Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 87

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَقَفَّيۡنَا مِنۢ بَعۡدِهِۦ بِٱلرُّسُلِۖ وَءَاتَيۡنَا عِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ٱلۡبَيِّنَٰتِ وَأَيَّدۡنَٰهُ بِرُوحِ ٱلۡقُدُسِۗ أَفَكُلَّمَا جَآءَكُمۡ رَسُولُۢ بِمَا لَا تَهۡوَىٰٓ أَنفُسُكُمُ ٱسۡتَكۡبَرۡتُمۡ فَفَرِيقٗا كَذَّبۡتُمۡ وَفَرِيقٗا تَقۡتُلُونَ

Kuma haqiqa Mun ba wa Musa Littafi, kuma Muka biyo bayansa da manzanni, kuma Mun bai wa Isa xan Maryam hujjoji bayyananu, kuma Mun qarfafe shi da Ruhi mai tsarki. Ashe yanzu duk sa’adda wani manzo ya zo muku da abin da zukatanku ba sa so, sai ku yi girman kai, don haka sai ku qaryata wasu, kuma ku kashe wasu?



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 45

إِذۡ قَالَتِ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ يَٰمَرۡيَمُ إِنَّ ٱللَّهَ يُبَشِّرُكِ بِكَلِمَةٖ مِّنۡهُ ٱسۡمُهُ ٱلۡمَسِيحُ عِيسَى ٱبۡنُ مَرۡيَمَ وَجِيهٗا فِي ٱلدُّنۡيَا وَٱلۡأٓخِرَةِ وَمِنَ ٱلۡمُقَرَّبِينَ

Ka tuna lokacin da mala’iku suka ce: “Ya ke Maryamu, lalle Allah Yana yi miki albishir da wata kalma daga gare shi, sunansa Almasihu Isa xan Maryamu, mai daraja a duniya da lahira, kuma yana cikin bayi makusanta



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 46

وَيُكَلِّمُ ٱلنَّاسَ فِي ٱلۡمَهۡدِ وَكَهۡلٗا وَمِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

“Kuma zai riqa yi wa mutane magana tun yana cikin shimfixar jego da kuma lokacin da ya zama dattijo, kuma yana cikin salihan bayi.”



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 47

قَالَتۡ رَبِّ أَنَّىٰ يَكُونُ لِي وَلَدٞ وَلَمۡ يَمۡسَسۡنِي بَشَرٞۖ قَالَ كَذَٰلِكِ ٱللَّهُ يَخۡلُقُ مَا يَشَآءُۚ إِذَا قَضَىٰٓ أَمۡرٗا فَإِنَّمَا يَقُولُ لَهُۥ كُن فَيَكُونُ

Sai ta ce: “Ya Ubangijina, ta yaya zan sami xa alhalin wani namiji bai kusance ni ba?” Sai ya ce: “Kamar haka ne Allah Yake halittar abin da Ya ga dama. Idan Ya yi zartar da wani al’amari, sai Ya ce da shi: “Kasance” Nan take sai ya kasance



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 48

وَيُعَلِّمُهُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَٱلتَّوۡرَىٰةَ وَٱلۡإِنجِيلَ

“Kuma zai sanar da shi rubutu da hikima da Attaura da Linjila



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 49

وَرَسُولًا إِلَىٰ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ أَنِّي قَدۡ جِئۡتُكُم بِـَٔايَةٖ مِّن رَّبِّكُمۡ أَنِّيٓ أَخۡلُقُ لَكُم مِّنَ ٱلطِّينِ كَهَيۡـَٔةِ ٱلطَّيۡرِ فَأَنفُخُ فِيهِ فَيَكُونُ طَيۡرَۢا بِإِذۡنِ ٱللَّهِۖ وَأُبۡرِئُ ٱلۡأَكۡمَهَ وَٱلۡأَبۡرَصَ وَأُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰ بِإِذۡنِ ٱللَّهِۖ وَأُنَبِّئُكُم بِمَا تَأۡكُلُونَ وَمَا تَدَّخِرُونَ فِي بُيُوتِكُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لَّكُمۡ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

“Kuma zai aiko shi a matsayin Manzo ga Banu Isra’ila (yana mai cewa): “Lalle ni na zo muku da wata aya daga Ubangijinku; lalle ni zan riqa mulmula muku tavo a siffar tsuntsu, sai in yi busa a cikinsa sai ya zama tsuntsu da izinin Allah; kuma zan warkar da wanda aka haifa makaho da mai cutar albaras, kuma in rayar da matattu da izinin Allah; kuma zan riqa ba ku labarin abin da kuke ci da abin da kuke ajiyewa a gidajenku. Lalle a cikin hakan akwai aya a gare ku in har kun kasance muminai



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 50

وَمُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيَّ مِنَ ٱلتَّوۡرَىٰةِ وَلِأُحِلَّ لَكُم بَعۡضَ ٱلَّذِي حُرِّمَ عَلَيۡكُمۡۚ وَجِئۡتُكُم بِـَٔايَةٖ مِّن رَّبِّكُمۡ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“Kuma zan zama mai gaskata abin da ya gabace ni na Attaura, kuma don in halatta muku sashin abubuwan da aka haramta muku. Kuma na zo muku da wata aya daga Ubangijinku, don haka ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku yi mini biyayya



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 51

إِنَّ ٱللَّهَ رَبِّي وَرَبُّكُمۡ فَٱعۡبُدُوهُۚ هَٰذَا صِرَٰطٞ مُّسۡتَقِيمٞ

“Lalle Allah Shi ne Ubangijina kuma Ubangijinku, don haka ku bautata masa Shi kaxai. Wannan shi ne tafarki madaidaici.”



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 52

۞فَلَمَّآ أَحَسَّ عِيسَىٰ مِنۡهُمُ ٱلۡكُفۡرَ قَالَ مَنۡ أَنصَارِيٓ إِلَى ٱللَّهِۖ قَالَ ٱلۡحَوَارِيُّونَ نَحۡنُ أَنصَارُ ٱللَّهِ ءَامَنَّا بِٱللَّهِ وَٱشۡهَدۡ بِأَنَّا مُسۡلِمُونَ

To yayin da Isa ya ga alamun kafirci a tare da su sai ya ce: “Su wane ne za su taimake ni wajen kira zuwa ga Allah?” Sai Hawariyawa suka ce: “Mu ne mataimaka addinin Allah, mun yi imani da Allah, kuma ka ba da shaida cewa, mu Musulmai ne



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 53

رَبَّنَآ ءَامَنَّا بِمَآ أَنزَلۡتَ وَٱتَّبَعۡنَا ٱلرَّسُولَ فَٱكۡتُبۡنَا مَعَ ٱلشَّـٰهِدِينَ

“Ya Ubangijinmu, mun yi imani da abin da Ka saukar, kuma mun yi xa’a ga Manzo, don haka Ka rubuta mu tare da masu shaida.”



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 54

وَمَكَرُواْ وَمَكَرَ ٱللَّهُۖ وَٱللَّهُ خَيۡرُ ٱلۡمَٰكِرِينَ

Sai suka shirya makirci, sai Allah Ya mayar musu da martani game da makircinsu; kuma Allah Shi ne Fiyayyen masu mayar da martanin makirci



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 55

إِذۡ قَالَ ٱللَّهُ يَٰعِيسَىٰٓ إِنِّي مُتَوَفِّيكَ وَرَافِعُكَ إِلَيَّ وَمُطَهِّرُكَ مِنَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَجَاعِلُ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُوكَ فَوۡقَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِۖ ثُمَّ إِلَيَّ مَرۡجِعُكُمۡ فَأَحۡكُمُ بَيۡنَكُمۡ فِيمَا كُنتُمۡ فِيهِ تَخۡتَلِفُونَ

