Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 125

وَإِذۡ جَعَلۡنَا ٱلۡبَيۡتَ مَثَابَةٗ لِّلنَّاسِ وَأَمۡنٗا وَٱتَّخِذُواْ مِن مَّقَامِ إِبۡرَٰهِـۧمَ مُصَلّٗىۖ وَعَهِدۡنَآ إِلَىٰٓ إِبۡرَٰهِـۧمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ أَن طَهِّرَا بَيۡتِيَ لِلطَّآئِفِينَ وَٱلۡعَٰكِفِينَ وَٱلرُّكَّعِ ٱلسُّجُودِ

Kuma ka tuna lokacin da Muka sanya wannan Xaki ya zama matattara ga mutane da kuma aminci; kuma ku mayar da Maqamu Ibrahim wajen salla; kuma Muka yi umarni ga Ibrahim da Isma’ila da cewa: “Ku tsarkake Xakina don masu xawafi da masu i’itikafi da masu ruku’u da sujjada”



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 126

وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ رَبِّ ٱجۡعَلۡ هَٰذَا بَلَدًا ءَامِنٗا وَٱرۡزُقۡ أَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلثَّمَرَٰتِ مَنۡ ءَامَنَ مِنۡهُم بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۚ قَالَ وَمَن كَفَرَ فَأُمَتِّعُهُۥ قَلِيلٗا ثُمَّ أَضۡطَرُّهُۥٓ إِلَىٰ عَذَابِ ٱلنَّارِۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu ya ce: “Ya Ubangijina, Ka sanya wannan (wuri) ya zama gari mai aminci, kuma Ka arzuta mutanensa da kayan marmari, (amma) wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira daga cikinsu”. Sai (Allah) Ya ce: “Har ma wanda ya kafirta, zan jiyar da shi daxi kaxan, sannan in tilasa masa shiga azabar wuta, tir da wannan makoma.”



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 127

وَإِذۡ يَرۡفَعُ إِبۡرَٰهِـۧمُ ٱلۡقَوَاعِدَ مِنَ ٱلۡبَيۡتِ وَإِسۡمَٰعِيلُ رَبَّنَا تَقَبَّلۡ مِنَّآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu yake xaga harsashen ginin Xakin Ka’aba tare da Isma’ila, suna cewa: “Ya Ubangijinmu Ka karva mana; lalle Kai Mai ji ne Mai gani.”



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 128

رَبَّنَا وَٱجۡعَلۡنَا مُسۡلِمَيۡنِ لَكَ وَمِن ذُرِّيَّتِنَآ أُمَّةٗ مُّسۡلِمَةٗ لَّكَ وَأَرِنَا مَنَاسِكَنَا وَتُبۡ عَلَيۡنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

“Ya Ubangijinmu, Ka sanya mu masu miqa wuya gare Ka, kuma a cikin zurriyarmu ma (Ka samar) da wata al’umma mai miqa wuya gare Ka, kuma Ka nuna mana ayyaukan ibadarmu, kuma Ka karvi tubanmu, lalle Kai Mai yawan karvar tuba ne Mai jin qai.”



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 129

رَبَّنَا وَٱبۡعَثۡ فِيهِمۡ رَسُولٗا مِّنۡهُمۡ يَتۡلُواْ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتِكَ وَيُعَلِّمُهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَيُزَكِّيهِمۡۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

“Ya Ubangijinmu, Ka aiko da wani manzo daga cikinsu, da zai riqa karanta musu ayoyinka, kuma yana koyar da su Littafi da hikima, kuma ya riqa yi musu tarbiyya. Lalle kai Mabuwayi ne, Mai hikima.”



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 133

أَمۡ كُنتُمۡ شُهَدَآءَ إِذۡ حَضَرَ يَعۡقُوبَ ٱلۡمَوۡتُ إِذۡ قَالَ لِبَنِيهِ مَا تَعۡبُدُونَ مِنۢ بَعۡدِيۖ قَالُواْ نَعۡبُدُ إِلَٰهَكَ وَإِلَٰهَ ءَابَآئِكَ إِبۡرَٰهِـۧمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَ إِلَٰهٗا وَٰحِدٗا وَنَحۡنُ لَهُۥ مُسۡلِمُونَ

Ko kuna nan ne lokacin da mutuwa ta zo wa Ya’aqubu, lokacin da ya ce wa ‘ya’yansa: “Me za ku bauta wa a bayana?” Sai suka ce: “Za mu bauta wa abin bautarka kuma abin bautar iyayenka, Ibrahim da Isma’il da Ishaq, abin bauta guda xaya, kuma mu gare Shi muke miqa wuya.”



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 163

۞إِنَّآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ كَمَآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ نُوحٖ وَٱلنَّبِيِّـۧنَ مِنۢ بَعۡدِهِۦۚ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ وَٱلۡأَسۡبَاطِ وَعِيسَىٰ وَأَيُّوبَ وَيُونُسَ وَهَٰرُونَ وَسُلَيۡمَٰنَۚ وَءَاتَيۡنَا دَاوُۥدَ زَبُورٗا

Lalle Mun yi maka wahayi irin wahayin da Muka yi wa Nuhu da kuma annabawan da suka biyo bayansa, kuma Mun yi wahayi ga Ibrahimu da Isma’ila da Ishaqa da Ya’aqubu da kuma jikokin (Ya’aqubu) da Isa da Ayyuba da Yunusa da Haruna da Sulaimanu; kuma Muka bai wa Dawuda littafin Zabura



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 86

وَإِسۡمَٰعِيلَ وَٱلۡيَسَعَ وَيُونُسَ وَلُوطٗاۚ وَكُلّٗا فَضَّلۡنَا عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Da Isma’ilu da Alyasa’u da Yunusu da Luxu. Kowanne daga cikinsu kuma Mun fifita shi a kan (sauran) talikai



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 54

وَٱذۡكُرۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ إِسۡمَٰعِيلَۚ إِنَّهُۥ كَانَ صَادِقَ ٱلۡوَعۡدِ وَكَانَ رَسُولٗا نَّبِيّٗا

Kuma ka ambaci (labarin) Isma’ila a cikin (wannan) Littafi (Alqur’ani). Lalle shi ya kasance mai gaskiyar alqawari ne, kuma ya kasance Annabi ne, Manzo



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 55

وَكَانَ يَأۡمُرُ أَهۡلَهُۥ بِٱلصَّلَوٰةِ وَٱلزَّكَوٰةِ وَكَانَ عِندَ رَبِّهِۦ مَرۡضِيّٗا

Kuma ya zamanto yana umartar iyalinsa da (tsai da) salla da kuma (ba da) zakka, kuma shi yardajje ne a wurin Ubangijinsa



Capítulo: Suratul Anbiya

Verso : 85

وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِدۡرِيسَ وَذَا ٱلۡكِفۡلِۖ كُلّٞ مِّنَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

(Ka tuna) kuma Isma’ila da Idrisa da kuma Zulkifli; dukkansu suna cikin masu haquri



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 48

وَٱذۡكُرۡ إِسۡمَٰعِيلَ وَٱلۡيَسَعَ وَذَا ٱلۡكِفۡلِۖ وَكُلّٞ مِّنَ ٱلۡأَخۡيَارِ

Ka kuma tuna Isma’ila da Alyasa’u da Zulkifli; dukkaninsu kuma suna cikin zavavvu