قَدۡ نَرَىٰ تَقَلُّبَ وَجۡهِكَ فِي ٱلسَّمَآءِۖ فَلَنُوَلِّيَنَّكَ قِبۡلَةٗ تَرۡضَىٰهَاۚ فَوَلِّ وَجۡهَكَ شَطۡرَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۚ وَحَيۡثُ مَا كُنتُمۡ فَوَلُّواْ وُجُوهَكُمۡ شَطۡرَهُۥۗ وَإِنَّ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ لَيَعۡلَمُونَ أَنَّهُ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّهِمۡۗ وَمَا ٱللَّهُ بِغَٰفِلٍ عَمَّا يَعۡمَلُونَ
Haqiqa Mun ga jujjuyawar fuskarka zuwa sama, to lalle za Mu fuskantar da kai zuwa ga alqibilar da za ka yarda da ita. Don haka ka juyar da fuskarka wajajen Masallaci mai alfarma; ku ma (Musulmi) a duk inda kuke to ku juyar da fuskokinku wajajensa. Lalle kuma waxanda aka ba su Littafi suna sane da cewa, lalle shi (wannan canji) gaskiya ne daga Ubangijinsu. Kuma Allah ba rafkananne ba ne game da abin da suke aikatawa
وَلَئِنۡ أَتَيۡتَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ بِكُلِّ ءَايَةٖ مَّا تَبِعُواْ قِبۡلَتَكَۚ وَمَآ أَنتَ بِتَابِعٖ قِبۡلَتَهُمۡۚ وَمَا بَعۡضُهُم بِتَابِعٖ قِبۡلَةَ بَعۡضٖۚ وَلَئِنِ ٱتَّبَعۡتَ أَهۡوَآءَهُم مِّنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَكَ مِنَ ٱلۡعِلۡمِ إِنَّكَ إِذٗا لَّمِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ
Lalle kuma da za ka kawo wa waxanda aka ba su Littafi kowace irin hujja ba za su bi alqibilarka ba; kuma kai ma ba mai bin alqibilarsu ba ne; kuma sashinsu bai zama mai bin alqibilar sashi ba. Kuma haqiqa idan har ka bi soye-soyen zukatansu bayan abin da ya zo maka na gaskiya, to lalle idan ka yi haka tabbas kana cikin azzalumai
وَمِنۡ حَيۡثُ خَرَجۡتَ فَوَلِّ وَجۡهَكَ شَطۡرَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۖ وَإِنَّهُۥ لَلۡحَقُّ مِن رَّبِّكَۗ وَمَا ٱللَّهُ بِغَٰفِلٍ عَمَّا تَعۡمَلُونَ
Ko ta ina ka fito, to ka juyar da fuskarka wajajen Masallaci mai alfarma; kuma lalle shi gaskiya ne daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama gafalalle game da abin da kuke aikatawa ba
وَمِنۡ حَيۡثُ خَرَجۡتَ فَوَلِّ وَجۡهَكَ شَطۡرَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۚ وَحَيۡثُ مَا كُنتُمۡ فَوَلُّواْ وُجُوهَكُمۡ شَطۡرَهُۥ لِئَلَّا يَكُونَ لِلنَّاسِ عَلَيۡكُمۡ حُجَّةٌ إِلَّا ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ مِنۡهُمۡ فَلَا تَخۡشَوۡهُمۡ وَٱخۡشَوۡنِي وَلِأُتِمَّ نِعۡمَتِي عَلَيۡكُمۡ وَلَعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ
Kuma duk inda ka fita, to ka juyar da fuskarka wajajen Masallaci mai alfarma. Ku ma duk inda kuke to ku juyar da fuskokinku wajajensa, don kada ya zama mutane suna da wata hujja a kanku, sai dai waxanda suka yi zalunci daga cikinsu, don haka kada ku ji tsoron su, ku ji tsorona, kuma domin in cika muku ni’imata, don ku shiriya
وَٱقۡتُلُوهُمۡ حَيۡثُ ثَقِفۡتُمُوهُمۡ وَأَخۡرِجُوهُم مِّنۡ حَيۡثُ أَخۡرَجُوكُمۡۚ وَٱلۡفِتۡنَةُ أَشَدُّ مِنَ ٱلۡقَتۡلِۚ وَلَا تُقَٰتِلُوهُمۡ عِندَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ حَتَّىٰ يُقَٰتِلُوكُمۡ فِيهِۖ فَإِن قَٰتَلُوكُمۡ فَٱقۡتُلُوهُمۡۗ كَذَٰلِكَ جَزَآءُ ٱلۡكَٰفِرِينَ
Kuma ku yaqe su duk inda kuka same su, kuma ku fitar da su ta inda suka fitar da ku; kuma fitina (ta kafirci) ita ce mafi tsanani fiye da kisa, kuma kada ku yaqe su a wurin Masallaci mai alfarma, har sai idan sun yaqe ku a cikinsa, idan har suka yaqe ku, to ku ma ku yaqe su. Kamar haka ne sakamakon kafirai yake
