Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 29

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ لَكُم مَّا فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰٓ إِلَى ٱلسَّمَآءِ فَسَوَّىٰهُنَّ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖۚ وَهُوَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Shi ne wanda Ya halitta muku abin da yake cikin qasa gaba xaya, sannan Ya nufi sama Ya daidaita su sammai bakwai, kuma Shi Masanin komai ne



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 2

ٱللَّهُ ٱلَّذِي رَفَعَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ بِغَيۡرِ عَمَدٖ تَرَوۡنَهَاۖ ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰ عَلَى ٱلۡعَرۡشِۖ وَسَخَّرَ ٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَۖ كُلّٞ يَجۡرِي لِأَجَلٖ مُّسَمّٗىۚ يُدَبِّرُ ٱلۡأَمۡرَ يُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّكُم بِلِقَآءِ رَبِّكُمۡ تُوقِنُونَ

Allah Wanda Ya xaukaka sammai ba tare da wasu ginshiqai da kuke ganinsu ba; sannan Ya daidaita bisa Al’arshi[1]; Ya kuma hore muku rana da wata; kowannensu yana gudu zuwa wani lokaci qayyadadde. Yana shirya al’amari, Yana bayyana ayoyi don ku sakankance da haxuwarku da Ubangijinku


1- Duba Suratul A’araf aya ta 54, hashiya ta 126.


Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 51

۞مَّآ أَشۡهَدتُّهُمۡ خَلۡقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَلَا خَلۡقَ أَنفُسِهِمۡ وَمَا كُنتُ مُتَّخِذَ ٱلۡمُضِلِّينَ عَضُدٗا

Ban halarto da su ba lokacin halittar sammai da qasa, ko ma halittar kawunansu, ban kuma kasance Mai riqon masu vatarwa mataimaka ba



Capítulo: Suratul Anbiya

Verso : 30

أَوَلَمۡ يَرَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَنَّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ كَانَتَا رَتۡقٗا فَفَتَقۡنَٰهُمَاۖ وَجَعَلۡنَا مِنَ ٱلۡمَآءِ كُلَّ شَيۡءٍ حَيٍّۚ أَفَلَا يُؤۡمِنُونَ

Yanzu waxanda suka kafirta ba sa ganin cewa a da can sammai da qasa a haxe suke, sannan Muka raba su[1]; Muka kuma halicci duk wani abu mai rai daga ruwa? To me ya sa ba za su yi imani ba?


1- Watau Allah () ya fara halittar sammai da qasa a manne da juna daga bisani ya raba tsakaninsu.


Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 59

ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰ عَلَى ٱلۡعَرۡشِۖ ٱلرَّحۡمَٰنُ فَسۡـَٔلۡ بِهِۦ خَبِيرٗا

(Shi ne) wanda Ya halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu cikin kwana shida, sannan Ya daidaita a kan Al’arshi. (Shi ne) Arrahmanu, sai ka tambayi Masani game da Shi



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 44

خَلَقَ ٱللَّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ

Allah Ya halicci sammai da qasa da gaskiya. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga muminai



Capítulo: Suratus Sajda

Verso : 4

ٱللَّهُ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰ عَلَى ٱلۡعَرۡشِۖ مَا لَكُم مِّن دُونِهِۦ مِن وَلِيّٖ وَلَا شَفِيعٍۚ أَفَلَا تَتَذَكَّرُونَ

Allah ne Wanda Ya halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu cikin kwana shida sannan Ya daidaita bisa Al’arshi; ba ku da wani majivincin al’amari ko mai ceto bayansa. Yanzu me ya sa ba kwa wa’azantuwa?



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 57

لَخَلۡقُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ أَكۡبَرُ مِنۡ خَلۡقِ ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Tabbas halittar sammai da qasa ta fi girma a kan halittar mutane, sai dai kuma yawancin mutane ba sa sanin (haka)



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 11

ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰٓ إِلَى ٱلسَّمَآءِ وَهِيَ دُخَانٞ فَقَالَ لَهَا وَلِلۡأَرۡضِ ٱئۡتِيَا طَوۡعًا أَوۡ كَرۡهٗا قَالَتَآ أَتَيۡنَا طَآئِعِينَ

“Sannan Ya nufi zuwa sama, (a sannan) ita kuma hayaqi ce, sai Ya ce da ita da kuma qasa: “Ku zo cikin biyayya ko kuma bisa tilas.” Suka ce: ‘Mun zo muna masu biyayya’



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 12

فَقَضَىٰهُنَّ سَبۡعَ سَمَٰوَاتٖ فِي يَوۡمَيۡنِ وَأَوۡحَىٰ فِي كُلِّ سَمَآءٍ أَمۡرَهَاۚ وَزَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِمَصَٰبِيحَ وَحِفۡظٗاۚ ذَٰلِكَ تَقۡدِيرُ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡعَلِيمِ

“Sai Ya mayar da su sammai bakwai a cikin kwana biyu, Ya kuma yi wa kowacce sama wahayin umarninta. Muka kuma qawata saman duniya da taurari da kuma tsaro[1]. Wannan tsari ne na Allah Mabuwayi, Masani.”


1- Watau daga aljannu masu qoqarin satar sauraro.


Capítulo: Suratu Qaf 

Verso : 38

وَلَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ وَمَا مَسَّنَا مِن لُّغُوبٖ

Haqiqa kuma Mun halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu cikin kwana shida, kuma wata gajiya ba ta shafe mu ba



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 9

يَوۡمَ تَمُورُ ٱلسَّمَآءُ مَوۡرٗا

A ranar da sama za ta yi matsananciyar jujjuyawa



Capítulo: Suratux Xalaq

Verso : 12

ٱللَّهُ ٱلَّذِي خَلَقَ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ وَمِنَ ٱلۡأَرۡضِ مِثۡلَهُنَّۖ يَتَنَزَّلُ ٱلۡأَمۡرُ بَيۡنَهُنَّ لِتَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ وَأَنَّ ٱللَّهَ قَدۡ أَحَاطَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عِلۡمَۢا

Allah ne Wanda Ya halicci sammai bakwai, qasa ma Ya halicci kwatankwacinsu (watau sammai), umarni yana sauka a tsakaninsu, don ku san cewa, Allah Mai iko ne a kan komai, kuma haqiqa Allah iliminsa ya kewaye kowane abu



Capítulo: Suratu Nuh

Verso : 15

أَلَمۡ تَرَوۡاْ كَيۡفَ خَلَقَ ٱللَّهُ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ طِبَاقٗا

“Shin ba kwa ganin yadda Allah Ya halicci sammai bakwai rufi-rufi?



Capítulo: Suratu Nuh

Verso : 16

وَجَعَلَ ٱلۡقَمَرَ فِيهِنَّ نُورٗا وَجَعَلَ ٱلشَّمۡسَ سِرَاجٗا

“Ya kuma sanya wata mai haske a cikinsu; rana kuma Ya sanya ta fitila?



Capítulo: Suratut Takwir

Verso : 1

إِذَا ٱلشَّمۡسُ كُوِّرَتۡ

Idan rana aka naxe ta[1]


1- Watau aka haxa ta da wata wuri xaya, aka kuma tafiyar da haskenta.


Capítulo: Suratut Takwir

Verso : 2

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتۡ

Idan kuma taurari suka farfaxo