وَلَا تَقُولُواْ لِمَن يُقۡتَلُ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ أَمۡوَٰتُۢۚ بَلۡ أَحۡيَآءٞ وَلَٰكِن لَّا تَشۡعُرُونَ
Kada kuma ku ce wa waxanda ake kashewa a kan hanyar Allah su matattu ne. A’a, rayayyu ne, sai dai ku ne ba ku sani ba
وَقَٰتِلُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ ٱلَّذِينَ يُقَٰتِلُونَكُمۡ وَلَا تَعۡتَدُوٓاْۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُحِبُّ ٱلۡمُعۡتَدِينَ
Kuma ku yaqi waxanda suke yaqar ku don ku xaukaka kalmar Allah, kuma kada ku qetare iyaka. Lalle Allah ba Ya son masu qetare iyaka
وَٱقۡتُلُوهُمۡ حَيۡثُ ثَقِفۡتُمُوهُمۡ وَأَخۡرِجُوهُم مِّنۡ حَيۡثُ أَخۡرَجُوكُمۡۚ وَٱلۡفِتۡنَةُ أَشَدُّ مِنَ ٱلۡقَتۡلِۚ وَلَا تُقَٰتِلُوهُمۡ عِندَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ حَتَّىٰ يُقَٰتِلُوكُمۡ فِيهِۖ فَإِن قَٰتَلُوكُمۡ فَٱقۡتُلُوهُمۡۗ كَذَٰلِكَ جَزَآءُ ٱلۡكَٰفِرِينَ
Kuma ku yaqe su duk inda kuka same su, kuma ku fitar da su ta inda suka fitar da ku; kuma fitina (ta kafirci) ita ce mafi tsanani fiye da kisa, kuma kada ku yaqe su a wurin Masallaci mai alfarma, har sai idan sun yaqe ku a cikinsa, idan har suka yaqe ku, to ku ma ku yaqe su. Kamar haka ne sakamakon kafirai yake
وَقَٰتِلُوهُمۡ حَتَّىٰ لَا تَكُونَ فِتۡنَةٞ وَيَكُونَ ٱلدِّينُ لِلَّهِۖ فَإِنِ ٱنتَهَوۡاْ فَلَا عُدۡوَٰنَ إِلَّا عَلَى ٱلظَّـٰلِمِينَ
Kuma ku yaqe su har ya zamanto babu wata fitina, kuma addini ya zamo na Allah ne. Idan suka daina, to babu sauran kai farmaki sai a kan azzalumai
كُتِبَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡقِتَالُ وَهُوَ كُرۡهٞ لَّكُمۡۖ وَعَسَىٰٓ أَن تَكۡرَهُواْ شَيۡـٔٗا وَهُوَ خَيۡرٞ لَّكُمۡۖ وَعَسَىٰٓ أَن تُحِبُّواْ شَيۡـٔٗا وَهُوَ شَرّٞ لَّكُمۡۚ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ وَأَنتُمۡ لَا تَعۡلَمُونَ
An wajabta muku yaqi (ku muminai), ga shi kuwa kuna qin sa, kuma zai iya yiwuwa ku qi wani abu alhalin shi alheri ne a gare ku, kuma zai iya yiwuwa ku so wani abu alhalin shi sharri ne a gare ku. Kuma Allah Shi yake da sani, ku ba ku sani ba
إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱلَّذِينَ هَاجَرُواْ وَجَٰهَدُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ أُوْلَـٰٓئِكَ يَرۡجُونَ رَحۡمَتَ ٱللَّهِۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ
Lalle waxanda suka yi imani da kuma waxanda suka yi hijira, kuma suka yi jihadi don Allah, waxannan su ne suke fatan rahamar Allah; Allah kuwa Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai
وَقَٰتِلُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٞ
Kuma ku yi yaqi don xaukaka kalmar Allah, kuma ku sani cewa, lalle Allah Mai ji ne, Masani
أَمۡ حَسِبۡتُمۡ أَن تَدۡخُلُواْ ٱلۡجَنَّةَ وَلَمَّا يَعۡلَمِ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ جَٰهَدُواْ مِنكُمۡ وَيَعۡلَمَ ٱلصَّـٰبِرِينَ
