سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 1

سَأَلَ سَآئِلُۢ بِعَذَابٖ وَاقِعٖ

Mai tambaya ya yi tambaya game da wata azaba mai aukuwa[1]


1- Watau wadda Annabi () yake musu kashedi da ita idan sun qi imani. Duba Suratul Anfal, aya ta 32. Mai tambayar kuwa shi ne Nadhru xan Haris.


سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 2

لِّلۡكَٰفِرِينَ لَيۡسَ لَهُۥ دَافِعٞ

Ga kafirai (wadda) ba ta da wani mai kaxe ta



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِي ٱلۡمَعَارِجِ

Daga Allah Mai matattakalai



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 4

تَعۡرُجُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيۡهِ فِي يَوۡمٖ كَانَ مِقۡدَارُهُۥ خَمۡسِينَ أَلۡفَ سَنَةٖ

Mala’iku tare da Jibrilu suna hawa zuwa gare Shi a cikin wata rana (wadda) gwargwadonta yake daidai da shekara dubu hamsin



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 5

فَٱصۡبِرۡ صَبۡرٗا جَمِيلًا

Sai ka yi haquri kyakkyawan haquri



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 6

إِنَّهُمۡ يَرَوۡنَهُۥ بَعِيدٗا

Lalle su suna ganin ta mai nisa ce



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبٗا

Mu kuma Muna ganin ta kusa-kusa



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 8

يَوۡمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلۡمُهۡلِ

A ranar da sama za ta kasance kamar narkakkiyar dalma



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 9

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga (ta gashin tumaki)



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 10

وَلَا يَسۡـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمٗا

Kuma aboki ba ya tambayar aboki



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 11

يُبَصَّرُونَهُمۡۚ يَوَدُّ ٱلۡمُجۡرِمُ لَوۡ يَفۡتَدِي مِنۡ عَذَابِ يَوۡمِئِذِۭ بِبَنِيهِ

(Alhali kuma) ana nuna musu junansu. Mai laifi ya riqa burin ina ma zai fanshi kansa daga azabar wannan rana da ‘ya’yansa



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 12

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

Da matarsa da xan’uwansa



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِي تُـٔۡوِيهِ

Da danginsa waxanda suke kare shi



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 14

وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ يُنجِيهِ

Da ma duk wanda yake a bayan qasa baki xaya, sannan (fansar) ta tserar da shi



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 17

تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ

Tana kiran wanda ya juya ya ba da baya



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 18

وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ

Ya kuma tara (dukiya) sai ya voye (ta)



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 19

۞إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا

Lalle mutum an halicce shi mai rashin nutsuwa ne



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 20

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعٗا

(Watau) idan sharri ya same shi ya zama mai raki



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 21

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلۡخَيۡرُ مَنُوعًا

Idan kuma alheri ya same shi ya zama mai maqo



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 22

إِلَّا ٱلۡمُصَلِّينَ

Sai dai masallata



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 23

ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ

Waxanda suke masu dawwama a kan sallarsu



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 24

وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ

Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

Ga mai roqo da wanda ake hana wa (saboda ba ya roqo)



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

Waxanda kuma suke gaskata ranar sakamako



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ

Waxanda kuma suke tsoron azabar Ubangijinsu



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ

Lalle azabar Ubangijinsu ba abar amincewa ba ce



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 29

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye al’aurarsu (daga yin zina)



سوره: Suratul Ma’arij

آيه : 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne