Capítulo: Suratun Nur

Verso : 41

أَلَمۡ تَرَ أَنَّ ٱللَّهَ يُسَبِّحُ لَهُۥ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَٱلطَّيۡرُ صَـٰٓفَّـٰتٖۖ كُلّٞ قَدۡ عَلِمَ صَلَاتَهُۥ وَتَسۡبِيحَهُۥۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِمَا يَفۡعَلُونَ

Ba ka gani cewa Allah duk abin da yake sammai da qasa yana tasbihi ne gare Shi, haka tsuntsaye kuma sun buxe fukafukansu sun yi sahu, kowanne xayansu ya san sallarsa da tasbihinsa? Allah kuwa Masanin abin da suke aikatawa ne



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 64

أَلَآ إِنَّ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ قَدۡ يَعۡلَمُ مَآ أَنتُمۡ عَلَيۡهِ وَيَوۡمَ يُرۡجَعُونَ إِلَيۡهِ فَيُنَبِّئُهُم بِمَا عَمِلُواْۗ وَٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمُۢ

Ku saurara, lalle abin da yake sammai da qasa na Allah ne; haqiqa Yana sane da abin da ku kuke kansa, da kuma ranar da za a komar da su zuwa gare Shi, sannan Ya ba su labarin abin da suka aikata. Allah Masanin komai ne



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 6

قُلۡ أَنزَلَهُ ٱلَّذِي يَعۡلَمُ ٱلسِّرَّ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ إِنَّهُۥ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Ka ce (da su): “Wanda Yake sane da asirin sammai da qasa Shi Ya saukar da shi. Lalle Shi Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 188

قَالَ رَبِّيٓ أَعۡلَمُ بِمَا تَعۡمَلُونَ

(Shu’aibu) Ya ce: “Ubangijina Ya fi kowa sanin abin da kuke aikatawa.”



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 25

أَلَّاۤ يَسۡجُدُواْۤ لِلَّهِ ٱلَّذِي يُخۡرِجُ ٱلۡخَبۡءَ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَيَعۡلَمُ مَا تُخۡفُونَ وَمَا تُعۡلِنُونَ

“Don kada su yi sujjada ga Allah wanda Yake fito da abin da yake voye a cikin sammai da qasa, kuma Yake sane da abin da kuke voyewa da abin da kuke bayyanawa



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 65

قُل لَّا يَعۡلَمُ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ ٱلۡغَيۡبَ إِلَّا ٱللَّهُۚ وَمَا يَشۡعُرُونَ أَيَّانَ يُبۡعَثُونَ

Ka ce (da su): “Duk wanda yake cikin sammai da qasa in ba Allah ba ba wanda ya san gaibu. Su kuma ba su san lokacin da za a tashe su ba.”



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 74

وَإِنَّ رَبَّكَ لَيَعۡلَمُ مَا تُكِنُّ صُدُورُهُمۡ وَمَا يُعۡلِنُونَ

Lalle kuma Ubangijinka tabbas Yana sane da abin da zukatansu suke voyewa, da kuma abin da suke bayyanawa



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 88

وَتَرَى ٱلۡجِبَالَ تَحۡسَبُهَا جَامِدَةٗ وَهِيَ تَمُرُّ مَرَّ ٱلسَّحَابِۚ صُنۡعَ ٱللَّهِ ٱلَّذِيٓ أَتۡقَنَ كُلَّ شَيۡءٍۚ إِنَّهُۥ خَبِيرُۢ بِمَا تَفۡعَلُونَ

Kuma za ka ga duwatsu ka zaci a tsaye suke cak, alhali kuwa su suna tafiya ne irin tafiyar gizagizai. Aikin Allah kenan wanda Ya kyautata halittar kowane irin abu. Lalle Shi Masanin abin da kuke aikatawa ne



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 56

إِنَّكَ لَا تَهۡدِي مَنۡ أَحۡبَبۡتَ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ يَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ

