Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 56

وَٱذۡكُرۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ إِدۡرِيسَۚ إِنَّهُۥ كَانَ صِدِّيقٗا نَّبِيّٗا

Kuma ka ambaci (labarin) Idrisu a cikin (wannan) Littafi (Alqur’ani). Lalle shi ya kasance mai yawan gaskiya ne, Annabi



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 57

وَرَفَعۡنَٰهُ مَكَانًا عَلِيًّا

Muka kuma xaukaka shi daraja maxaukakiya[1]


1- A Mi’iraji da Annabi () ya yi ya haxu da shi a sama ta huxu.


Capítulo: Suratul Anbiya

Verso : 85

وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِدۡرِيسَ وَذَا ٱلۡكِفۡلِۖ كُلّٞ مِّنَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

(Ka tuna) kuma Isma’ila da Idrisa da kuma Zulkifli; dukkansu suna cikin masu haquri