Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 34

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ أَبَىٰ وَٱسۡتَكۡبَرَ وَكَانَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Muka ce wa mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu.” Sai duk suka yi sujjada[1], in ban da Iblis, sai shi ya qi, ya kuma yi girman kai, kuma ya tabbata cikin kafirai


1- Mala’iku sun yi wa Adamu () sujjada ne don biyayya ga umarnin Allah. Ba ya halatta a Musulunci wani ya yi wa wani sujjada ba Allah ba.


Capítulo: Suratul An’am

Verso : 100

وَجَعَلُواْ لِلَّهِ شُرَكَآءَ ٱلۡجِنَّ وَخَلَقَهُمۡۖ وَخَرَقُواْ لَهُۥ بَنِينَ وَبَنَٰتِۭ بِغَيۡرِ عِلۡمٖۚ سُبۡحَٰنَهُۥ وَتَعَٰلَىٰ عَمَّا يَصِفُونَ

Kuma sun sanya wa Allah aljannu a matsayin abokanan tarayya, alhali kuwa Shi ya halicce su; kuma suka qago masa ‘ya’ya maza da mata, ba tare da wani ilimi ba. Tsarki ya tabbata a gare Shi, kuma Ya xaukaka daga irin abin da suke siffanta (Shi da shi)



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 112

وَكَذَٰلِكَ جَعَلۡنَا لِكُلِّ نَبِيٍّ عَدُوّٗا شَيَٰطِينَ ٱلۡإِنسِ وَٱلۡجِنِّ يُوحِي بَعۡضُهُمۡ إِلَىٰ بَعۡضٖ زُخۡرُفَ ٱلۡقَوۡلِ غُرُورٗاۚ وَلَوۡ شَآءَ رَبُّكَ مَا فَعَلُوهُۖ فَذَرۡهُمۡ وَمَا يَفۡتَرُونَ

Kuma kamar haka ne Muka sanya wa kowane annabi maqiya daga shaixanun mutane da aljannu, sashinsu yana kimsa wa wani sashi qayataccen zance, don ruxi. Kuma da Ubangijinka Ya ga dama da ba su aikata haka ba; don haka ka qyale su da irin abin da suke qagowa



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 128

وَيَوۡمَ يَحۡشُرُهُمۡ جَمِيعٗا يَٰمَعۡشَرَ ٱلۡجِنِّ قَدِ ٱسۡتَكۡثَرۡتُم مِّنَ ٱلۡإِنسِۖ وَقَالَ أَوۡلِيَآؤُهُم مِّنَ ٱلۡإِنسِ رَبَّنَا ٱسۡتَمۡتَعَ بَعۡضُنَا بِبَعۡضٖ وَبَلَغۡنَآ أَجَلَنَا ٱلَّذِيٓ أَجَّلۡتَ لَنَاۚ قَالَ ٱلنَّارُ مَثۡوَىٰكُمۡ خَٰلِدِينَ فِيهَآ إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّ رَبَّكَ حَكِيمٌ عَلِيمٞ

Kuma (ka tuna) ranar da zai tara su gaba xaya (Ya ce): “Ya ku jama’ar aljannu, haqiqa kun samu mabiya da yawa daga cikin mutane.” Sai majivinta lamarinsu cikin mutane su ce: “Ya Ubangijinmu; mun dai daxaxa wa junanmu kuma mun kawo qarshen lokacin da Ka yanka mana.” Sai Ya ce: “Wuta ita ce makomarku, za ku dawwama a cikinta, sai dai abin da Allah Ya ga dama.” Lalle Ubangijinka Mai hikima ne, Mai yawan sani



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 129

وَكَذَٰلِكَ نُوَلِّي بَعۡضَ ٱلظَّـٰلِمِينَ بَعۡضَۢا بِمَا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ

Kuma kamar haka ne Muke xora wani sashi na azzalumai a kan wani sashi, saboda abin da suka kasance suna aikatawa



