Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 83

وَإِذۡ أَخَذۡنَا مِيثَٰقَ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ لَا تَعۡبُدُونَ إِلَّا ٱللَّهَ وَبِٱلۡوَٰلِدَيۡنِ إِحۡسَانٗا وَذِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَقُولُواْ لِلنَّاسِ حُسۡنٗا وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ ثُمَّ تَوَلَّيۡتُمۡ إِلَّا قَلِيلٗا مِّنكُمۡ وَأَنتُم مُّعۡرِضُونَ

Kuma ka tuna lokacin da Muka xauki alqwari daga Banu Isra’ila cewa, ba za ku bauta wa kowa ba sai Allah, kuma za ku kyautata wa iyaye da makusanta da marayu da miskinai, kuma ku riqa yi wa mutane kyakkyawar magana, kuma ku tsai da salla, kuma ku ba da zakka, sannan sai kuka ba da baya sai ‘yan kaxan daga cikinku, alhalin kuna masu bijirewa



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 177

۞لَّيۡسَ ٱلۡبِرَّ أَن تُوَلُّواْ وُجُوهَكُمۡ قِبَلَ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ وَلَٰكِنَّ ٱلۡبِرَّ مَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ وَٱلۡكِتَٰبِ وَٱلنَّبِيِّـۧنَ وَءَاتَى ٱلۡمَالَ عَلَىٰ حُبِّهِۦ ذَوِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينَ وَٱبۡنَ ٱلسَّبِيلِ وَٱلسَّآئِلِينَ وَفِي ٱلرِّقَابِ وَأَقَامَ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتَى ٱلزَّكَوٰةَ وَٱلۡمُوفُونَ بِعَهۡدِهِمۡ إِذَا عَٰهَدُواْۖ وَٱلصَّـٰبِرِينَ فِي ٱلۡبَأۡسَآءِ وَٱلضَّرَّآءِ وَحِينَ ٱلۡبَأۡسِۗ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ صَدَقُواْۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُتَّقُونَ

Ba wai aikin xa’a shi ne ku juyar da fuskokinku mahudar rana ko mafaxarta ba ; sai dai aikin xa’a shi ne, wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira da mala’iku da littattafai da annabawa, kuma ya bayar da dukiyarsa, alhalin yana son ta, ga dangi na kusa da marayu da mabuqata da matafiyi da kuma masu roqo (bisa larura) da ‘yantar da bayi, sannan kuma ya tsayar da salla, kuma ya bayar da zakka, da kuma masu cika alqawarinsu idan suka qulla alqawari ; da masu haquri a cikin halin talauci da halin rashin lafiya da lokacin yaqi. Waxannan su ne waxanda suka yi gaskiya, kuma waxannan su ne masu taqawa



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 180

كُتِبَ عَلَيۡكُمۡ إِذَا حَضَرَ أَحَدَكُمُ ٱلۡمَوۡتُ إِن تَرَكَ خَيۡرًا ٱلۡوَصِيَّةُ لِلۡوَٰلِدَيۡنِ وَٱلۡأَقۡرَبِينَ بِٱلۡمَعۡرُوفِۖ حَقًّا عَلَى ٱلۡمُتَّقِينَ

An wajabta muku, idan alamun mutuwa suka zo wa xayanku, idan har ya bar wani alheri (dukiya), to ya yi wasiyya ga mahaifa biyu da dangi mafiya kusanci, ta hanyar da ta dace (a shari’a). Haqqi ne tabbatacce a kan masu taqawa[1]


1- Wasu malamai suna ganin cewa, ayar rabon gado ta Suratun Nisa’i aya ta 11 ta shafe hukuncin wannan ayar. Wasu kuma suna ganin hukuncinta dangane da wasiyya ga makusanta da ba za su ci gado ba yana nan, amma da sharaxin kada wasiyyar ta wuce sulusin abin da ya bari na dukiya.


Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 181

فَمَنۢ بَدَّلَهُۥ بَعۡدَ مَا سَمِعَهُۥ فَإِنَّمَآ إِثۡمُهُۥ عَلَى ٱلَّذِينَ يُبَدِّلُونَهُۥٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٞ

To wanda ya canza shi (lamarin wasiyya) bayan ya ji shi, to lalle laifinsa yana kan waxanda suka canza shi ne kawai. Lalle Allah Mai ji ne, Masani



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 182

فَمَنۡ خَافَ مِن مُّوصٖ جَنَفًا أَوۡ إِثۡمٗا فَأَصۡلَحَ بَيۡنَهُمۡ فَلَآ إِثۡمَ عَلَيۡهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

To duk wanda ya ji tsoron kaucewa bisa kuskure ko bisa zalunci daga mai yin wasiyya sai ya sasanta tsakaninsu (mai wasiyyar da waxanda aka yi wa wasiyyar); to wannan babu laifi a kansa; lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 215

