Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 33

۞إِنَّ ٱللَّهَ ٱصۡطَفَىٰٓ ءَادَمَ وَنُوحٗا وَءَالَ إِبۡرَٰهِيمَ وَءَالَ عِمۡرَٰنَ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Lalle Allah Ya zavi Adamu, da Nuhu da iyalan gidan Ibrahimu da iyalan gidan Imrana Ya fifita su a kan sauran talikai



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 163

۞إِنَّآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ كَمَآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ نُوحٖ وَٱلنَّبِيِّـۧنَ مِنۢ بَعۡدِهِۦۚ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ وَٱلۡأَسۡبَاطِ وَعِيسَىٰ وَأَيُّوبَ وَيُونُسَ وَهَٰرُونَ وَسُلَيۡمَٰنَۚ وَءَاتَيۡنَا دَاوُۥدَ زَبُورٗا

Lalle Mun yi maka wahayi irin wahayin da Muka yi wa Nuhu da kuma annabawan da suka biyo bayansa, kuma Mun yi wahayi ga Ibrahimu da Isma’ila da Ishaqa da Ya’aqubu da kuma jikokin (Ya’aqubu) da Isa da Ayyuba da Yunusa da Haruna da Sulaimanu; kuma Muka bai wa Dawuda littafin Zabura



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 84

وَوَهَبۡنَا لَهُۥٓ إِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَۚ كُلًّا هَدَيۡنَاۚ وَنُوحًا هَدَيۡنَا مِن قَبۡلُۖ وَمِن ذُرِّيَّتِهِۦ دَاوُۥدَ وَسُلَيۡمَٰنَ وَأَيُّوبَ وَيُوسُفَ وَمُوسَىٰ وَهَٰرُونَۚ وَكَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kuma Muka ba shi Ishaqa da Ya’aqubu. Kowanne daga cikinsu Mun shiryar da shi, kuma Mun shiryar da Nuhu tun gabaninsu. Kuma daga cikin zurriyarsa akwai Dawudu da Sulaimanu da Ayyuba da Yusufu da Musa da Haruna. Kuma kamar haka ne Muke saka wa masu kyautata (ayyukansu)



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 59

لَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوۡمِهِۦ فَقَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥٓ إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

Lalle haqiqa Mun aiko Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya ce: “Ya ku mutanena, ku bautata wa Allah, ba ku da wani abin bautawa da gaskiya sai Shi, lalle ni ina ji muku tsoron azabar wani yini mai girma.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 60

قَالَ ٱلۡمَلَأُ مِن قَوۡمِهِۦٓ إِنَّا لَنَرَىٰكَ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Sai manyan gari cikin mutanensa suka ce: “Lalle mu tabbas muna ganin kana cikin vata mabayyani.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 61

قَالَ يَٰقَوۡمِ لَيۡسَ بِي ضَلَٰلَةٞ وَلَٰكِنِّي رَسُولٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Sai ya ce: “Ya ku mutanena, babu wata vata tare da ni, sai dai ni Manzo ne daga Ubangijin halittu.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 62

أُبَلِّغُكُمۡ رِسَٰلَٰتِ رَبِّي وَأَنصَحُ لَكُمۡ وَأَعۡلَمُ مِنَ ٱللَّهِ مَا لَا تَعۡلَمُونَ

“Ina isar muku da saqonnin Ubangijina, ina kuma yi muku nasiha, na kuma san abin da ba ku sani ba daga Allah



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 63

أَوَعَجِبۡتُمۡ أَن جَآءَكُمۡ ذِكۡرٞ مِّن رَّبِّكُمۡ عَلَىٰ رَجُلٖ مِّنكُمۡ لِيُنذِرَكُمۡ وَلِتَتَّقُواْ وَلَعَلَّكُمۡ تُرۡحَمُونَ

“Shin kun yi mamaki ne don wa’azi ya zo muku daga Ubangijinku, ta kan harshen wani mutum cikinku, don ya gargaxe ku, don ku kuma kiyaye dokokin Allah domin a ji qan ku?”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 64

فَكَذَّبُوهُ فَأَنجَيۡنَٰهُ وَٱلَّذِينَ مَعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ وَأَغۡرَقۡنَا ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَآۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمًا عَمِينَ