Yanzu kuna tsammanin za ku shiga Aljanna ne alhalin Allah bai bayyanar da masu yin jihadi daga cikinku ba, kuma bai bayyanar da masu haquri ba
وَلَئِن قُتِلۡتُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ أَوۡ مُتُّمۡ لَمَغۡفِرَةٞ مِّنَ ٱللَّهِ وَرَحۡمَةٌ خَيۡرٞ مِّمَّا يَجۡمَعُونَ
Kuma lalle idan ma har an kashe ku a hanyar Allah ko kuma kuka mutu, to kuna da gafara ta musamman a wajen Allah da kuma rahama, wanda shi ne mafi alheri fiye da abin da suke tarawa
وَلَئِن مُّتُّمۡ أَوۡ قُتِلۡتُمۡ لَإِلَى ٱللَّهِ تُحۡشَرُونَ
Kuma lalle in kuka mutu ko aka kashe ku, lalle zuwa ga Allah dai za a tattara ku
وَلَا تَحۡسَبَنَّ ٱلَّذِينَ قُتِلُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ أَمۡوَٰتَۢاۚ بَلۡ أَحۡيَآءٌ عِندَ رَبِّهِمۡ يُرۡزَقُونَ
Kuma kada ka yi tsammanin waxanda aka kashe su a wajen yaxa kalmar Allah matattu ne. A’a, rayayyu ne a wajen Ubangijinsu, ana arzurta su
۞يَسۡتَبۡشِرُونَ بِنِعۡمَةٖ مِّنَ ٱللَّهِ وَفَضۡلٖ وَأَنَّ ٱللَّهَ لَا يُضِيعُ أَجۡرَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Suna ta farin ciki da ni’ima daga Allah da falala, kuma Allah ba Ya tozarta ladan masu imani
فَٱسۡتَجَابَ لَهُمۡ رَبُّهُمۡ أَنِّي لَآ أُضِيعُ عَمَلَ عَٰمِلٖ مِّنكُم مِّن ذَكَرٍ أَوۡ أُنثَىٰۖ بَعۡضُكُم مِّنۢ بَعۡضٖۖ فَٱلَّذِينَ هَاجَرُواْ وَأُخۡرِجُواْ مِن دِيَٰرِهِمۡ وَأُوذُواْ فِي سَبِيلِي وَقَٰتَلُواْ وَقُتِلُواْ لَأُكَفِّرَنَّ عَنۡهُمۡ سَيِّـَٔاتِهِمۡ وَلَأُدۡخِلَنَّهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ ثَوَابٗا مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِۚ وَٱللَّهُ عِندَهُۥ حُسۡنُ ٱلثَّوَابِ
Sai Ubangijinsu Ya amsa musu (cewa): “Lalle Ni ba zan tozarta aikin wani mai aiki daga cikinku ba, namiji ne ko mace; sashinku yana tare da sashe. To waxanda suka yi hijira kuma aka fitar da su daga gidajensu kuma aka cutar da su wajen bin tafarkina kuma suka yi yaqi kuma aka kashe su, lalle zan kankare musu kurakuransu, kuma lalle zan shigar da su gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. (Wannan) lada ne daga wajen Allah, kuma a wurin Allah ne mafi kyawun lada yake.”
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ خُذُواْ حِذۡرَكُمۡ فَٱنفِرُواْ ثُبَاتٍ أَوِ ٱنفِرُواْ جَمِيعٗا
Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi taka-tsantsan, kuma ku fita qungiya-qungiya, ko kuma ku fita gaba xaya
وَإِنَّ مِنكُمۡ لَمَن لَّيُبَطِّئَنَّ فَإِنۡ أَصَٰبَتۡكُم مُّصِيبَةٞ قَالَ قَدۡ أَنۡعَمَ ٱللَّهُ عَلَيَّ إِذۡ لَمۡ أَكُن مَّعَهُمۡ شَهِيدٗا
Kuma lalle a cikinku akwai wanda yake daqilewa, idan wata musiba ta same ku, sai ya ce: “Haqiqa Allah Ya yi mini ni’ima da ban halarci (yaqin) tare da su ba.”