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 130

يَٰمَعۡشَرَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ رُسُلٞ مِّنكُمۡ يَقُصُّونَ عَلَيۡكُمۡ ءَايَٰتِي وَيُنذِرُونَكُمۡ لِقَآءَ يَوۡمِكُمۡ هَٰذَاۚ قَالُواْ شَهِدۡنَا عَلَىٰٓ أَنفُسِنَاۖ وَغَرَّتۡهُمُ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا وَشَهِدُواْ عَلَىٰٓ أَنفُسِهِمۡ أَنَّهُمۡ كَانُواْ كَٰفِرِينَ

Ya ku jama’ar aljannu da mutane, shin manzanni daga cikinku ba su zo muku ba, suna karanta muku ayoyina, kuma suna gargaxin ku game da saduwarku da wannan yini?” Sai su ce: “Mun ba da shaida a kan kawunanmu;” rayuwar duniya kuma ta ruxe su, kuma suka yi wa kansu shaidar cewa lalle su sun kasance kafirai



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 38

قَالَ ٱدۡخُلُواْ فِيٓ أُمَمٖ قَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِكُم مِّنَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ فِي ٱلنَّارِۖ كُلَّمَا دَخَلَتۡ أُمَّةٞ لَّعَنَتۡ أُخۡتَهَاۖ حَتَّىٰٓ إِذَا ٱدَّارَكُواْ فِيهَا جَمِيعٗا قَالَتۡ أُخۡرَىٰهُمۡ لِأُولَىٰهُمۡ رَبَّنَا هَـٰٓؤُلَآءِ أَضَلُّونَا فَـَٔاتِهِمۡ عَذَابٗا ضِعۡفٗا مِّنَ ٱلنَّارِۖ قَالَ لِكُلّٖ ضِعۡفٞ وَلَٰكِن لَّا تَعۡلَمُونَ

Sai Ya ce: “Ku shiga cikin jerin al’ummomin da suka shuxe kafinku na aljannu da mutane a cikin wuta.” Ko da yaushe wata al’umma ta shiga (wutar) sai ta la’anci ‘yar’uwarta; har sai lokacin da suka haxu a cikinta gaba xaya, sai na qarshensu su ce wa na farkonsu: “Ya Ubangijinmu, waxannan ne suka vatar da mu, don haka Ka ninka musu azabar wuta.” Sai Ya ce: “Kowanne yana da ninki, sai dai ku ba ku sani ba ne.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 179

وَلَقَدۡ ذَرَأۡنَا لِجَهَنَّمَ كَثِيرٗا مِّنَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِۖ لَهُمۡ قُلُوبٞ لَّا يَفۡقَهُونَ بِهَا وَلَهُمۡ أَعۡيُنٞ لَّا يُبۡصِرُونَ بِهَا وَلَهُمۡ ءَاذَانٞ لَّا يَسۡمَعُونَ بِهَآۚ أُوْلَـٰٓئِكَ كَٱلۡأَنۡعَٰمِ بَلۡ هُمۡ أَضَلُّۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡغَٰفِلُونَ

Kuma lalle haqiqa Mun halitta wa Jahannama da yawa daga cikin aljannu da mutane; ga su da zukata da ba sa hankalta da su, ga kuma idanu da ba sa kallo da su, ga kunnuwa da ba sa sauraro da su. Waxannan kamar dabbobi suke; a’a, sun ma fi (dabbobi) vacewa. Waxannan su ne gafalallu



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 119

إِلَّا مَن رَّحِمَ رَبُّكَۚ وَلِذَٰلِكَ خَلَقَهُمۡۗ وَتَمَّتۡ كَلِمَةُ رَبِّكَ لَأَمۡلَأَنَّ جَهَنَّمَ مِنَ ٱلۡجِنَّةِ وَٱلنَّاسِ أَجۡمَعِينَ

