Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 281

وَٱتَّقُواْ يَوۡمٗا تُرۡجَعُونَ فِيهِ إِلَى ٱللَّهِۖ ثُمَّ تُوَفَّىٰ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا كَسَبَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Kuma ku kiyayi wani yini da za a mayar da ku zuwa ga Allah a cikinsa, sannan kowane rai za a cika masa abin da ya aiwatar na aiki, kuma su ba za a zalunce su ba



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 282

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا تَدَايَنتُم بِدَيۡنٍ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗى فَٱكۡتُبُوهُۚ وَلۡيَكۡتُب بَّيۡنَكُمۡ كَاتِبُۢ بِٱلۡعَدۡلِۚ وَلَا يَأۡبَ كَاتِبٌ أَن يَكۡتُبَ كَمَا عَلَّمَهُ ٱللَّهُۚ فَلۡيَكۡتُبۡ وَلۡيُمۡلِلِ ٱلَّذِي عَلَيۡهِ ٱلۡحَقُّ وَلۡيَتَّقِ ٱللَّهَ رَبَّهُۥ وَلَا يَبۡخَسۡ مِنۡهُ شَيۡـٔٗاۚ فَإِن كَانَ ٱلَّذِي عَلَيۡهِ ٱلۡحَقُّ سَفِيهًا أَوۡ ضَعِيفًا أَوۡ لَا يَسۡتَطِيعُ أَن يُمِلَّ هُوَ فَلۡيُمۡلِلۡ وَلِيُّهُۥ بِٱلۡعَدۡلِۚ وَٱسۡتَشۡهِدُواْ شَهِيدَيۡنِ مِن رِّجَالِكُمۡۖ فَإِن لَّمۡ يَكُونَا رَجُلَيۡنِ فَرَجُلٞ وَٱمۡرَأَتَانِ مِمَّن تَرۡضَوۡنَ مِنَ ٱلشُّهَدَآءِ أَن تَضِلَّ إِحۡدَىٰهُمَا فَتُذَكِّرَ إِحۡدَىٰهُمَا ٱلۡأُخۡرَىٰۚ وَلَا يَأۡبَ ٱلشُّهَدَآءُ إِذَا مَا دُعُواْۚ وَلَا تَسۡـَٔمُوٓاْ أَن تَكۡتُبُوهُ صَغِيرًا أَوۡ كَبِيرًا إِلَىٰٓ أَجَلِهِۦۚ ذَٰلِكُمۡ أَقۡسَطُ عِندَ ٱللَّهِ وَأَقۡوَمُ لِلشَّهَٰدَةِ وَأَدۡنَىٰٓ أَلَّا تَرۡتَابُوٓاْ إِلَّآ أَن تَكُونَ تِجَٰرَةً حَاضِرَةٗ تُدِيرُونَهَا بَيۡنَكُمۡ فَلَيۡسَ عَلَيۡكُمۡ جُنَاحٌ أَلَّا تَكۡتُبُوهَاۗ وَأَشۡهِدُوٓاْ إِذَا تَبَايَعۡتُمۡۚ وَلَا يُضَآرَّ كَاتِبٞ وَلَا شَهِيدٞۚ وَإِن تَفۡعَلُواْ فَإِنَّهُۥ فُسُوقُۢ بِكُمۡۗ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَۖ وَيُعَلِّمُكُمُ ٱللَّهُۗ وَٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka ba wa junanku bashi zuwa wani lokaci sananne, to ku rubuta shi, kuma a sami wani marubuci da zai rubuta a tsakaninku da adalci, kuma marubucin kar ya qi rubutawa kamar yadda Allah ya sanar da shi. Don haka ya rubuta, kuma shi wanda haqqi yake kansa sai ya yi shifta gare shi, kuma ya ji tsoron Allah Ubangijinsa, kuma kada ya tauye wani abu a cikinsa. To idan wanda haqqi yake kansa ya kasance wawa ne ko mai rauni ko ba shi da ikon ya yi shifta shi da kansa, to sai majivincin lamarinsa ya yi shifta (a madadinsa) da adalci. Kuma ku kafa shaidu biyu cikin mazajenku; kuma idan ba su kasance mazaje biyu ba, to sai a nemi namiji xaya da mata biyu daga shaidun da kuka yarda da su, saboda idan xaya daga cikinsu ta manta sai xayar ta tuna mata, kuma kada shaidun su qi zuwa idan an kiraye su, kuma kada ku qosa, ku rubuta shi, kaxan ne ko da yawa, zuwa cikar wa’adinsa. Abin da aka ambata mukun nan shi ne ya fi zama adalci a wajen Allah, kuma ya fi daidaita shaida, kuma shi ya fi kusata ku ta yadda ba za ku yi shakka ba, sai dai idan ya kasance ciniki ne hannu da hannu da kuke gudanar da shi tsakaninku; to babu laifi a kanku idan ba ku rubuta shi ba. Kuma ku kafa shaida idan kun yi hulxa ta ciniki, kuma kada marubuci ya yi cuta, haka shi ma mai shaida (kada ya yi cuta)[1]. Idan kuwa har kuka aikata haka, to lalle wannan fasiqanci ne a gare ku. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma Allah Yana sanar da ku (dokokinsa). Kuma Allah Masanin komai ne