Sai suka qaryata shi, sai Muka tserar da shi da waxanda suke tare da shi, a cikin jirgin ruwa, kuma Muka dulmiyar da waxanda suka qaryata ayoyinmu. Lalle su sun kasance mutane makafi



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 71

۞وَٱتۡلُ عَلَيۡهِمۡ نَبَأَ نُوحٍ إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦ يَٰقَوۡمِ إِن كَانَ كَبُرَ عَلَيۡكُم مَّقَامِي وَتَذۡكِيرِي بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ فَعَلَى ٱللَّهِ تَوَكَّلۡتُ فَأَجۡمِعُوٓاْ أَمۡرَكُمۡ وَشُرَكَآءَكُمۡ ثُمَّ لَا يَكُنۡ أَمۡرُكُمۡ عَلَيۡكُمۡ غُمَّةٗ ثُمَّ ٱقۡضُوٓاْ إِلَيَّ وَلَا تُنظِرُونِ

Ka kuma karanta musu labarin (Annabi) Nuhu, a lokacin da ya ce da mutanensa: “Ya ku mutanena, idan zamana a cikinku da kuma wa’azin da nake muku da ayoyin Allah sun dame ku, to ni fa ga Allah ne kawai na dogara, sai ku tattara al’amarinku ku kuma (ku kira) abokan tarayyarku, sannan kada al’amarin naku ya zama a voye, sannan ku zartar (da shi) a gare ni, kada kuma ku saurara mini



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 72

فَإِن تَوَلَّيۡتُمۡ فَمَا سَأَلۡتُكُم مِّنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَى ٱللَّهِۖ وَأُمِرۡتُ أَنۡ أَكُونَ مِنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ

“To idan kuka ba da baya, to ban tambaye ku wani lada ba; ladana yana ga Allah; an kuwa umarce ni da in kasance cikin Musulmai.”



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 73

فَكَذَّبُوهُ فَنَجَّيۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ وَجَعَلۡنَٰهُمۡ خَلَـٰٓئِفَ وَأَغۡرَقۡنَا ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَاۖ فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُنذَرِينَ

Sai suka qaryata shi, sai Muka tserar da shi da waxanda suke tare da shi a cikin jirgin ruwa, Muka kuma mayar da su masu maye gurbin (waxanda suka gabace su), Muka kuma nutsar da waxanda suka qaryata ayoyinmu. To duba ka ga yadda qarshen waxanda aka yi wa gargaxi ya kasance



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 25

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوۡمِهِۦٓ إِنِّي لَكُمۡ نَذِيرٞ مُّبِينٌ

Haqiqa kuma Mun aiko Nuhu zuwa ga mutanensa (ya ce da su): “Lalle ni mai gargaxi bayyananne ne a gare ku



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 26

أَن لَّا تَعۡبُدُوٓاْ إِلَّا ٱللَّهَۖ إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٍ أَلِيمٖ

“Cewa kada ku bauta wa (kowa) sai Allah. Lalle ni ina jiye muku tsoron azabar wata rana mai raxaxi.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 27

فَقَالَ ٱلۡمَلَأُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن قَوۡمِهِۦ مَا نَرَىٰكَ إِلَّا بَشَرٗا مِّثۡلَنَا وَمَا نَرَىٰكَ ٱتَّبَعَكَ إِلَّا ٱلَّذِينَ هُمۡ أَرَاذِلُنَا بَادِيَ ٱلرَّأۡيِ وَمَا نَرَىٰ لَكُمۡ عَلَيۡنَا مِن فَضۡلِۭ بَلۡ نَظُنُّكُمۡ كَٰذِبِينَ

Sai manya-manya daga cikin mutanensa, waxanda suka kafirta suka ce (da shi): “Mu fa mun xauke ka kawai mutum ne kamarmu, kuma ba ma ganin wani ya bi ka in ban da wulakantattun cikinmu gidadawa. Kuma ba ma ganin ku da wani fifiko a kanmu; kai muna ma tsammanin ku maqaryata ne.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 28

قَالَ يَٰقَوۡمِ أَرَءَيۡتُمۡ إِن كُنتُ عَلَىٰ بَيِّنَةٖ مِّن رَّبِّي وَءَاتَىٰنِي رَحۡمَةٗ مِّنۡ عِندِهِۦ فَعُمِّيَتۡ عَلَيۡكُمۡ أَنُلۡزِمُكُمُوهَا وَأَنتُمۡ لَهَا كَٰرِهُونَ

(Annabi Nuhu) ya ce: “Ya ku mutanena, ku ba ni labari, yanzu idan na zamanto ina riqe da hujja daga Ubangijina, Ya kuma ba ni wata rahama daga gare Shi, sai aka voye muku ita, yanzu ma tilasta muku ita, alhali kuwa kuna qin ta?