Sai wanda Ubangijinka Ya yi wa rahama. A kan haka kuwa Ya halicce su; kuma Kalmar Ubangijinka ta tabbata (cewa): Lalle zan cika Jahannama da aljannu da mutane baki xaya



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 17

وَحَفِظۡنَٰهَا مِن كُلِّ شَيۡطَٰنٖ رَّجِيمٍ

Kuma Muka kiyaye ta daga duk wani shaixani la’ananne



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 18

إِلَّا مَنِ ٱسۡتَرَقَ ٱلسَّمۡعَ فَأَتۡبَعَهُۥ شِهَابٞ مُّبِينٞ

Sai dai wanda ya yi satar sauraro, sannan sai tauraro mai harshen wuta ya biyo shi



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 27

وَٱلۡجَآنَّ خَلَقۡنَٰهُ مِن قَبۡلُ مِن نَّارِ ٱلسَّمُومِ

Aljani kuwa Mun halicce shi ne gabanin (halittar mutum) daga wuta mai tsananin zafi



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 88

قُل لَّئِنِ ٱجۡتَمَعَتِ ٱلۡإِنسُ وَٱلۡجِنُّ عَلَىٰٓ أَن يَأۡتُواْ بِمِثۡلِ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ لَا يَأۡتُونَ بِمِثۡلِهِۦ وَلَوۡ كَانَ بَعۡضُهُمۡ لِبَعۡضٖ ظَهِيرٗا

Ka ce da su: “Lalle da mutane da aljannu sun haxu kan su kawo irin wannan Alqur’anin, to ba za su zo da irinsa ba, ko da kuwa wasu sun zamanto suna taimaka wa wasu.”



Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 50

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ كَانَ مِنَ ٱلۡجِنِّ فَفَسَقَ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِۦٓۗ أَفَتَتَّخِذُونَهُۥ وَذُرِّيَّتَهُۥٓ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِي وَهُمۡ لَكُمۡ عَدُوُّۢۚ بِئۡسَ لِلظَّـٰلِمِينَ بَدَلٗا

Kuma ka tuna lokacin da Muka ce da mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu”, sai suka yi sujjadar in ban da Iblis, ya kasance kuwa daga cikin aljannu, sai ya sava wa umarnin Ubangijinsa. Yanzu kwa riqe shi shi da zurriyarsa masoya ba Ni ba, alhali kuwa su maqiyanku ne? Wannan canji na azzalumai ya munana



Capítulo: Suratul Anbiya

Verso : 82

وَمِنَ ٱلشَّيَٰطِينِ مَن يَغُوصُونَ لَهُۥ وَيَعۡمَلُونَ عَمَلٗا دُونَ ذَٰلِكَۖ وَكُنَّا لَهُمۡ حَٰفِظِينَ

Akwai kuma wasu aljannu da suke nutso don fito masa (da lu’u-lu’u) suna kuma yin wani aikin ban da wannan (kamar gine-gine); Mun zamanto kuma Masu kula da su))



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 17

وَحُشِرَ لِسُلَيۡمَٰنَ جُنُودُهُۥ مِنَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ وَٱلطَّيۡرِ فَهُمۡ يُوزَعُونَ

Aka kuma tattara wa Sulaimanu rundunoninsa na aljannu da mutane da kuma tsuntsaye, sai aka riqa turo su sahu-sahu



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 38

قَالَ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡمَلَؤُاْ أَيُّكُمۡ يَأۡتِينِي بِعَرۡشِهَا قَبۡلَ أَن يَأۡتُونِي مُسۡلِمِينَ

Sai (Sulaimanu) ya ce: “Ya ku manyan fada, wane ne daga cikinku zai zo min da gadon mulkinta tun kafin su zo min suna masu miqa wuya?”