1- Hakanan ayar tana nufin cewa, su ma kuma kada a cutar da su.


Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 18

شَهِدَ ٱللَّهُ أَنَّهُۥ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَأُوْلُواْ ٱلۡعِلۡمِ قَآئِمَۢا بِٱلۡقِسۡطِۚ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Allah Ya shaida cewa, babu abin bauta wa da gaskiya sai Shi, haka mala’iku ma da ma’abota ilimi, Tsayayye ne da adalci. Babu abin bauta wa da gaskiya sai Shi, Mabuwayi, Mai hikima



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 25

فَكَيۡفَ إِذَا جَمَعۡنَٰهُمۡ لِيَوۡمٖ لَّا رَيۡبَ فِيهِ وَوُفِّيَتۡ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا كَسَبَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

To yaya halinsu zai kasance idan Muka tara su a wani yini da babu shakka game da shi, kuma kowane rai za a saka masa da abin da ya aikata, kuma su ba za a zalunce su ba?



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 64

قُلۡ يَـٰٓأَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ تَعَالَوۡاْ إِلَىٰ كَلِمَةٖ سَوَآءِۭ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَكُمۡ أَلَّا نَعۡبُدَ إِلَّا ٱللَّهَ وَلَا نُشۡرِكَ بِهِۦ شَيۡـٔٗا وَلَا يَتَّخِذَ بَعۡضُنَا بَعۡضًا أَرۡبَابٗا مِّن دُونِ ٱللَّهِۚ فَإِن تَوَلَّوۡاْ فَقُولُواْ ٱشۡهَدُواْ بِأَنَّا مُسۡلِمُونَ

Ka ce: “Ya ku Ma’abota Littafi, ku taho ga wata kalma mai daidaitawa tsakaninmu da ku cewa, kar mu bauta wa kowa sai Allah, kuma kar mu haxa Shi da wani, kuma kada wani sashi a cikinmu ya riqi wani sashi a matsayin abin bauta ba Allah ba.” Idan kuwa sun ba da baya, to ku ce: “Ku shaida cewa, lalle mu Musulmi ne.”



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 3

وَإِنۡ خِفۡتُمۡ أَلَّا تُقۡسِطُواْ فِي ٱلۡيَتَٰمَىٰ فَٱنكِحُواْ مَا طَابَ لَكُم مِّنَ ٱلنِّسَآءِ مَثۡنَىٰ وَثُلَٰثَ وَرُبَٰعَۖ فَإِنۡ خِفۡتُمۡ أَلَّا تَعۡدِلُواْ فَوَٰحِدَةً أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُكُمۡۚ ذَٰلِكَ أَدۡنَىٰٓ أَلَّا تَعُولُواْ

Kuma idan kun ji tsoron cewa ba za ku iya yin adalci ba dangane da marayu, to ku auri matan da kuke so, ko dai bibbiyu ko uku-uku ko kuma hurhuxu. To idan kun ji tsoron ba za ku iya yin adalci ba, to sai ku taqaita a kan xaya ko kuma abin da kuka mallaka na qwarqwarori. Hakan shi ya fi nisanta ku daga zalunci



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 58

۞إِنَّ ٱللَّهَ يَأۡمُرُكُمۡ أَن تُؤَدُّواْ ٱلۡأَمَٰنَٰتِ إِلَىٰٓ أَهۡلِهَا وَإِذَا حَكَمۡتُم بَيۡنَ ٱلنَّاسِ أَن تَحۡكُمُواْ بِٱلۡعَدۡلِۚ إِنَّ ٱللَّهَ نِعِمَّا يَعِظُكُم بِهِۦٓۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ سَمِيعَۢا بَصِيرٗا