وَلَئِنۡ أَصَٰبَكُمۡ فَضۡلٞ مِّنَ ٱللَّهِ لَيَقُولَنَّ كَأَن لَّمۡ تَكُنۢ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَهُۥ مَوَدَّةٞ يَٰلَيۡتَنِي كُنتُ مَعَهُمۡ فَأَفُوزَ فَوۡزًا عَظِيمٗا
Amma idan wata falala ta same ku daga Allah, tabbas zai riqa cewa, kamar daxai ba wata soyayya tsakaninku da shi: “Ina ma na kasance tare da su, don ni ma in rabauta rabo mai girma?”[1]
1- Watau a raba ganimar da aka samo tare da shi, shi ma ya more sosai.
۞فَلۡيُقَٰتِلۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ ٱلَّذِينَ يَشۡرُونَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا بِٱلۡأٓخِرَةِۚ وَمَن يُقَٰتِلۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ فَيُقۡتَلۡ أَوۡ يَغۡلِبۡ فَسَوۡفَ نُؤۡتِيهِ أَجۡرًا عَظِيمٗا
To waxanda suke sayen rayuwar lahira da ta duniya, sai su yi yaqi don xaukaka kalmar Allah. Duk wanda yake yin yaqi don xaukaka kalmar Allah kuwa, sai aka kashe shi ko kuma ya yi galaba, to za Mu ba shi lada mai girma
وَمَا لَكُمۡ لَا تُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَٱلۡمُسۡتَضۡعَفِينَ مِنَ ٱلرِّجَالِ وَٱلنِّسَآءِ وَٱلۡوِلۡدَٰنِ ٱلَّذِينَ يَقُولُونَ رَبَّنَآ أَخۡرِجۡنَا مِنۡ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةِ ٱلظَّالِمِ أَهۡلُهَا وَٱجۡعَل لَّنَا مِن لَّدُنكَ وَلِيّٗا وَٱجۡعَل لَّنَا مِن لَّدُنكَ نَصِيرًا
Kuma me ya same ku ne, da ba za ku yi yaqi don xaukaka kalmar Allah ba, da kuma kuvutar da raunana maza da mata da yara qanana, waxanda suke cewa: “Ya Ubangijinmu, Ka fitar da mu daga wannan alqaryar wadda mutanenta suke azzalumai, kuma Ka sanya mana wani majivincin lamari daga wurinka, kuma Ka sanya mana wani mai taimako daga wurinka?”
ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱلطَّـٰغُوتِ فَقَٰتِلُوٓاْ أَوۡلِيَآءَ ٱلشَّيۡطَٰنِۖ إِنَّ كَيۡدَ ٱلشَّيۡطَٰنِ كَانَ ضَعِيفًا
Waxanda suka yi imani suna yaqi ne don xaukaka kalmar Allah; waxanda kuma suka kafirce suna yin yaqi ne don kare Xagutu; to ku yaqi masoya Shaixan; lalle makircin Shaixan rarrauna ne
أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلَّذِينَ قِيلَ لَهُمۡ كُفُّوٓاْ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ فَلَمَّا كُتِبَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقِتَالُ إِذَا فَرِيقٞ مِّنۡهُمۡ يَخۡشَوۡنَ ٱلنَّاسَ كَخَشۡيَةِ ٱللَّهِ أَوۡ أَشَدَّ خَشۡيَةٗۚ وَقَالُواْ رَبَّنَا لِمَ كَتَبۡتَ عَلَيۡنَا ٱلۡقِتَالَ لَوۡلَآ أَخَّرۡتَنَآ إِلَىٰٓ أَجَلٖ قَرِيبٖۗ قُلۡ مَتَٰعُ ٱلدُّنۡيَا قَلِيلٞ وَٱلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لِّمَنِ ٱتَّقَىٰ وَلَا تُظۡلَمُونَ فَتِيلًا
Shin ba ka ganin waxanda aka ce da su: “Ku kame hannayenku kuma ku tsayar da salla kuma ku bayar da zakka?”[1] To yayin da aka wajabta musu yaqi, sai ga wani vangare daga cikinsu suna jin tsoron mutane kamar yadda suke jin tsoron Allah, ko ma fiye da hakan. Kuma sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, don me Ka wajabta mana yin yaqi, me ya hana Ka jinkirta mana zuwa wani lokaci makusanci?” Ka ce: “Jin daxin duniya kaxan ne, lahira kuwa ita ce mafi alheri ga wanda ya yi taqawa, kuma ba za a zalunce ku ba, ko da gwargwadon zaren qwallon dabino ne.”