Lalle kai ba ka iya shiryar da wanda ka so, sai dai Allah ne Yana shiryar da wanda Ya ga dama. Shi kuma ne Ya san masu shiryuwa



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 69

وَرَبُّكَ يَعۡلَمُ مَا تُكِنُّ صُدُورُهُمۡ وَمَا يُعۡلِنُونَ

Kuma Ubangijinka Ya san abin da zukatansu suke voyewa da kuma abin da suke bayyanawa



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 85

إِنَّ ٱلَّذِي فَرَضَ عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ لَرَآدُّكَ إِلَىٰ مَعَادٖۚ قُل رَّبِّيٓ أَعۡلَمُ مَن جَآءَ بِٱلۡهُدَىٰ وَمَنۡ هُوَ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Lalle Wanda Ya saukar maka da Alqur’ani tabbas zai mayar da kai zuwa makomarka[1]. Ka ce: “Ubangijina Shi Ya san wanda ya zo da shiriya da kuma wanda yake cikin vata mabayyani.”


1- Watau zai mayar da shi mahaifarsa garin Makka; ko kuma zai mayar da shi makomarsa ta qarshe watau Aljanna.


Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 10

وَمِنَ ٱلنَّاسِ مَن يَقُولُ ءَامَنَّا بِٱللَّهِ فَإِذَآ أُوذِيَ فِي ٱللَّهِ جَعَلَ فِتۡنَةَ ٱلنَّاسِ كَعَذَابِ ٱللَّهِۖ وَلَئِن جَآءَ نَصۡرٞ مِّن رَّبِّكَ لَيَقُولُنَّ إِنَّا كُنَّا مَعَكُمۡۚ أَوَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَعۡلَمَ بِمَا فِي صُدُورِ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma cikin mutane akwai mai cewa: “Mun yi imani da Allah,” to idan aka cuce shi a kan hanyar Allah sai yakan xauki fitinar mutane kamar azabar Allah, lalle kuwa idan wata nasara ta zo daga Ubangijinka, tabbas zai riqa cewa: “Lalle mu mun kasance tare da ku.” Yanzu Allah ba Shi Ya fi kowa sanin abin da ke cikin zukatan talikai ba?



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 42

إِنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ مَا يَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ مِن شَيۡءٖۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Lalle Allah Yana sane da kowane abu da suke bauta wa wanda ba Shi ba. Kuma Shi ne Mabuwayi, Mai hikima



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 45

ٱتۡلُ مَآ أُوحِيَ إِلَيۡكَ مِنَ ٱلۡكِتَٰبِ وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَۖ إِنَّ ٱلصَّلَوٰةَ تَنۡهَىٰ عَنِ ٱلۡفَحۡشَآءِ وَٱلۡمُنكَرِۗ وَلَذِكۡرُ ٱللَّهِ أَكۡبَرُۗ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ مَا تَصۡنَعُونَ

Ka karanta abin da ake yi maka wahayinsa na Alqur’ani, ka kuma tsai da salla; lalle salla tana hana alfasha da kuma abin qi. Kuma tabbas ambaton Allah shi ne mafi girma. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 52

قُلۡ كَفَىٰ بِٱللَّهِ بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡ شَهِيدٗاۖ يَعۡلَمُ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۗ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱلۡبَٰطِلِ وَكَفَرُواْ بِٱللَّهِ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Ka ce (da su): “Allah Ya isa shaida tsakanina da ku; Yana sane da abin da yake cikin sammai da qasa. Waxanda kuwa suka yi imani da qarya suka kuma kafirce wa Allah, waxannan su ne asararru.”