يَسۡـَٔلُونَكَ مَاذَا يُنفِقُونَۖ قُلۡ مَآ أَنفَقۡتُم مِّنۡ خَيۡرٖ فَلِلۡوَٰلِدَيۡنِ وَٱلۡأَقۡرَبِينَ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَٱبۡنِ ٱلسَّبِيلِۗ وَمَا تَفۡعَلُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٞ

Suna tambayar ka, me za su ciyar ne? Ka ce: “Duk abin da za ku ciyar na alheri, to ga mahaifa da dangi mafiya kusanci da marayu da miskinai da matafiyi. Kuma duk abin da kuka aikata na alheri, to lalle Allah Masani ne da shi.”



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 233

۞وَٱلۡوَٰلِدَٰتُ يُرۡضِعۡنَ أَوۡلَٰدَهُنَّ حَوۡلَيۡنِ كَامِلَيۡنِۖ لِمَنۡ أَرَادَ أَن يُتِمَّ ٱلرَّضَاعَةَۚ وَعَلَى ٱلۡمَوۡلُودِ لَهُۥ رِزۡقُهُنَّ وَكِسۡوَتُهُنَّ بِٱلۡمَعۡرُوفِۚ لَا تُكَلَّفُ نَفۡسٌ إِلَّا وُسۡعَهَاۚ لَا تُضَآرَّ وَٰلِدَةُۢ بِوَلَدِهَا وَلَا مَوۡلُودٞ لَّهُۥ بِوَلَدِهِۦۚ وَعَلَى ٱلۡوَارِثِ مِثۡلُ ذَٰلِكَۗ فَإِنۡ أَرَادَا فِصَالًا عَن تَرَاضٖ مِّنۡهُمَا وَتَشَاوُرٖ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡهِمَاۗ وَإِنۡ أَرَدتُّمۡ أَن تَسۡتَرۡضِعُوٓاْ أَوۡلَٰدَكُمۡ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ إِذَا سَلَّمۡتُم مَّآ ءَاتَيۡتُم بِٱلۡمَعۡرُوفِۗ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

Kuma iyaye mata za su shayar da ‘ya’yansu tsawon shekara biyu cikakku, ga wanda ya yi nufin ya cika wa’adi na shayarwa. Kuma wajibi ne a kan wanda aka yi wa haihuwa ya ciyar da su (mata masu shayarwa) da yi musu tufafi ta hanyar da aka saba. Ba a xora wa wani rai sai abin da zai iya. Kar a cutar da uwa saboda xanta, haka kuma kar a cutar da uba saboda xansa. Kuma kwatankwacin irin wannan ya wajaba kan magajinsa. To idan su biyun sun yi nufin yaye bisa ga yarjejeniya da shawara da junansu, to babu laifi a kansu. Kuma idan kun yi nufin nema wa ‘ya’yanku mai shayarwa, to babu laifi a kanku idan kun bayar da abin da ya kamata ta yadda aka saba. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku sani cewa, lalle Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 7

لِّلرِّجَالِ نَصِيبٞ مِّمَّا تَرَكَ ٱلۡوَٰلِدَانِ وَٱلۡأَقۡرَبُونَ وَلِلنِّسَآءِ نَصِيبٞ مِّمَّا تَرَكَ ٱلۡوَٰلِدَانِ وَٱلۡأَقۡرَبُونَ مِمَّا قَلَّ مِنۡهُ أَوۡ كَثُرَۚ نَصِيبٗا مَّفۡرُوضٗا

Mazaje suna da wani kaso daga abin da mahaifa da dangi mafiya kusanci suka bari, haka mata su ma suna da wani kaso cikin abin da mahaifa da dangi mafiya kusanci suka bari, daga abin da yake xan kaxan ko mai yawa. Kaso ne wanda an riga an rarraba shi



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 8

وَإِذَا حَضَرَ ٱلۡقِسۡمَةَ أُوْلُواْ ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينُ فَٱرۡزُقُوهُم مِّنۡهُ وَقُولُواْ لَهُمۡ قَوۡلٗا مَّعۡرُوفٗا

Kuma idan dangi makusanta da marayu da mabuqata suka halarci rabon gado, to ku arzurta su daga cikin wannan dukiya, kuma ku faxa musu magana mai daxi



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 9

وَلۡيَخۡشَ ٱلَّذِينَ لَوۡ تَرَكُواْ مِنۡ خَلۡفِهِمۡ ذُرِّيَّةٗ ضِعَٰفًا خَافُواْ عَلَيۡهِمۡ فَلۡيَتَّقُواْ ٱللَّهَ وَلۡيَقُولُواْ قَوۡلٗا سَدِيدًا