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 29

وَيَٰقَوۡمِ لَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مَالًاۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَى ٱللَّهِۚ وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْۚ إِنَّهُم مُّلَٰقُواْ رَبِّهِمۡ وَلَٰكِنِّيٓ أَرَىٰكُمۡ قَوۡمٗا تَجۡهَلُونَ

“Kuma ya ku mutanena, ba na tambayar ku wata dukiya a kansa (kiran); ladana a wurin Allah kawai yake. Ni kuwa ba zan kori waxanda suka yi imani ba. Lalle su masu saduwa ne da Ubangijinsu, sai dai ni ina ganin ku mutane ne da kuke jahiltar (gaskiya).”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 30

وَيَٰقَوۡمِ مَن يَنصُرُنِي مِنَ ٱللَّهِ إِن طَرَدتُّهُمۡۚ أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

“Ya ku mutanena, wa zai kare ni daga Allah idan na kore su? Me ya sa ne ba kwa wa’azantuwa?



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 31

وَلَآ أَقُولُ لَكُمۡ عِندِي خَزَآئِنُ ٱللَّهِ وَلَآ أَعۡلَمُ ٱلۡغَيۡبَ وَلَآ أَقُولُ إِنِّي مَلَكٞ وَلَآ أَقُولُ لِلَّذِينَ تَزۡدَرِيٓ أَعۡيُنُكُمۡ لَن يُؤۡتِيَهُمُ ٱللَّهُ خَيۡرًاۖ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا فِيٓ أَنفُسِهِمۡ إِنِّيٓ إِذٗا لَّمِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

“Ba kuma zan ce da ku ina da taskokin Allah ba, ban kuma san gaibu ba, kuma ba zan ce lalle ni mala’ika ne ba, ba kuma zan ce wa waxanda idanuwanku suke wulaqantawa, Allah ba zai ba su wani alheri ba. Allah ne Ya fi sanin abin da yake zukatansu. Idan na yi haka, to lalle na zamanto daga cikin azzalumai.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 32

قَالُواْ يَٰنُوحُ قَدۡ جَٰدَلۡتَنَا فَأَكۡثَرۡتَ جِدَٰلَنَا فَأۡتِنَا بِمَا تَعِدُنَآ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

Suka ce: “Ya Nuhu, haqiqa ka ja da mu, ka kuma yawaita jayayya da mu; to sai ka zo mana da abin da kake yi mana alqawari da shi (na narko) in ka zamo daga masu gaskiya.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 33

قَالَ إِنَّمَا يَأۡتِيكُم بِهِ ٱللَّهُ إِن شَآءَ وَمَآ أَنتُم بِمُعۡجِزِينَ

Ya ce: “Ai Allah ne zai zo muku da shi idan Ya ga dama, ku kuma ba za ku gagara ba



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 34

وَلَا يَنفَعُكُمۡ نُصۡحِيٓ إِنۡ أَرَدتُّ أَنۡ أَنصَحَ لَكُمۡ إِن كَانَ ٱللَّهُ يُرِيدُ أَن يُغۡوِيَكُمۡۚ هُوَ رَبُّكُمۡ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

“Nasihata kuma ba za ta amfane ku ba - ko da na yi nufin yi muku nasihar - idan har da ma can Allah Yana nufin Ya vatar da ku. Shi ne Ubangijinku, kuma wurinsa za ku koma.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 35

أَمۡ يَقُولُونَ ٱفۡتَرَىٰهُۖ قُلۡ إِنِ ٱفۡتَرَيۡتُهُۥ فَعَلَيَّ إِجۡرَامِي وَأَنَا۠ بَرِيٓءٞ مِّمَّا تُجۡرِمُونَ

A’a, ko dai cewa suke: “Qagar sa ya yi?” (wato Alqur’ani) Ka ce: “Idan qagar sa na yi, to alhakin qagena yana kaina ne, ni kuma ba ruwana da laifin abin da kuke tabkawa.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 36