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 62

ٱللَّهُ يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦ وَيَقۡدِرُ لَهُۥٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Allah Yana shimfixa arziki ga wanda Ya ga dama daga bayinsa, Ya kuma quntata masa. Lalle Allah Masanin komai ne



Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 23

وَمَن كَفَرَ فَلَا يَحۡزُنكَ كُفۡرُهُۥٓۚ إِلَيۡنَا مَرۡجِعُهُمۡ فَنُنَبِّئُهُم بِمَا عَمِلُوٓاْۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Duk kuwa wanda ya kafirta, to kada kafircinsa ya vata maka rai. Zuwa gare Mu ne kawai makomarsu take, sai Mu ba su labarin abin da suka aikata. Lalle Allah Masanin abin da yake cikin qiraza ne



Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 34

إِنَّ ٱللَّهَ عِندَهُۥ عِلۡمُ ٱلسَّاعَةِ وَيُنَزِّلُ ٱلۡغَيۡثَ وَيَعۡلَمُ مَا فِي ٱلۡأَرۡحَامِۖ وَمَا تَدۡرِي نَفۡسٞ مَّاذَا تَكۡسِبُ غَدٗاۖ وَمَا تَدۡرِي نَفۡسُۢ بِأَيِّ أَرۡضٖ تَمُوتُۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمٌ خَبِيرُۢ

Lalle Allah a wurinsa ne (kaxai) sanin lokacin tashin alqiyama yake, kuma (Shi) Yake saukar da ruwa, (Shi) kuma Yake sane da abin da yake cikin mahaifa[1]; ba kuwa wani rai da yake sane da abin da zai aikata gobe, ba kuma wani rai da yake sane da qasar da zai mutu. Lalle Allah Shi ne Masani, Mai cikakken ilimi


1- Watau ya san komai na halittarsa, tun daga lokacin shigarsa mahaifa har zuwa makomarsa ta qarshe.


Capítulo: Suratus Sajda

Verso : 6

ذَٰلِكَ عَٰلِمُ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Wannan (Shi ne) Masanin voye da sarari, Mabuwayi, Mai rahama



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 40

مَّا كَانَ مُحَمَّدٌ أَبَآ أَحَدٖ مِّن رِّجَالِكُمۡ وَلَٰكِن رَّسُولَ ٱللَّهِ وَخَاتَمَ ٱلنَّبِيِّـۧنَۗ وَكَانَ ٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٗا

(Annabi) Muhammadu bai kasance uban xaya daga cikin mazajenku ba, sai dai (shi) ya kasance Manzon Allah ne kuma cikamakin annabawa. Allah kuma Ya kasance Masanin komai ne



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 54

إِن تُبۡدُواْ شَيۡـًٔا أَوۡ تُخۡفُوهُ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٗا

Idan kuma kuka bayyana wani abu ko kuka voye shi, to Allah Ya kasance Masanin komai ne



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 63

يَسۡـَٔلُكَ ٱلنَّاسُ عَنِ ٱلسَّاعَةِۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ ٱللَّهِۚ وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّ ٱلسَّاعَةَ تَكُونُ قَرِيبًا

Mutane suna tambayar ka game da (ranar) alqiyama; ka ce (da su): “Saninta a wajen Allah kawai yake.” Ba ka sani ba ko watakila alqiyamar za ta kasance kusa



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 2

يَعۡلَمُ مَا يَلِجُ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا يَخۡرُجُ مِنۡهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ وَمَا يَعۡرُجُ فِيهَاۚ وَهُوَ ٱلرَّحِيمُ ٱلۡغَفُورُ

Yana sane da abin da yake shiga cikin qasa da abin da yake fitowa daga cikinta, da kuma abin da yake sauka daga sama da abin da yake hawa cikinta. Kuma Shi Mai rahama ne, Mai gafara



Capítulo: Suratu Faxir

Verso : 8

أَفَمَن زُيِّنَ لَهُۥ سُوٓءُ عَمَلِهِۦ فَرَءَاهُ حَسَنٗاۖ فَإِنَّ ٱللَّهَ يُضِلُّ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۖ فَلَا تَذۡهَبۡ نَفۡسُكَ عَلَيۡهِمۡ حَسَرَٰتٍۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِمَا يَصۡنَعُونَ