وَأَتِمُّواْ ٱلۡحَجَّ وَٱلۡعُمۡرَةَ لِلَّهِۚ فَإِنۡ أُحۡصِرۡتُمۡ فَمَا ٱسۡتَيۡسَرَ مِنَ ٱلۡهَدۡيِۖ وَلَا تَحۡلِقُواْ رُءُوسَكُمۡ حَتَّىٰ يَبۡلُغَ ٱلۡهَدۡيُ مَحِلَّهُۥۚ فَمَن كَانَ مِنكُم مَّرِيضًا أَوۡ بِهِۦٓ أَذٗى مِّن رَّأۡسِهِۦ فَفِدۡيَةٞ مِّن صِيَامٍ أَوۡ صَدَقَةٍ أَوۡ نُسُكٖۚ فَإِذَآ أَمِنتُمۡ فَمَن تَمَتَّعَ بِٱلۡعُمۡرَةِ إِلَى ٱلۡحَجِّ فَمَا ٱسۡتَيۡسَرَ مِنَ ٱلۡهَدۡيِۚ فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ ثَلَٰثَةِ أَيَّامٖ فِي ٱلۡحَجِّ وَسَبۡعَةٍ إِذَا رَجَعۡتُمۡۗ تِلۡكَ عَشَرَةٞ كَامِلَةٞۗ ذَٰلِكَ لِمَن لَّمۡ يَكُنۡ أَهۡلُهُۥ حَاضِرِي ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ
Kuma ku cika aikin Hajji da umara domin Allah. To idan an tsare ku, sai ku gabatar da abin da ya sawwaqa na hadaya, kuma kada ku aske kawunanku har sai hadaya ta kai wurin yankanta. To wanda ya kasance a cikinku mara lafiya ko akwai wata cuta a kansa, (idan yayi aski) to sai ya yi fidiya ta (hanyar) yin azumi ko sadaqa ko yanka[1]. Idan kuwa kun amintu, to duk wanda ya yi tamattu’i da yin umara tare da Hajji, to sai ya yanka abin da ya sawwaqa na hadaya; amma wanda bai samu ba, sai ya yi azumin kwana uku a lokacin aikin Hajji, da kuma na kwana bakwai idan kun dawo gida. Waxannan kwana goma ke nan cikakku. Wannan hukuncin yana ga wanda iyalinsa ba sa cikin hurumin Makka ne. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, ku sani cewa, lalle Allah Mai tsananin uquba ne
1- Watau ya yi azumi na kwana uku, ko ya ciyar da miskinai shida, kowanne ya ba shi rabin mudu ko ya yanka akuya.
يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلشَّهۡرِ ٱلۡحَرَامِ قِتَالٖ فِيهِۖ قُلۡ قِتَالٞ فِيهِ كَبِيرٞۚ وَصَدٌّ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ وَكُفۡرُۢ بِهِۦ وَٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ وَإِخۡرَاجُ أَهۡلِهِۦ مِنۡهُ أَكۡبَرُ عِندَ ٱللَّهِۚ وَٱلۡفِتۡنَةُ أَكۡبَرُ مِنَ ٱلۡقَتۡلِۗ وَلَا يَزَالُونَ يُقَٰتِلُونَكُمۡ حَتَّىٰ يَرُدُّوكُمۡ عَن دِينِكُمۡ إِنِ ٱسۡتَطَٰعُواْۚ وَمَن يَرۡتَدِدۡ مِنكُمۡ عَن دِينِهِۦ فَيَمُتۡ وَهُوَ كَافِرٞ فَأُوْلَـٰٓئِكَ حَبِطَتۡ أَعۡمَٰلُهُمۡ فِي ٱلدُّنۡيَا وَٱلۡأٓخِرَةِۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ
Suna tambayar ka game da wata mai alfarma, yin yaqi a cikinsa. Ka ce: “Yaqi a cikinsa, babban laifi ne, amma hana (mutane) bin tafarkin Allah da kafirce masa da kuma (hana mutane shiga) Masallaci mai alfarma da fitar da mutanensa daga gare shi, su ne mafi girman laifi a wajen Allah. Kuma (laifin) fitina ya fi na kisa girma.”[1] Kuma (kafirai) ba za su gushe ba suna yaqar ku, har sai sun raba ku da addininku, idan da za su sami dama. Kuma duk wanda ya yi ridda daga cikinku, ya bar addininsa, kuma ya mutu yana kafiri, to waxannan ayyukansu sun lalace a duniya da lahira, kuma waxannan su ne ma’abota wuta, suna masu dawwama a cikinta
1- Wannan ayar ta sauka ne bayan da wata runduna ta Musulmi suka kashe wani kafiri mai suna Ibnul Hadhrami a watan Rajab ba su sani ba. Sai kafirai suka riqa aibata su da haka, sai Allah ya saukar da wannan ayar.