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 39

قَالَ عِفۡرِيتٞ مِّنَ ٱلۡجِنِّ أَنَا۠ ءَاتِيكَ بِهِۦ قَبۡلَ أَن تَقُومَ مِن مَّقَامِكَۖ وَإِنِّي عَلَيۡهِ لَقَوِيٌّ أَمِينٞ

Sai wani ifritu[1] daga cikin aljannu ya ce: “Ni zan zo maka da shi kafin ka tashi daga majalisarka; lalle ni kuma mai qarfi ne amintacce game da (kawo) shi.”


1- Watau wani qaqqarfan aljani.


Capítulo: Suratun Namli

Verso : 40

قَالَ ٱلَّذِي عِندَهُۥ عِلۡمٞ مِّنَ ٱلۡكِتَٰبِ أَنَا۠ ءَاتِيكَ بِهِۦ قَبۡلَ أَن يَرۡتَدَّ إِلَيۡكَ طَرۡفُكَۚ فَلَمَّا رَءَاهُ مُسۡتَقِرًّا عِندَهُۥ قَالَ هَٰذَا مِن فَضۡلِ رَبِّي لِيَبۡلُوَنِيٓ ءَأَشۡكُرُ أَمۡ أَكۡفُرُۖ وَمَن شَكَرَ فَإِنَّمَا يَشۡكُرُ لِنَفۡسِهِۦۖ وَمَن كَفَرَ فَإِنَّ رَبِّي غَنِيّٞ كَرِيمٞ

Sai wani (mutum) wanda yake da ilimin Littafi (na Attaura) ya ce: “Ni zan kawo maka shi kafin ka qifta idonka!” To lokacin da (Sulaimanu) ya gan shi ga shi nan a gabansa sai ya ce: “Wannan yana daga falalar Ubangijina don Ya jarraba ni (Ya gani) shin zan gode ne ko zan butulce; to duk wanda ya gode kansa ya yi wa; wanda kuwa ya butulce, to lalle Ubangijina Mawadaci ne, Mai karamci.”



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 12

وَلِسُلَيۡمَٰنَ ٱلرِّيحَ غُدُوُّهَا شَهۡرٞ وَرَوَاحُهَا شَهۡرٞۖ وَأَسَلۡنَا لَهُۥ عَيۡنَ ٱلۡقِطۡرِۖ وَمِنَ ٱلۡجِنِّ مَن يَعۡمَلُ بَيۡنَ يَدَيۡهِ بِإِذۡنِ رَبِّهِۦۖ وَمَن يَزِغۡ مِنۡهُمۡ عَنۡ أَمۡرِنَا نُذِقۡهُ مِنۡ عَذَابِ ٱلسَّعِيرِ

Kuma (Muka hore wa) Sulaimanu iska, tafiyarta ta safe wata guda ce, ta yamma ma kuma wata guda ce; Muka kuma vuvvugo masa da narkakkiyar tagulla tana gudana. Daga aljannu kuma akwai masu aiki a wajensa da umarnin Ubangijinsa; wanda kuwa ya kauce wa umarninmu daga cikinsu, to za Mu xanxana masa azabar wutar Sa’ira



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 13

يَعۡمَلُونَ لَهُۥ مَا يَشَآءُ مِن مَّحَٰرِيبَ وَتَمَٰثِيلَ وَجِفَانٖ كَٱلۡجَوَابِ وَقُدُورٖ رَّاسِيَٰتٍۚ ٱعۡمَلُوٓاْ ءَالَ دَاوُۥدَ شُكۡرٗاۚ وَقَلِيلٞ مِّنۡ عِبَادِيَ ٱلشَّكُورُ

Suna aikata masa abubuwan da yake bukata na manya-manyan gine-gine[1] da mutum-mutumi[2] da akusa manya-manya kamar tafkuna da kafaffun tukwane. Ya ku iyalin Dawuda, ku yi aikin (xa’a) domin godiya. Masu godiya daga bayina kuwa kaxan ne


1- Watau wuraren ibada.


