Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 185

شَهۡرُ رَمَضَانَ ٱلَّذِيٓ أُنزِلَ فِيهِ ٱلۡقُرۡءَانُ هُدٗى لِّلنَّاسِ وَبَيِّنَٰتٖ مِّنَ ٱلۡهُدَىٰ وَٱلۡفُرۡقَانِۚ فَمَن شَهِدَ مِنكُمُ ٱلشَّهۡرَ فَلۡيَصُمۡهُۖ وَمَن كَانَ مَرِيضًا أَوۡ عَلَىٰ سَفَرٖ فَعِدَّةٞ مِّنۡ أَيَّامٍ أُخَرَۗ يُرِيدُ ٱللَّهُ بِكُمُ ٱلۡيُسۡرَ وَلَا يُرِيدُ بِكُمُ ٱلۡعُسۡرَ وَلِتُكۡمِلُواْ ٱلۡعِدَّةَ وَلِتُكَبِّرُواْ ٱللَّهَ عَلَىٰ مَا هَدَىٰكُمۡ وَلَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Watan Ramadan shi ne wanda aka saukar da Alqur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane kuma ayoyi ne bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa (tsakanin qarya da gaskiya). Don haka duk wanda ya halarci wannan watan daga cikinku, to ya azumce shi, kuma wanda ya kasance marar lafiya ko a kan wata tafiya, to (idan ya sha azumi) sai ya rama a waxansu kwanakin na daban. Allah Yana nufin sauqi a gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani a gare ku, don ku cika adadin (kwanakin Ramadan), kuma domin ku girmama Allah bisa ga shiryar da ku da Ya yi, don ku yi godiya