Lalle Allah Yana umartar ku da ku mayar da amanoni ga masu su, kuma idan za ku yi hukunci a tsakanin mutane, to ku yi hukunci da adalci. Lalle kam madalla da abin da Allah Yake muku wa’azi da shi. Lalle Allah Ya kasance Mai ji ne, Mai gani



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 65

فَلَا وَرَبِّكَ لَا يُؤۡمِنُونَ حَتَّىٰ يُحَكِّمُوكَ فِيمَا شَجَرَ بَيۡنَهُمۡ ثُمَّ لَا يَجِدُواْ فِيٓ أَنفُسِهِمۡ حَرَجٗا مِّمَّا قَضَيۡتَ وَيُسَلِّمُواْ تَسۡلِيمٗا

To ina rantsuwa da Ubangijinka, ba za su yi imani ba har sai sun kai hukunci a gabanka game da duk abin da ya faru na savani a tsakaninsu, sannan ba su ji wani qunci a cikin zukatansu ba game da abin da ka zartar na hukunci, kuma su miqa wuya miqawa gaba xaya



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 105

إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ لِتَحۡكُمَ بَيۡنَ ٱلنَّاسِ بِمَآ أَرَىٰكَ ٱللَّهُۚ وَلَا تَكُن لِّلۡخَآئِنِينَ خَصِيمٗا

Lalle Mu Mun saukar maka da Littafi da gaskiya domin ka yi hukunci a tsakanin mutane da abin da Allah Ya sanar da kai, kuma kada ka zamo mai ba da kariya ga maha’inta



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 129

وَلَن تَسۡتَطِيعُوٓاْ أَن تَعۡدِلُواْ بَيۡنَ ٱلنِّسَآءِ وَلَوۡ حَرَصۡتُمۡۖ فَلَا تَمِيلُواْ كُلَّ ٱلۡمَيۡلِ فَتَذَرُوهَا كَٱلۡمُعَلَّقَةِۚ وَإِن تُصۡلِحُواْ وَتَتَّقُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma ba za ku iya yin adalci (na soyayya) a tsakankanin mata ba, ko da kuna matuqar son yin hakan. To kada ku karkata, karkata ta gaba xaya, ta yadda za ku qyale xayar kamar ratayayya[1]. Amma idan za ku kyautata kuma ku yi taqawa, to lalle Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai


1- Watau su karkata ga xaya su qyale xayar a rataye, ita ba a sake ta ba ita kuma ba mai jin daxin aure ba.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 135

۞يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ كُونُواْ قَوَّـٰمِينَ بِٱلۡقِسۡطِ شُهَدَآءَ لِلَّهِ وَلَوۡ عَلَىٰٓ أَنفُسِكُمۡ أَوِ ٱلۡوَٰلِدَيۡنِ وَٱلۡأَقۡرَبِينَۚ إِن يَكُنۡ غَنِيًّا أَوۡ فَقِيرٗا فَٱللَّهُ أَوۡلَىٰ بِهِمَاۖ فَلَا تَتَّبِعُواْ ٱلۡهَوَىٰٓ أَن تَعۡدِلُواْۚ وَإِن تَلۡوُۥٓاْ أَوۡ تُعۡرِضُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku zamo masu tsayawa da adalci, kuna masu ba da shaida don Allah, ko da kuwa a kan kawunanku ne ko a kan mahaifanku ko a kan dangi makusanta. Idan ya kasance mawadaci ne ko matalauci, to Allah Shi ne Ya fi sanin abin da ya fi cancanta gare su[1]; don haka kada ku bi son zuciyarku ku qi yin adalci. Idan kuwa kuka karkatar da shaida ko kuka qi ba da ita, to lalle Allah Ya kasance Mai cikakken sanin abin da kuke aikatawa ne


1- Watau da mai wadata da matalauci duk al'amuransu na ga Allah, ya fi kowa sanin abin da ya fi zama maslaha a gare su.


Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 8

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ كُونُواْ قَوَّـٰمِينَ لِلَّهِ شُهَدَآءَ بِٱلۡقِسۡطِۖ وَلَا يَجۡرِمَنَّكُمۡ شَنَـَٔانُ قَوۡمٍ عَلَىٰٓ أَلَّا تَعۡدِلُواْۚ ٱعۡدِلُواْ هُوَ أَقۡرَبُ لِلتَّقۡوَىٰۖ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَۚ إِنَّ ٱللَّهَ خَبِيرُۢ بِمَا تَعۡمَلُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku zamo masu tsayawa qyam da haqqoqin Allah, kuna masu yin shaida da adalci; kuma kada qin waxansu mutane ya hana ku yi musu adalci. Ku yi adalci shi ne mafi kusanci ga taqawa. Kuma ku kiyaye dokokin Allah. Lalle Allah Mai cikakken sanin abin da kuke aikatawa ne



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 42

سَمَّـٰعُونَ لِلۡكَذِبِ أَكَّـٰلُونَ لِلسُّحۡتِۚ فَإِن جَآءُوكَ فَٱحۡكُم بَيۡنَهُمۡ أَوۡ أَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡۖ وَإِن تُعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ فَلَن يَضُرُّوكَ شَيۡـٔٗاۖ وَإِنۡ حَكَمۡتَ فَٱحۡكُم بَيۡنَهُم بِٱلۡقِسۡطِۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُقۡسِطِينَ

(Su ne) masu yawan sauraron qarya, masu yawan cin haram. Don haka idan sun zo maka, to ka yi musu hukunci, ko ka kau da kai daga gare su; idan kuwa ka kawar da kai daga gare su, to ba za su cutar da kai da komai ba; idan kuwa za ka yi hukuncin, to ka yi hukunci tsakaninsu da adalci. Lalle Allah Yana son masu adalci



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 45

وَكَتَبۡنَا عَلَيۡهِمۡ فِيهَآ أَنَّ ٱلنَّفۡسَ بِٱلنَّفۡسِ وَٱلۡعَيۡنَ بِٱلۡعَيۡنِ وَٱلۡأَنفَ بِٱلۡأَنفِ وَٱلۡأُذُنَ بِٱلۡأُذُنِ وَٱلسِّنَّ بِٱلسِّنِّ وَٱلۡجُرُوحَ قِصَاصٞۚ فَمَن تَصَدَّقَ بِهِۦ فَهُوَ كَفَّارَةٞ لَّهُۥۚ وَمَن لَّمۡ يَحۡكُم بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Kuma Mun wajabta a kansu a cikinta (Attaura), lalle rai da rai, kuma ido da ido, kuma hanci da hanci, kuma kunne da kunne, kuma haqori da haqori, raunuka kuma a yi ramuwa. To duk wanda ya yi sadaka da shi, to wannan kaffara ce gare shi. Duk wanda bai yi hukunci da abin da Allah Ya saukar ba kuwa, to waxannan su ne azzalumai



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 152

وَلَا تَقۡرَبُواْ مَالَ ٱلۡيَتِيمِ إِلَّا بِٱلَّتِي هِيَ أَحۡسَنُ حَتَّىٰ يَبۡلُغَ أَشُدَّهُۥۚ وَأَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَٱلۡمِيزَانَ بِٱلۡقِسۡطِۖ لَا نُكَلِّفُ نَفۡسًا إِلَّا وُسۡعَهَاۖ وَإِذَا قُلۡتُمۡ فَٱعۡدِلُواْ وَلَوۡ كَانَ ذَا قُرۡبَىٰۖ وَبِعَهۡدِ ٱللَّهِ أَوۡفُواْۚ ذَٰلِكُمۡ وَصَّىٰكُم بِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تَذَكَّرُونَ

“Kuma kada ku kusanci dukiyar maraya sai da kyakkyawar niyya, har sai qarfinsa ya kawo; kuma ku cika ma’auni na mudu da na nauyi bisa adalci; ba ma xora wa rai sai abin da zai iya. Kuma idan za ku yi magana to ku yi adalci, ko da kuwa a kan xan’uwa ne na kusa; kuma lalle ku cika alqawarin Allah. Wannan ne abin da (Allah) Yake yi muku wasicci da shi, don ku wa’azantu.”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 161