Kuma ka tuna lokacin da Allah Ya ce: “Ya kai Isa, lalle Ni Mai karvar ranka ne, kuma Ni Mai xaukaka ka ne zuwa gare Ni, kuma zan tsarkake ka daga (cutarwar) waxanda suka kafirta, kuma zan xora waxanda suka bi ka a kan waxanda suka kafirta har zuwa ranar tashin alqiyama; sannan zuwa gare Ni ne makomarku take, sai In yi hukunci a tsakaninku game da abin da kuke savani a kansa



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 59

إِنَّ مَثَلَ عِيسَىٰ عِندَ ٱللَّهِ كَمَثَلِ ءَادَمَۖ خَلَقَهُۥ مِن تُرَابٖ ثُمَّ قَالَ لَهُۥ كُن فَيَكُونُ

Lalle misalin Isa a wurin Allah kamar misalin Adamu ne; Ya halicce shi daga turvaya, sannan Ya ce da shi: “Kasance.” nan take sai ya kasance



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 156

وَبِكُفۡرِهِمۡ وَقَوۡلِهِمۡ عَلَىٰ مَرۡيَمَ بُهۡتَٰنًا عَظِيمٗا

Kuma saboda kafircinsu da kuma wata babbar qarya da suka yi wa Maryamu[1]


1- Watau tuhumar da Yahudawa suka yi mata da cewa, wai zina ta yi ta haifi Annabi Isa ().


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 157

وَقَوۡلِهِمۡ إِنَّا قَتَلۡنَا ٱلۡمَسِيحَ عِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ رَسُولَ ٱللَّهِ وَمَا قَتَلُوهُ وَمَا صَلَبُوهُ وَلَٰكِن شُبِّهَ لَهُمۡۚ وَإِنَّ ٱلَّذِينَ ٱخۡتَلَفُواْ فِيهِ لَفِي شَكّٖ مِّنۡهُۚ مَا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٍ إِلَّا ٱتِّبَاعَ ٱلظَّنِّۚ وَمَا قَتَلُوهُ يَقِينَۢا

Da kuma faxarsu cewa: “Lalle mu mun kashe Almasihu Isa xan Maryamu Manzon Allah,” alhalin kuwa ba su kashe shi ba, kuma ba su gicciye shi ba, sai dai an kamanta musu (wani da shi ne)[1]. Kuma lalle waxanda suka yi savani game da shi (Annabi Isa) suna cikin shakka game da (kashe) shi, ba su da wani ilimi face bin zato. Kuma a haqiqanin gaskiya ba su kashe shi ba


1- Watau suka zaci shi ne Annabi Isa (), suka kama shi suka kashe.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 158

بَل رَّفَعَهُ ٱللَّهُ إِلَيۡهِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَزِيزًا حَكِيمٗا

Ba haka ba ne, Allah ya xaga shi zuwa gare Shi ne. kuma Allah Ya kasance Mabuwayi ne, Mai hikima



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 159

وَإِن مِّنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ إِلَّا لَيُؤۡمِنَنَّ بِهِۦ قَبۡلَ مَوۡتِهِۦۖ وَيَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ يَكُونُ عَلَيۡهِمۡ شَهِيدٗا

Kuma babu wani daga Ma’abota Littafi face sai ya yi imani da shi kafin mutuwarsa[1]; kuma a ranar tashin alqiyama zai zama mai ba da shaida a kansu


1- Watau lokacin da Annabi Isa () zai sauko qasa a qarshen zamani duk wani Bayahude ba Banasare sai ya yi imani da shi kafin mutuwar Annabi Isa ().


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 163

۞إِنَّآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ كَمَآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ نُوحٖ وَٱلنَّبِيِّـۧنَ مِنۢ بَعۡدِهِۦۚ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ وَٱلۡأَسۡبَاطِ وَعِيسَىٰ وَأَيُّوبَ وَيُونُسَ وَهَٰرُونَ وَسُلَيۡمَٰنَۚ وَءَاتَيۡنَا دَاوُۥدَ زَبُورٗا

Lalle Mun yi maka wahayi irin wahayin da Muka yi wa Nuhu da kuma annabawan da suka biyo bayansa, kuma Mun yi wahayi ga Ibrahimu da Isma’ila da Ishaqa da Ya’aqubu da kuma jikokin (Ya’aqubu) da Isa da Ayyuba da Yunusa da Haruna da Sulaimanu; kuma Muka bai wa Dawuda littafin Zabura