1- Watau wasu daga cikin sahabbai waxanda suke ta roqon a farlanta musu jihadi, amma ana nuna musu su bar wannan maganar, su dai tsayar da salla su ba da zakka.
فَقَٰتِلۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ لَا تُكَلَّفُ إِلَّا نَفۡسَكَۚ وَحَرِّضِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۖ عَسَى ٱللَّهُ أَن يَكُفَّ بَأۡسَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۚ وَٱللَّهُ أَشَدُّ بَأۡسٗا وَأَشَدُّ تَنكِيلٗا
To ka yi yaqi domin xaukaka kalmar Allah, ba a xora maka nauyin tilasta kowa ba sai kanka. Kuma ka zaburar da muminai; Allah zai dankwafe qarfin waxanda suka kafirta; kuma Allah Shi ne Mafi tsananin qarfi, kuma Mafi tsananin uquba
لَّا يَسۡتَوِي ٱلۡقَٰعِدُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ غَيۡرُ أُوْلِي ٱلضَّرَرِ وَٱلۡمُجَٰهِدُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡۚ فَضَّلَ ٱللَّهُ ٱلۡمُجَٰهِدِينَ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡ عَلَى ٱلۡقَٰعِدِينَ دَرَجَةٗۚ وَكُلّٗا وَعَدَ ٱللَّهُ ٱلۡحُسۡنَىٰۚ وَفَضَّلَ ٱللَّهُ ٱلۡمُجَٰهِدِينَ عَلَى ٱلۡقَٰعِدِينَ أَجۡرًا عَظِيمٗا
Waxanda suka zauna a gida daga cikin muminai ba su fita yaqi ba, in dai ba masu larura ba, ba za su yi daidai da masu jihadi don xaukaka kalmar Allah da dukiyoyinsu da kawunansu ba. Allah Ya fifita darajar masu jihadi da dukiyoyinsu da kawunansu a kan waxanda suka zauna a gida. Kuma dukkansu Allah Ya yi masu alqawarin Aljanna. Kuma Allah Ya fifita masu jihadi a kan waxanda suka zauna a gida, da lada mai girma
وَلَا تَهِنُواْ فِي ٱبۡتِغَآءِ ٱلۡقَوۡمِۖ إِن تَكُونُواْ تَأۡلَمُونَ فَإِنَّهُمۡ يَأۡلَمُونَ كَمَا تَأۡلَمُونَۖ وَتَرۡجُونَ مِنَ ٱللَّهِ مَا لَا يَرۡجُونَۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمًا
Kuma kada ku yi rauni wajen neman mutanen; in kun kasance kuna jin raxaxi, to ai su ma (kafirai) suna jin raxaxi kamar yadda kuke jin raxaxi; kuma kuna fatan wani lada a wurin Allah, wanda su ba sa fatan irinsa. Allah kuwa Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai yawan hikima
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱبۡتَغُوٓاْ إِلَيۡهِ ٱلۡوَسِيلَةَ وَجَٰهِدُواْ فِي سَبِيلِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ
Ya ku waxanda suka yi imani, ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku nemi abin da zai sada ku da shi, kuma ku yi jihadi wajen yaxa kalmarsa, don ku rabauta
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَن يَرۡتَدَّ مِنكُمۡ عَن دِينِهِۦ فَسَوۡفَ يَأۡتِي ٱللَّهُ بِقَوۡمٖ يُحِبُّهُمۡ وَيُحِبُّونَهُۥٓ أَذِلَّةٍ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ أَعِزَّةٍ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ يُجَٰهِدُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَلَا يَخَافُونَ لَوۡمَةَ لَآئِمٖۚ ذَٰلِكَ فَضۡلُ ٱللَّهِ يُؤۡتِيهِ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٌ
Ya ku waxanda suka yi imani, duk wanda ya yi ridda daga cikinku, ya bar addininsa, to (ya sani) Allah zai kawo waxansu mutane da Yake son su suna son Sa, suna masu qasqantar da kai ga muminai, suna masu nuna wa kafirai isa, suna yin jihadi don xaukaka kalmar Allah, kuma ba sa jin tsoron zargin wani mai zargi. Wannan falalar Allah ce da Yake bayar da ita ga wanda Ya ga dama. Kuma Allah Mayalwaci ne, Masani
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا لَقِيتُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ زَحۡفٗا فَلَا تُوَلُّوهُمُ ٱلۡأَدۡبَارَ
Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka haxu da cincirindon waxanda suka kafirta, to kada ku ba su baya
وَمَن يُوَلِّهِمۡ يَوۡمَئِذٖ دُبُرَهُۥٓ إِلَّا مُتَحَرِّفٗا لِّقِتَالٍ أَوۡ مُتَحَيِّزًا إِلَىٰ فِئَةٖ فَقَدۡ بَآءَ بِغَضَبٖ مِّنَ ٱللَّهِ وَمَأۡوَىٰهُ جَهَنَّمُۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ
Duk kuwa wanda ya ba su baya a wannan ranar idan dai ba wanda ya gudu da niyyar juyowa ya kai xauki ko kuma mai niyyar haxuwa da wata jama’a (ta mayaqa) ba, to haqiqa ya komo da fushin Allah, kuma makomarsa Jahannama ce; wannan makoma kuwa ta munana
وَقَٰتِلُوهُمۡ حَتَّىٰ لَا تَكُونَ فِتۡنَةٞ وَيَكُونَ ٱلدِّينُ كُلُّهُۥ لِلَّهِۚ فَإِنِ ٱنتَهَوۡاْ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِمَا يَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ
Kuma ku yaqe su har sai ya zamanto ba wata fitina[1], addini kuma ya zamanto dukkaninsa na Allah. Sannan idan suka daina, to lalle Allah Mai ganin abin da suke aikatawa ne
1- Watau watsuwar shirka a cikin al’umma da yunqurin hana mutane karvar gaskiya.
وَإِن تَوَلَّوۡاْ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ مَوۡلَىٰكُمۡۚ نِعۡمَ ٱلۡمَوۡلَىٰ وَنِعۡمَ ٱلنَّصِيرُ
Idan kuma suka ba da baya, to ku sani cewa, Allah (Shi ne) Majivincin al’amarinku. Madalla da wannan Majivinci, kuma madalla da wannan Mai taimako
۞وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّمَا غَنِمۡتُم مِّن شَيۡءٖ فَأَنَّ لِلَّهِ خُمُسَهُۥ وَلِلرَّسُولِ وَلِذِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَٱبۡنِ ٱلسَّبِيلِ إِن كُنتُمۡ ءَامَنتُم بِٱللَّهِ وَمَآ أَنزَلۡنَا عَلَىٰ عَبۡدِنَا يَوۡمَ ٱلۡفُرۡقَانِ يَوۡمَ ٱلۡتَقَى ٱلۡجَمۡعَانِۗ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ
Kuma ku sani cewa duk abin da kuka samu na ganima to lalle xaya bisa biyar na Allah ne da Manzo da kuma makusantan (Annabi)[1], da marayu da kuma miskinai da kuma matafiya[2], idan kun kasance kun yi imani da Allah da kuma abin da Muka saukar wa bawanmu ranar rabewa (ranar yaqin Badar) ranar da qungiyoyin nan biyu suka haxu. Allah kuwa Mai iko ne a kan komai
1- Su ne Banu Hashim da Banu Muxxalib waxanda aka haramta musu cin zakka.
2- Suran kashi huxun kuwa na mayaqa ne.