وَأُوحِيَ إِلَىٰ نُوحٍ أَنَّهُۥ لَن يُؤۡمِنَ مِن قَوۡمِكَ إِلَّا مَن قَدۡ ءَامَنَ فَلَا تَبۡتَئِسۡ بِمَا كَانُواْ يَفۡعَلُونَ

Aka kuma yi wa Nuhu wahayi cewa: “Ba wanda zai yi imani daga mutanenka sai waxanda suka riga suka yi. To kada ka yi baqin ciki game da abin da suke aikatawa



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 37

وَٱصۡنَعِ ٱلۡفُلۡكَ بِأَعۡيُنِنَا وَوَحۡيِنَا وَلَا تُخَٰطِبۡنِي فِي ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ إِنَّهُم مُّغۡرَقُونَ

“Ka kuma sassaqa jirgin ruwa a kan idanunmu da koyarwarmu. Kada kuma ka yi Mini maganar komai game da kafirai. Lalle su nutsar da su za a yi.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 38

وَيَصۡنَعُ ٱلۡفُلۡكَ وَكُلَّمَا مَرَّ عَلَيۡهِ مَلَأٞ مِّن قَوۡمِهِۦ سَخِرُواْ مِنۡهُۚ قَالَ إِن تَسۡخَرُواْ مِنَّا فَإِنَّا نَسۡخَرُ مِنكُمۡ كَمَا تَسۡخَرُونَ

Ya kuma riqa sassaqa jirgin, duk sanda kuma wasu manya daga mutanensa suka wuce ta wajensa sai su riqa yi masa ba’a. Ya ce: “Idan kun yi mana ba’a, to lalle mu ma fa (wata rana) za mu yi muku ba’ar kamar yadda kuke mana (yanzu)



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 39

فَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَ مَن يَأۡتِيهِ عَذَابٞ يُخۡزِيهِ وَيَحِلُّ عَلَيۡهِ عَذَابٞ مُّقِيمٌ

“To ba da daxewa ba za ku san wanda azaba mai kunyatarwa za ta zo masa, kuma wata azaba madawwamiya ta sauka a kansa.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 40

حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَ أَمۡرُنَا وَفَارَ ٱلتَّنُّورُ قُلۡنَا ٱحۡمِلۡ فِيهَا مِن كُلّٖ زَوۡجَيۡنِ ٱثۡنَيۡنِ وَأَهۡلَكَ إِلَّا مَن سَبَقَ عَلَيۡهِ ٱلۡقَوۡلُ وَمَنۡ ءَامَنَۚ وَمَآ ءَامَنَ مَعَهُۥٓ إِلَّا قَلِيلٞ

Har dai zuwa lokacin da umarninmu ya zo, kuma tanderu ya vuvvugo da ruwa, Muka ce: “Ka xauki ma’aurata bibbiyu daga kowace (halitta) a cikinsa (jirgin) haxe da iyalanka in ban da wanda maganar (halakar da shi) ta gabata a kansa, kuma (ka xauki) waxanda suka yi imani.” Ba kuwa waxanda suka yi imani da shi sai ‘yan tsirari



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 41

۞وَقَالَ ٱرۡكَبُواْ فِيهَا بِسۡمِ ٱللَّهِ مَجۡرٜىٰهَا وَمُرۡسَىٰهَآۚ إِنَّ رَبِّي لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ya kuma ce: “Ku shiga cikinsa, da sunan Allah ne tafiyarsa da kuma tsayawarsa. Lalle Ubangijina Mai gafara ne, Mai rahama.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 42

وَهِيَ تَجۡرِي بِهِمۡ فِي مَوۡجٖ كَٱلۡجِبَالِ وَنَادَىٰ نُوحٌ ٱبۡنَهُۥ وَكَانَ فِي مَعۡزِلٖ يَٰبُنَيَّ ٱرۡكَب مَّعَنَا وَلَا تَكُن مَّعَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Shi kuma (jirgin) yana tafiya da su cikin raquman ruwa kamar duwatsu, Nuhu kuwa sai ya kirawo xansa alhalin ya kasance a ware waje xaya (ya ce): “Kai xana, ka hawo mana tare da mu, kada ka zama tare da kafirai.”