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 171

يَـٰٓأَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ لَا تَغۡلُواْ فِي دِينِكُمۡ وَلَا تَقُولُواْ عَلَى ٱللَّهِ إِلَّا ٱلۡحَقَّۚ إِنَّمَا ٱلۡمَسِيحُ عِيسَى ٱبۡنُ مَرۡيَمَ رَسُولُ ٱللَّهِ وَكَلِمَتُهُۥٓ أَلۡقَىٰهَآ إِلَىٰ مَرۡيَمَ وَرُوحٞ مِّنۡهُۖ فَـَٔامِنُواْ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦۖ وَلَا تَقُولُواْ ثَلَٰثَةٌۚ ٱنتَهُواْ خَيۡرٗا لَّكُمۡۚ إِنَّمَا ٱللَّهُ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞۖ سُبۡحَٰنَهُۥٓ أَن يَكُونَ لَهُۥ وَلَدٞۘ لَّهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۗ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ وَكِيلٗا

Ya ku Ma’abota Littafi, kada ku wuce iyaka cikin addininku[1], kuma kada ku faxi wata magana game da Allah sai ta gaskiya. Almasihu Isa xan Maryamu Manzon Allah ne, kuma kalmarsa ce da ya jefa wa Maryamu, kuma Ruhi ne daga gare Shi; don haka ku yi imani da Allah da manzanninsa, kuma kada ku riqa cewa su uku ne. Ku daina shi ya fi alheri a gare ku. Allah Shi ne kaxai abin bauta da gaskiya, Xaya ne; Ya tsarkaka a ce Yana da xa. Kuma abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa nasa ne, kuma Allah Ya isa Abin dogaro


1- Watau kada su wuce iyaka wajen kuzuzuta lamarin Annabi Isa () har ta kai su ga cewa xan Allah ne.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 172

لَّن يَسۡتَنكِفَ ٱلۡمَسِيحُ أَن يَكُونَ عَبۡدٗا لِّلَّهِ وَلَا ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ ٱلۡمُقَرَّبُونَۚ وَمَن يَسۡتَنكِفۡ عَنۡ عِبَادَتِهِۦ وَيَسۡتَكۡبِرۡ فَسَيَحۡشُرُهُمۡ إِلَيۡهِ جَمِيعٗا

Almasihu ba zai tava qyamar ya zama bawan Allah ba, hakanan su ma mala’iku makusanta. Duk wanda yake qyamar bautar Allah, kuma suke girman kai, to zai tattara su gaba xaya zuwa gare Shi



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 17

لَّقَدۡ كَفَرَ ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡمَسِيحُ ٱبۡنُ مَرۡيَمَۚ قُلۡ فَمَن يَمۡلِكُ مِنَ ٱللَّهِ شَيۡـًٔا إِنۡ أَرَادَ أَن يُهۡلِكَ ٱلۡمَسِيحَ ٱبۡنَ مَرۡيَمَ وَأُمَّهُۥ وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗاۗ وَلِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَاۚ يَخۡلُقُ مَا يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Lalle haqiqa, waxannan da suka ce: “Lalle Allah Shi ne Almasihu xan Maryamu” sun kafirta. Ka ce: “To wane ne ya isa ya hana Allah, idan Ya yi nufin Ya hallaka Almasihu xan Maryamu da mahaifiyarsa da duk wanda yake ban qasa gaba xaya? Allah kuwa Shi Yake mallakar abin da yake cikin sammai da qasa da kuma abin da yake tsakaninsu. Yana halittar abin da Ya ga dama. Kuma Allah Mai cikakken iko ne a kan komai.”