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تُحِلُّواْ شَعَـٰٓئِرَ ٱللَّهِ وَلَا ٱلشَّهۡرَ ٱلۡحَرَامَ وَلَا ٱلۡهَدۡيَ وَلَا ٱلۡقَلَـٰٓئِدَ وَلَآ ءَآمِّينَ ٱلۡبَيۡتَ ٱلۡحَرَامَ يَبۡتَغُونَ فَضۡلٗا مِّن رَّبِّهِمۡ وَرِضۡوَٰنٗاۚ وَإِذَا حَلَلۡتُمۡ فَٱصۡطَادُواْۚ وَلَا يَجۡرِمَنَّكُمۡ شَنَـَٔانُ قَوۡمٍ أَن صَدُّوكُمۡ عَنِ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ أَن تَعۡتَدُواْۘ وَتَعَاوَنُواْ عَلَى ٱلۡبِرِّ وَٱلتَّقۡوَىٰۖ وَلَا تَعَاوَنُواْ عَلَى ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡعُدۡوَٰنِۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ
Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku halatta keta alfarmar alamomin addinin Allah, ko (ku wulaqanta) Wata mai alfarma[1] ko dabbobin hadaya ko dabbobin hadaya masu alama da (tare) masu nufin ziyarar Xaki mai alfarma, suna neman falala daga wurin Ubangijinsu da yardarsa. Idan kuwa kuka kwance Harami, to ku yi farauta (idan kuna so). Kuma kada qiyayyar wasu mutane da suka hana ku isa masallaci mai alfarma, ta sa ku yi ta’addanci. Kuma ku taimaki juna a kan aikin alheri da taqawa; kada kuma ku taimaka wa juna a kan ayyukan savo da ta’addanci. Kuma ku kiyaye dokokin Allah; lalle Allah Mai tsananin uquba ne
1- Watanni masu alfarma su ne: Zulqi’ida, Zulhijja, Al-Muharram da Rajab. An haramta yaqi a cikinsu.
وَمَا لَهُمۡ أَلَّا يُعَذِّبَهُمُ ٱللَّهُ وَهُمۡ يَصُدُّونَ عَنِ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ وَمَا كَانُوٓاْ أَوۡلِيَآءَهُۥٓۚ إِنۡ أَوۡلِيَآؤُهُۥٓ إِلَّا ٱلۡمُتَّقُونَ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ
Me zai hana Allah Ya yi musu azaba alhali su suna hana mutane zuwa Masallaci mai alfarma, alhali kuwa ba su zamanto masu qaunar Sa na haqiqa ba. Masu qaunar Sa na haqiqa su ne masu taqawa, sai dai yawancinsu ba sa sanin (haka)
وَمَا كَانَ صَلَاتُهُمۡ عِندَ ٱلۡبَيۡتِ إِلَّا مُكَآءٗ وَتَصۡدِيَةٗۚ فَذُوقُواْ ٱلۡعَذَابَ بِمَا كُنتُمۡ تَكۡفُرُونَ
Kuma sallarsu a Xakin (Ka’aba) ba ta zamanto ba sai fito da tafi. Sai ku xanxani azaba saboda abin da kuka zamanto kuna yi na kafirci
كَيۡفَ يَكُونُ لِلۡمُشۡرِكِينَ عَهۡدٌ عِندَ ٱللَّهِ وَعِندَ رَسُولِهِۦٓ إِلَّا ٱلَّذِينَ عَٰهَدتُّمۡ عِندَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۖ فَمَا ٱسۡتَقَٰمُواْ لَكُمۡ فَٱسۡتَقِيمُواْ لَهُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُتَّقِينَ
Ta yaya zai yiwu a samu wani alqawari tsakanin Allah da Manzonsa da kuma mushirikai in ban da waxanda kuka yi alqawari da su a Masallaci mai alfarma? To matuqar sun tsaya muku (bisa gaskiya) sai ku ma ku tsaya musu. Lalle Allah Yana son masu taqawa
۞أَجَعَلۡتُمۡ سِقَايَةَ ٱلۡحَآجِّ وَعِمَارَةَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ كَمَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَجَٰهَدَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۚ لَا يَسۡتَوُۥنَ عِندَ ٱللَّهِۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ
Yanzu kwa mayar da shayar da alhazai da raya Masallaci mai alfarma kamar wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira ya kuma yi jihadi saboda Allah? Ai ba za su zama xaya ba a wurin Allah. Allah kuma ba Ya shiryar da mutane azzalumai
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِنَّمَا ٱلۡمُشۡرِكُونَ نَجَسٞ فَلَا يَقۡرَبُواْ ٱلۡمَسۡجِدَ ٱلۡحَرَامَ بَعۡدَ عَامِهِمۡ هَٰذَاۚ وَإِنۡ خِفۡتُمۡ عَيۡلَةٗ فَسَوۡفَ يُغۡنِيكُمُ ٱللَّهُ مِن فَضۡلِهِۦٓ إِن شَآءَۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمٌ حَكِيمٞ
Ya ku waxanda suka yi imani, lalle mushrikai najasa ne kawai, saboda haka kada su kusanci Masallaci mai alfarma bayan wannan shekarar tasu. Idan kuma kuna tsoron talauci ne to Allah zai wadata ku daga falalarsa idan Ya ga dama. Lalle Allah Masani ne, Mai hikima
إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَيَصُدُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ وَٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ ٱلَّذِي جَعَلۡنَٰهُ لِلنَّاسِ سَوَآءً ٱلۡعَٰكِفُ فِيهِ وَٱلۡبَادِۚ وَمَن يُرِدۡ فِيهِ بِإِلۡحَادِۭ بِظُلۡمٖ نُّذِقۡهُ مِنۡ عَذَابٍ أَلِيمٖ
Lalle waxanda suka kafirta suke kuma toshe hanyar Allah da kuma Masallacin Harami wanda Muka sanya shi bai-xaya ga mutane, mazaunin cikinsa da kuma mai zuwa (daga waje). Wanda kuwa ya nufe shi da wata fanxara da zalunci to za Mu xanxana masa azaba mai raxaxi[1]
1- Watau qudurce niyyar aikata laifi a cikin hurumin Makka kawai ya isa ya jawo wa mutum azabar Allah ko da kuwa bai aikata ba.
هُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَصَدُّوكُمۡ عَنِ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ وَٱلۡهَدۡيَ مَعۡكُوفًا أَن يَبۡلُغَ مَحِلَّهُۥۚ وَلَوۡلَا رِجَالٞ مُّؤۡمِنُونَ وَنِسَآءٞ مُّؤۡمِنَٰتٞ لَّمۡ تَعۡلَمُوهُمۡ أَن تَطَـُٔوهُمۡ فَتُصِيبَكُم مِّنۡهُم مَّعَرَّةُۢ بِغَيۡرِ عِلۡمٖۖ لِّيُدۡخِلَ ٱللَّهُ فِي رَحۡمَتِهِۦ مَن يَشَآءُۚ لَوۡ تَزَيَّلُواْ لَعَذَّبۡنَا ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡهُمۡ عَذَابًا أَلِيمًا
Su ne waxanda suka kafirta suka kuma hana ku isa ga Masallaci mai alfarma, suka kuma hana dabbobin hadaya isa wurin yankansu. Kuma ba don wasu mazaje muminai da wasu mataye muminai da ba ku san su ba, don kada ku kashe su, sannan wani laifi nasu ya same ku ba tare da sani ba, (da Ya ba ku damar yaqar su. Wannan ya faru ne) don Allah Ya shigar da wanda Ya ga dama cikin rahamarsa. Da sun ware to lalle da Mun azabtar da waxanda suka kafirta daga cikinsu azaba mai tsanani
لَّقَدۡ صَدَقَ ٱللَّهُ رَسُولَهُ ٱلرُّءۡيَا بِٱلۡحَقِّۖ لَتَدۡخُلُنَّ ٱلۡمَسۡجِدَ ٱلۡحَرَامَ إِن شَآءَ ٱللَّهُ ءَامِنِينَ مُحَلِّقِينَ رُءُوسَكُمۡ وَمُقَصِّرِينَ لَا تَخَافُونَۖ فَعَلِمَ مَا لَمۡ تَعۡلَمُواْ فَجَعَلَ مِن دُونِ ذَٰلِكَ فَتۡحٗا قَرِيبًا
Haqiqa Allah Ya tabbatar wa Manzonsa gaskiyar mafarkin cewa, lalle za ku shiga Masallaci mai alfarma insha Allahu, kuna cikin aminci kuna masu aske kawunanku da masu yin saisaye, ba tare da kuna jin tsoron (komai) ba, to Ya san abin da ba ku sani ba, sai Ya sanya buxi na kusa[1] kafin wannan
1- Watau sulhul Hudaibiyya da buxe Khaibar.