2- A wancan lokacin ba a haramta yin su ba. Sai bayan zuwan Annabi () ne ya haramta suranta su ko gina su.


Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 14

فَلَمَّا قَضَيۡنَا عَلَيۡهِ ٱلۡمَوۡتَ مَا دَلَّهُمۡ عَلَىٰ مَوۡتِهِۦٓ إِلَّا دَآبَّةُ ٱلۡأَرۡضِ تَأۡكُلُ مِنسَأَتَهُۥۖ فَلَمَّا خَرَّ تَبَيَّنَتِ ٱلۡجِنُّ أَن لَّوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ ٱلۡغَيۡبَ مَا لَبِثُواْ فِي ٱلۡعَذَابِ ٱلۡمُهِينِ

Sannan lokacin da Muka qaddara masa mutuwa ba abin da ya nuna musu mutuwarsa sai gara da ta riqa cin sandarsa[1]; to lokacin da ya faxi sai aljannu suka gane cewa da sun san gaibu da ba su zauna cikin azabar wulaqanci ba


1- Sandarsa da yake tsaye a kanta.


Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 41

قَالُواْ سُبۡحَٰنَكَ أَنتَ وَلِيُّنَا مِن دُونِهِمۖ بَلۡ كَانُواْ يَعۡبُدُونَ ٱلۡجِنَّۖ أَكۡثَرُهُم بِهِم مُّؤۡمِنُونَ

Suka ce: “Tsarki ya tabbata a gare Ka, Kai ne Majivincinmu ba su ba.” Ba haka ba ne, sun kasance suna bauta wa aljannu ne; mafiya yawansu masu yin imani da su ne



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 6

إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِزِينَةٍ ٱلۡكَوَاكِبِ

Lalle Mun qawata sama ta kusa da ado na taurari



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 7

وَحِفۡظٗا مِّن كُلِّ شَيۡطَٰنٖ مَّارِدٖ

Da kuma tsaro daga dukkan wani shaixan mai tsaurin kai



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 8

لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلۡمَلَإِ ٱلۡأَعۡلَىٰ وَيُقۡذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٖ

Ba kuma za su iya jiyowa ba (daga asirin) mala’iku na sama, sai a yi ta jifan su ta kowane vangare



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 9

دُحُورٗاۖ وَلَهُمۡ عَذَابٞ وَاصِبٌ

Don kora; suna kuma da wata azaba dawwamamma



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 10

إِلَّا مَنۡ خَطِفَ ٱلۡخَطۡفَةَ فَأَتۡبَعَهُۥ شِهَابٞ ثَاقِبٞ

Sai dai wanda ya yi fautowar jin, to sai wani tauraro mai haske da quna ya biyo shi



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 25

۞وَقَيَّضۡنَا لَهُمۡ قُرَنَآءَ فَزَيَّنُواْ لَهُم مَّا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُمۡ وَحَقَّ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقَوۡلُ فِيٓ أُمَمٖ قَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِهِم مِّنَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ خَٰسِرِينَ

Muka kuma haxa su da abokai (shaixanu), sai suka qawata musu abin da yake gabansu (na duniya) da abin da yake bayansu (na musun alqiyama), sai kalmar (azaba) ta tabbata a kansu (na zamantowa) cikin al’ummun da suka gabace su na aljannu da mutane; lalle su, sun kasance hasararru



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 29

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ رَبَّنَآ أَرِنَا ٱلَّذَيۡنِ أَضَلَّانَا مِنَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ نَجۡعَلۡهُمَا تَحۡتَ أَقۡدَامِنَا لِيَكُونَا مِنَ ٱلۡأَسۡفَلِينَ

Waxanda kuma suka kafirta suka ce: “Ya Ubangijinmu, Ka nuna mana waxanda suka vatar da mu daga aljannu da mutane, mu sanya su a qarqashin dugaduganmu don su zamanto cikin na can qasan qasa.”