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 46

وَقَفَّيۡنَا عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِم بِعِيسَى ٱبۡنِ مَرۡيَمَ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِ مِنَ ٱلتَّوۡرَىٰةِۖ وَءَاتَيۡنَٰهُ ٱلۡإِنجِيلَ فِيهِ هُدٗى وَنُورٞ وَمُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِ مِنَ ٱلتَّوۡرَىٰةِ وَهُدٗى وَمَوۡعِظَةٗ لِّلۡمُتَّقِينَ

Sai Muka biyar da Isa xan Maryamu a bayansu wanda yake gaskata abin da ya gabace shi na Attaura, kuma Muka ba shi Linjila, a cikinta akwai shiriya da haske, kuma tana gaskata abin da ya gabace ta na Attaura, kuma shiriya ce, da wa’azi ga masu taqawa



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 72

لَقَدۡ كَفَرَ ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡمَسِيحُ ٱبۡنُ مَرۡيَمَۖ وَقَالَ ٱلۡمَسِيحُ يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ رَبِّي وَرَبَّكُمۡۖ إِنَّهُۥ مَن يُشۡرِكۡ بِٱللَّهِ فَقَدۡ حَرَّمَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِ ٱلۡجَنَّةَ وَمَأۡوَىٰهُ ٱلنَّارُۖ وَمَا لِلظَّـٰلِمِينَ مِنۡ أَنصَارٖ

Lalle haqiqa waxanda suka ce: “Lalle Allah Shi ne Almasihu xan Maryamu” sun kafirta. Shi kuwa Almasihu cewa ya yi: “Ya ku Bani-Isra’ila, ku bauta wa Allah Ubangijina kuma Ubangijinku. Lalle yadda al’amarin yake, duk wanda ya yi shirka da Allah, to haqiqa Allah Ya haramta masa shiga Aljanna, kuma makomarsa ita ce wuta, kuma azzalumai ba su da wasu mataimaka.”



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 75

مَّا ٱلۡمَسِيحُ ٱبۡنُ مَرۡيَمَ إِلَّا رَسُولٞ قَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِهِ ٱلرُّسُلُ وَأُمُّهُۥ صِدِّيقَةٞۖ كَانَا يَأۡكُلَانِ ٱلطَّعَامَۗ ٱنظُرۡ كَيۡفَ نُبَيِّنُ لَهُمُ ٱلۡأٓيَٰتِ ثُمَّ ٱنظُرۡ أَنَّىٰ يُؤۡفَكُونَ

Shi fa Almasihu xan Maryamu bai zamo ba face Manzo, wanda haqiqa manzanni sun shuxe kafinsa. Mahaifiyarsa kuma Siddiqa ce; shi da ita sun kasance suna cin abinci. Duba ka ga yadda Muke bayyana musu ayoyi, sannan ka sake dubawa, ta yaya ake kautar da su?



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 78

لُعِنَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۢ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ عَلَىٰ لِسَانِ دَاوُۥدَ وَعِيسَى ٱبۡنِ مَرۡيَمَۚ ذَٰلِكَ بِمَا عَصَواْ وَّكَانُواْ يَعۡتَدُونَ

An la’anci waxanda suka kafirta daga cikin Bani-Isra’ila a bisa harshen Dawuda da kuma Isa xan Maryamu. Hakan kuwa saboda abin da suka riqa yi ne na savo, kuma sun kasance suna qetare iyaka



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 110

إِذۡ قَالَ ٱللَّهُ يَٰعِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ٱذۡكُرۡ نِعۡمَتِي عَلَيۡكَ وَعَلَىٰ وَٰلِدَتِكَ إِذۡ أَيَّدتُّكَ بِرُوحِ ٱلۡقُدُسِ تُكَلِّمُ ٱلنَّاسَ فِي ٱلۡمَهۡدِ وَكَهۡلٗاۖ وَإِذۡ عَلَّمۡتُكَ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَٱلتَّوۡرَىٰةَ وَٱلۡإِنجِيلَۖ وَإِذۡ تَخۡلُقُ مِنَ ٱلطِّينِ كَهَيۡـَٔةِ ٱلطَّيۡرِ بِإِذۡنِي فَتَنفُخُ فِيهَا فَتَكُونُ طَيۡرَۢا بِإِذۡنِيۖ وَتُبۡرِئُ ٱلۡأَكۡمَهَ وَٱلۡأَبۡرَصَ بِإِذۡنِيۖ وَإِذۡ تُخۡرِجُ ٱلۡمَوۡتَىٰ بِإِذۡنِيۖ وَإِذۡ كَفَفۡتُ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ عَنكَ إِذۡ جِئۡتَهُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِ فَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡهُمۡ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٞ

