Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 71

وَسِيقَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِلَىٰ جَهَنَّمَ زُمَرًاۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءُوهَا فُتِحَتۡ أَبۡوَٰبُهَا وَقَالَ لَهُمۡ خَزَنَتُهَآ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ رُسُلٞ مِّنكُمۡ يَتۡلُونَ عَلَيۡكُمۡ ءَايَٰتِ رَبِّكُمۡ وَيُنذِرُونَكُمۡ لِقَآءَ يَوۡمِكُمۡ هَٰذَاۚ قَالُواْ بَلَىٰ وَلَٰكِنۡ حَقَّتۡ كَلِمَةُ ٱلۡعَذَابِ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Aka kuma ingiza qeyar waxanda suka kafirta zuwa (wutar) Jahannama qungiya-qungiya; har yayin da suka zo wurinta sai aka buxe qofofinta, masu tsaronta suka ce (da su): “Yanzu manzanni daga cikinku ba su zo muku ba ne suna karanta muku ayoyin Ubangijinku, suna kuma gargaxin ku game da haxuwa da wannan ranar taku?” Sai suka ce: “Haka ne, (sun zo mana),” sai dai kuma kalmar azaba ta tabbata a kan kafirai.”



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 49

وَقَالَ ٱلَّذِينَ فِي ٱلنَّارِ لِخَزَنَةِ جَهَنَّمَ ٱدۡعُواْ رَبَّكُمۡ يُخَفِّفۡ عَنَّا يَوۡمٗا مِّنَ ٱلۡعَذَابِ

Kuma waxanda suke cikin wuta suka ce da masu tsaron Jahannama: “Ku roqa mana Ubangijinku mana Ya sauqaqe mana azaba ta wuni (xaya).”



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 50

قَالُوٓاْ أَوَلَمۡ تَكُ تَأۡتِيكُمۡ رُسُلُكُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِۖ قَالُواْ بَلَىٰۚ قَالُواْ فَٱدۡعُواْۗ وَمَا دُعَـٰٓؤُاْ ٱلۡكَٰفِرِينَ إِلَّا فِي ضَلَٰلٍ

Suka ce: “Yanzu manzanninku ba su kasance suna zo muku da (ayoyi) bayyanannu ba?” Suka ce: “Haka ne (sun zo)”. Sai su ce: “To sai ku yi ta roqon. Roqon kafirai kuwa bai zamo ba sai a tave.”



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 77

وَنَادَوۡاْ يَٰمَٰلِكُ لِيَقۡضِ عَلَيۡنَا رَبُّكَۖ قَالَ إِنَّكُم مَّـٰكِثُونَ

Suka kuma yi kiran: “Ya (kai mai tsaron wuta) Maliku, Ubangijinka Ya kashe mu mana!” Ya ce: “Lalle ku masu dawwama ne.”



Capítulo: Suratut Tahrim

Verso : 6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ قُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ وَأَهۡلِيكُمۡ نَارٗا وَقُودُهَا ٱلنَّاسُ وَٱلۡحِجَارَةُ عَلَيۡهَا مَلَـٰٓئِكَةٌ غِلَاظٞ شِدَادٞ لَّا يَعۡصُونَ ٱللَّهَ مَآ أَمَرَهُمۡ وَيَفۡعَلُونَ مَا يُؤۡمَرُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kare kawunanku da iyalanku daga wuta (wadda) makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa sava wa Allah abin da Ya umarce su, suna kuma aikata abin da ake umartar su



Capítulo: Suratul Mulk

Verso : 8

تَكَادُ تَمَيَّزُ مِنَ ٱلۡغَيۡظِۖ كُلَّمَآ أُلۡقِيَ فِيهَا فَوۡجٞ سَأَلَهُمۡ خَزَنَتُهَآ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ نَذِيرٞ

Tana kusa da ta kekkece saboda tsananin fushi; duk sanda aka jefa wata tawaga a cikinta sai masu tsaron ta su tambaye su: “Shin mai gargaxi bai zo muku ba?”



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 30

عَلَيۡهَا تِسۡعَةَ عَشَرَ

Akwai (mala’iku) goma sha tara suna tsaron ta



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 18

سَنَدۡعُ ٱلزَّبَانِيَةَ

Mu kuma lalle za Mu kirawo (mala’iku) zabaniyawa