قُلۡ إِنَّنِي هَدَىٰنِي رَبِّيٓ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ دِينٗا قِيَمٗا مِّلَّةَ إِبۡرَٰهِيمَ حَنِيفٗاۚ وَمَا كَانَ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Ka ce: “Lalle ni, Ubangijina Ya shiryar da ni zuwa ga tafarki madaidaici, shi ne addini miqaqqe, addinin Ibrahimu wanda ya karkace wa varna, kuma bai zama daga masu shirka ba.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 29

قُلۡ أَمَرَ رَبِّي بِٱلۡقِسۡطِۖ وَأَقِيمُواْ وُجُوهَكُمۡ عِندَ كُلِّ مَسۡجِدٖ وَٱدۡعُوهُ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَۚ كَمَا بَدَأَكُمۡ تَعُودُونَ

Ka ce: “Ubangijina Ya yi umarni da adalci; kuma ku tsai da fuskokinku (don Allah) a kowace salla, ku kuma roqe Shi kuna masu tsantsanta addini gare Shi. Kamar yadda Ya fari halittarku, haka za ku koma (wurinsa)



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 47

وَلِكُلِّ أُمَّةٖ رَّسُولٞۖ فَإِذَا جَآءَ رَسُولُهُمۡ قُضِيَ بَيۡنَهُم بِٱلۡقِسۡطِ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Kowacce al’umma kuma tana da manzo. To idan manzonsu ya zo (suka qaryata shi) to sai a yi hukunci a tsakaninsu da adalci, su kuma ba za a zalunce su ba



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 54

وَلَوۡ أَنَّ لِكُلِّ نَفۡسٖ ظَلَمَتۡ مَا فِي ٱلۡأَرۡضِ لَٱفۡتَدَتۡ بِهِۦۗ وَأَسَرُّواْ ٱلنَّدَامَةَ لَمَّا رَأَوُاْ ٱلۡعَذَابَۖ وَقُضِيَ بَيۡنَهُم بِٱلۡقِسۡطِ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Da a ce kowane rai da ya yi zalunci ya mallaki duk abin da yake bayan qasa, to lalle da ya fanshi kansa da shi. Suka kuwa voye nadama a lokacin da suka ga azaba; an kuma yi hukunci tsakaninsu na adalci; ba kuma za a zalunce su ba



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 90

۞إِنَّ ٱللَّهَ يَأۡمُرُ بِٱلۡعَدۡلِ وَٱلۡإِحۡسَٰنِ وَإِيتَآيِٕ ذِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَيَنۡهَىٰ عَنِ ٱلۡفَحۡشَآءِ وَٱلۡمُنكَرِ وَٱلۡبَغۡيِۚ يَعِظُكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَذَكَّرُونَ

Lalle Allah Yana umarni da yin adalci da kyautatawa da kuma bai wa makusanta (taimako), Yana kuma hana alfasha da mummunan aiki da zalunci. Yana gargaxin ku don ku wa’azantu



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 111

۞يَوۡمَ تَأۡتِي كُلُّ نَفۡسٖ تُجَٰدِلُ عَن نَّفۡسِهَا وَتُوَفَّىٰ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا عَمِلَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Ranar da kowanne rai zai zo yana kare kansa, kuma a cika wa kowanne rai (sakamakon) abin da ya aikata, kuma su ba za a zalunce su ba



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 71

يَوۡمَ نَدۡعُواْ كُلَّ أُنَاسِۭ بِإِمَٰمِهِمۡۖ فَمَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَأُوْلَـٰٓئِكَ يَقۡرَءُونَ كِتَٰبَهُمۡ وَلَا يُظۡلَمُونَ فَتِيلٗا

Ranar da za Mu kirawo kowanne (jinsin) mutane da shugabansu, sannan wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na dama to waxannan za su karanta littafinsu, sannan ba za a zalunce su ko da gwargwadon zaren qwallon dabino ne ba



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 62

وَلَا نُكَلِّفُ نَفۡسًا إِلَّا وُسۡعَهَاۚ وَلَدَيۡنَا كِتَٰبٞ يَنطِقُ بِٱلۡحَقِّ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Ba Ma kuwa xora wa kowane rai wani abu sai wanda zai iya. Kuma a wurinmu akwai littafi da yake furuci da gaskiya, kuma su ba za a zalunce su ba