Yanzu wanda aka qawata wa mummunan aikinsa ya gan shi kyakkyawa (zai yi daidai da wanda Allah Ya shiryar)? To lalle Allah Yana vatar da wanda Ya ga dama Ya shiryi wanda Ya ga dama; saboda haka kada ka halakar da kanka don baqin ciki game da su. Lalle Allah Masanin abin da suke aikatawa ne



Capítulo: Suratu Faxir

Verso : 11

وَٱللَّهُ خَلَقَكُم مِّن تُرَابٖ ثُمَّ مِن نُّطۡفَةٖ ثُمَّ جَعَلَكُمۡ أَزۡوَٰجٗاۚ وَمَا تَحۡمِلُ مِنۡ أُنثَىٰ وَلَا تَضَعُ إِلَّا بِعِلۡمِهِۦۚ وَمَا يُعَمَّرُ مِن مُّعَمَّرٖ وَلَا يُنقَصُ مِنۡ عُمُرِهِۦٓ إِلَّا فِي كِتَٰبٍۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ

Kuma Allah Ya halicce ku ne daga turvaya sannan daga maniyyi, sannan kuma Ya mayar da ku maza da mata. Kuma mace ba za ta xauki ciki ba, ba kuma za ta haifu ba sai da saninsa. Ba kuma wani mai tsawon rai da za a raya shi, ko kuma wani da za a rage tsawon ransa face yana (rubuce) a cikin Lauhul-Mahafuzu. Wannan kuwa a wurin Allah mai sauqi ne



Capítulo: Suratu Faxir

Verso : 38

إِنَّ ٱللَّهَ عَٰلِمُ غَيۡبِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ إِنَّهُۥ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Lalle Allah Masanin gaibin sammai da qasa ne. Lalle Shi Masanin abubuwan da suke cikin zukata ne



Capítulo: Suratu Yasin

Verso : 76

فَلَا يَحۡزُنكَ قَوۡلُهُمۡۘ إِنَّا نَعۡلَمُ مَا يُسِرُّونَ وَمَا يُعۡلِنُونَ

To kada maganarsu ta baqanta maka. Lalle Mu Muna sane da abin da suke voyewa da kuma abin da suke bayyanawa



Capítulo: Suratu Yasin

Verso : 79

قُلۡ يُحۡيِيهَا ٱلَّذِيٓ أَنشَأَهَآ أَوَّلَ مَرَّةٖۖ وَهُوَ بِكُلِّ خَلۡقٍ عَلِيمٌ

Ka ce: “Wannan da Ya fare su tun farko Shi ne zai raya su; Shi kuwa Masanin kowacce irin halitta ne



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 70

وَوُفِّيَتۡ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا عَمِلَتۡ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِمَا يَفۡعَلُونَ

Aka kuma yi wa kowane rai cikakken sakamakon abin da ya aikata, Shi ko (Allah) Yana sane da abin da suke aikatawa



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 7

ٱلَّذِينَ يَحۡمِلُونَ ٱلۡعَرۡشَ وَمَنۡ حَوۡلَهُۥ يُسَبِّحُونَ بِحَمۡدِ رَبِّهِمۡ وَيُؤۡمِنُونَ بِهِۦ وَيَسۡتَغۡفِرُونَ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْۖ رَبَّنَا وَسِعۡتَ كُلَّ شَيۡءٖ رَّحۡمَةٗ وَعِلۡمٗا فَٱغۡفِرۡ لِلَّذِينَ تَابُواْ وَٱتَّبَعُواْ سَبِيلَكَ وَقِهِمۡ عَذَابَ ٱلۡجَحِيمِ

Waxanda suke xauke da Al’arshi da waxanda suke kewaye da shi suna yin tasbihi da yabon Ubangijinsu, suna kuma yin imani da Shi, kuma suna nema wa waxanda suka yi imani gafara, (suna cewa): “Ya Ubangiijnmu, ka yalwaci kowane abu da rahama da ilimi, to Ka gafarta wa waxanda suka tuba suka kuma bi hanyarka, Ka kuma kiyaye su daga azabar (wutar) Jahimu