(Ka tuna) lokacin da Allah zai ce: “Ya kai Isa xan Maryamu, ka tuna ni’imata da Na yi maka kai da mahaifiyarka, yayin da Na qarfafe ka da Ruhi mai tsarki, kana yi wa mutane magana lokacin kana cikin zanin goyo, da kuma lokacin da kake dattijo, kuma ka tuna lokacin da Na koyar da kai rubutu da hikima da Attaura da Linjila. Kuma ka tuna lokacin da kake qirqirar (wani abu) kamar tsuntsu da tavo da izinina, sai ka yi busa a cikinsa, sai ya zamo tsuntsu da izinina; kuma kake warkar da wanda aka haifa da makanta da mai albaras da izinina; kuma ka tuna lokacin da kake fito da matattu (daga cikin qaburburansu) da izinina; kuma ka tuna lokacin da Na kare ka (daga cutar) Bani Isra’ila yayin da ka zo musu da hujjoji bayyanannu, sai waxanda suka kafirta daga cikinsu suka ce: “Ai wannan ba komai ba ne face sihiri mabayyani.”



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 111

وَإِذۡ أَوۡحَيۡتُ إِلَى ٱلۡحَوَارِيِّـۧنَ أَنۡ ءَامِنُواْ بِي وَبِرَسُولِي قَالُوٓاْ ءَامَنَّا وَٱشۡهَدۡ بِأَنَّنَا مُسۡلِمُونَ

Kuma ka tuna lokacin da Na yi wahayi zuwa ga Hawariyyawa: “Ku yi imani da Ni da Manzona,” sai suka ce: “Mun yi imani, kuma Ka shaida cewa, mu Musulmai ne.”



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 112

إِذۡ قَالَ ٱلۡحَوَارِيُّونَ يَٰعِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ هَلۡ يَسۡتَطِيعُ رَبُّكَ أَن يُنَزِّلَ عَلَيۡنَا مَآئِدَةٗ مِّنَ ٱلسَّمَآءِۖ قَالَ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Lokacin da Hawariyyawa suka ce: “Ya Isa xan Maryamu, shin Ubangijinka Yana iya saukar mana da kavaki daga sama?” Ya ce: “Ku kiyayi Allah, idan har kun kasance muminai.”



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 113

قَالُواْ نُرِيدُ أَن نَّأۡكُلَ مِنۡهَا وَتَطۡمَئِنَّ قُلُوبُنَا وَنَعۡلَمَ أَن قَدۡ صَدَقۡتَنَا وَنَكُونَ عَلَيۡهَا مِنَ ٱلشَّـٰهِدِينَ

Suka ce: “Mu muna nufin mu ci daga gare shi, kuma zukatanmu su sami nutsuwa, sannan mu haqiqance cewa, lalle ka faxa mana gaskiya, kuma mu zamo masu ba da shaida a kansa.”



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 114

قَالَ عِيسَى ٱبۡنُ مَرۡيَمَ ٱللَّهُمَّ رَبَّنَآ أَنزِلۡ عَلَيۡنَا مَآئِدَةٗ مِّنَ ٱلسَّمَآءِ تَكُونُ لَنَا عِيدٗا لِّأَوَّلِنَا وَءَاخِرِنَا وَءَايَةٗ مِّنكَۖ وَٱرۡزُقۡنَا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰزِقِينَ

Isa xan Maryamu ya ce: “Ya Allah Ubangijinmu, Ka saukar mana da kavaki daga sama, wanda zai zame mana wani Idi, ga na farkonmu da na qarshenmu, kuma ya zamo wata aya daga gare Ka; kuma Ka arzuta mu, lalle Kai ne Fiyayyen masu arzutawa.”