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   20 
    
    
        
            
                 قَالَ فَعَلۡتُهَآ إِذٗا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
                
                    (Musa) ya ce: “Na aikata haka ne a lokacin ina cikin marasa shiriya (ta rashin wahayi)
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   21 
    
    
        
            
                 فَفَرَرۡتُ مِنكُمۡ لَمَّا خِفۡتُكُمۡ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكۡمٗا وَجَعَلَنِي مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
                
                    “Sannan na guje muku lokacin da na tsorata da ku, sai Ubangijina Ya ba ni kyautar ilimi Ya kuma sanya ni daga manzanni
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   22 
    
    
        
            
                 وَتِلۡكَ نِعۡمَةٞ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنۡ عَبَّدتَّ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ
                
                    “Waccen ni’imar kuwa da kake goranta min ita saboda ka bautar da Bani-Isra’ila ne.”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   23 
    
    
        
            
                 قَالَ فِرۡعَوۡنُ وَمَا رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
                
                    Fir’auna ya ce: “To wane ne Ubangijin talikai?”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   24 
    
    
        
            
                 قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
                
                    (Musa) ya ce: “(Shi ne) Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu, idan har kun kasance masu sakankancewa (da hakan)”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   25 
    
    
        
            
                 قَالَ لِمَنۡ حَوۡلَهُۥٓ أَلَا تَسۡتَمِعُونَ
                
                    (Fir’auna) ya ce da waxanda suke kewaye da shi: “Shin ba kwa jin (abin da yake faxa)?”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   26 
    
    
        
            
                 قَالَ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ
                
                    (Musa) ya ce: “Shi ne Ubangijinku kuma Ubangijin iyayenku na farko!”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   27 
    
    
        
            
                 قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِيٓ أُرۡسِلَ إِلَيۡكُمۡ لَمَجۡنُونٞ
                
                    (Fir’auna) ya ce: “Lalle Manzon da aka aiko muku tabbas mai tavin hankali ne!”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   28 
    
    
        
            
                 قَالَ رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡقِلُونَ
                
                    (Musa) ya ce: “(Shi ne) Ubangijin mahudar rana da mafaxarta da kuma abin da yake tsakaninsu; in kun zamanto masu hankalta.”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   29 
    
    
        
            
                 قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذۡتَ إِلَٰهًا غَيۡرِي لَأَجۡعَلَنَّكَ مِنَ ٱلۡمَسۡجُونِينَ
                
                    (Fir’auna) ya ce: “Na rantse in har ka riqi wani abin bauta ba ni ba, tabbas zan jefa ka cikin ‘yan kurkuku!”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
- 
                            
                        
 
                
                                    
             
         
     
 
    
        
            سوره:
              Suratus Shu’ara 
        
        آيه :   30 
    
    
        
            
                 قَالَ أَوَلَوۡ جِئۡتُكَ بِشَيۡءٖ مُّبِينٖ
                
                    (Musa) ya ce: “Ko da na zo maka da wani abu bayyananne?”
                
             
            
            
            
         
        
        
            
                
                    
                        - 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                         
 
 
 
- 
                            
                                
                            
                            
                                
                                    
                                        
                                        
                                            
                                            
                                            
                                            تمام خطا 
 
 
 
 
-