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 5

ٱدۡعُوهُمۡ لِأٓبَآئِهِمۡ هُوَ أَقۡسَطُ عِندَ ٱللَّهِۚ فَإِن لَّمۡ تَعۡلَمُوٓاْ ءَابَآءَهُمۡ فَإِخۡوَٰنُكُمۡ فِي ٱلدِّينِ وَمَوَٰلِيكُمۡۚ وَلَيۡسَ عَلَيۡكُمۡ جُنَاحٞ فِيمَآ أَخۡطَأۡتُم بِهِۦ وَلَٰكِن مَّا تَعَمَّدَتۡ قُلُوبُكُمۡۚ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمًا

Ku danganta su (‘ya’yan riqo) ga iyayensu maza shi ne adalci a wurin Allah. Amma idan ba ku san iyayensu maza ba, to ‘yan’uwanku ne a addini, kuma bararrun bayinku ne. Babu kuma laifi a kanku game da abin da kuka yi kuskuren yin sa, sai dai abin da zukatanku suka yi gangancin (aikatawa). Allah kuwa Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 69

وَأَشۡرَقَتِ ٱلۡأَرۡضُ بِنُورِ رَبِّهَا وَوُضِعَ ٱلۡكِتَٰبُ وَجِاْيٓءَ بِٱلنَّبِيِّـۧنَ وَٱلشُّهَدَآءِ وَقُضِيَ بَيۡنَهُم بِٱلۡحَقِّ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Qasa kuma ta yi haske da hasken Ubangijinta, aka kuma ajiye takardu (na ayyuka), kuma aka zo da annabawa da masu shaida, kuma aka yi hukunci a tsakaninsu da gaskiya, ba kuma za a zalunce su ba



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 70

وَوُفِّيَتۡ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا عَمِلَتۡ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِمَا يَفۡعَلُونَ

Aka kuma yi wa kowane rai cikakken sakamakon abin da ya aikata, Shi ko (Allah) Yana sane da abin da suke aikatawa



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 20

وَٱللَّهُ يَقۡضِي بِٱلۡحَقِّۖ وَٱلَّذِينَ يَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ لَا يَقۡضُونَ بِشَيۡءٍۗ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡبَصِيرُ

Allah Yana hukunci da gaskiya; waxanda kuwa suke bauta wa wanda ba Shi ba, ba sa hukunta komai. Haqiqa Allah Shi ne Mai ji, Mai gani



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 15

فَلِذَٰلِكَ فَٱدۡعُۖ وَٱسۡتَقِمۡ كَمَآ أُمِرۡتَۖ وَلَا تَتَّبِعۡ أَهۡوَآءَهُمۡۖ وَقُلۡ ءَامَنتُ بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ مِن كِتَٰبٖۖ وَأُمِرۡتُ لِأَعۡدِلَ بَيۡنَكُمُۖ ٱللَّهُ رَبُّنَا وَرَبُّكُمۡۖ لَنَآ أَعۡمَٰلُنَا وَلَكُمۡ أَعۡمَٰلُكُمۡۖ لَا حُجَّةَ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَكُمُۖ ٱللَّهُ يَجۡمَعُ بَيۡنَنَاۖ وَإِلَيۡهِ ٱلۡمَصِيرُ

Saboda wannan sai ka yi kira (zuwa ga addinin Allah), kuma ka tsaya kyam kamar yadda aka umarce ka, kada ka bi son ransu; ka kuma ce: “Na yi imani da abin da Allah Ya saukar na littattafai; an kuma umarce ni da yin adalci a tsakaninku; Allah ne Ubangijinmu kuma Ubangijinku; (sakamakon) ayyukanmu namu ne, ku ma (sakamakon) ayyukanku naku ne; babu wata jayayya a tsakaninmu da ku; Allah zai tara mu; kuma zuwa gare Shi ne kaxai makoma



Capítulo: Suratul Jasiya

Verso : 22

وَخَلَقَ ٱللَّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّ وَلِتُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Allah kuma Ya halicci sammai da qasa da gaskiya, don kuma a saka wa kowane rai irin abin da ya aikata, alhali kuma su ba za a zalunce su ba



Capítulo: Suratul Ahqaf 

Verso : 19

وَلِكُلّٖ دَرَجَٰتٞ مِّمَّا عَمِلُواْۖ وَلِيُوَفِّيَهُمۡ أَعۡمَٰلَهُمۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Kuma kowane yana da darajoji (na sakamakon) abin da suka aikata; don kuma tabbas zai cika musu sakamakon ayyukansu, ba kuma za a zalunce su ba