Waxanda suke jin tsoron za su mutu su bar ‘ya’ya raunana a bayansu, suna kuma jin tsoron a zalunce su, to su kiyaye dokokin Allah, kuma su faxi magana ta daidai



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَأۡكُلُونَ أَمۡوَٰلَ ٱلۡيَتَٰمَىٰ ظُلۡمًا إِنَّمَا يَأۡكُلُونَ فِي بُطُونِهِمۡ نَارٗاۖ وَسَيَصۡلَوۡنَ سَعِيرٗا

Lalle waxanda suke cin dukiyar marayu bisa zalunci, wuta ce kawai suke ci a cikkunansu; kuma da sannu za su shiga wuta mai tsananin quna



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 11

يُوصِيكُمُ ٱللَّهُ فِيٓ أَوۡلَٰدِكُمۡۖ لِلذَّكَرِ مِثۡلُ حَظِّ ٱلۡأُنثَيَيۡنِۚ فَإِن كُنَّ نِسَآءٗ فَوۡقَ ٱثۡنَتَيۡنِ فَلَهُنَّ ثُلُثَا مَا تَرَكَۖ وَإِن كَانَتۡ وَٰحِدَةٗ فَلَهَا ٱلنِّصۡفُۚ وَلِأَبَوَيۡهِ لِكُلِّ وَٰحِدٖ مِّنۡهُمَا ٱلسُّدُسُ مِمَّا تَرَكَ إِن كَانَ لَهُۥ وَلَدٞۚ فَإِن لَّمۡ يَكُن لَّهُۥ وَلَدٞ وَوَرِثَهُۥٓ أَبَوَاهُ فَلِأُمِّهِ ٱلثُّلُثُۚ فَإِن كَانَ لَهُۥٓ إِخۡوَةٞ فَلِأُمِّهِ ٱلسُّدُسُۚ مِنۢ بَعۡدِ وَصِيَّةٖ يُوصِي بِهَآ أَوۡ دَيۡنٍۗ ءَابَآؤُكُمۡ وَأَبۡنَآؤُكُمۡ لَا تَدۡرُونَ أَيُّهُمۡ أَقۡرَبُ لَكُمۡ نَفۡعٗاۚ فَرِيضَةٗ مِّنَ ٱللَّهِۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Allah Yana yi muku wasiyya game da ‘ya’yanku; namiji xaya yana da rabon ‘ya’ya mata biyu. Amma idan sun kasance mata ne biyu ko fiye da biyu, to suna da kaso biyu bisa uku na abin da ya bari; kuma idan ta kasance ‘ya ce guda xaya to tana da rabi. Kuma kowane xaya daga cikin mahaifansa biyu yana da kaso xaya bisa shida daga cikin abin da ya bari in ya kasance yana da xa ko ‘ya[1]. Idan kuma ya kasance ba shi da xa ko ‘ya, kuma mahaifansa biyu ne za su ci gadonsa, to mahaifiyarsa tana da kaso xaya bisa uku. Amma idan yana da ‘yan’uwa[2], to mahaifiyarsa tana da kaso xaya bisa shida; bayan an fitar da wasiyyar da aka yi ko kuma bashi[3]. Iyayenku da ‘ya’yanku, ba ku san daga cikinsu wane ne zai fi yi muku amfani ba. Rabo ne daga Allah. Lalle Allah Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai cikakkiyar hikima


1- Ko kuma jika na vangaren ‘ya’ya maza.


2- Watau Shaqiqai ko li’abbai ko li’ummai.


3- Ana fara fitar da bashi, sannan wasiyya wadda ba za ta wuce xaya bisa uku na dukiyar mamaci ba. Kuma babu wasiyya ga wanda yake da gado.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 12

۞وَلَكُمۡ نِصۡفُ مَا تَرَكَ أَزۡوَٰجُكُمۡ إِن لَّمۡ يَكُن لَّهُنَّ وَلَدٞۚ فَإِن كَانَ لَهُنَّ وَلَدٞ فَلَكُمُ ٱلرُّبُعُ مِمَّا تَرَكۡنَۚ مِنۢ بَعۡدِ وَصِيَّةٖ يُوصِينَ بِهَآ أَوۡ دَيۡنٖۚ وَلَهُنَّ ٱلرُّبُعُ مِمَّا تَرَكۡتُمۡ إِن لَّمۡ يَكُن لَّكُمۡ وَلَدٞۚ فَإِن كَانَ لَكُمۡ وَلَدٞ فَلَهُنَّ ٱلثُّمُنُ مِمَّا تَرَكۡتُمۚ مِّنۢ بَعۡدِ وَصِيَّةٖ تُوصُونَ بِهَآ أَوۡ دَيۡنٖۗ وَإِن كَانَ رَجُلٞ يُورَثُ كَلَٰلَةً أَوِ ٱمۡرَأَةٞ وَلَهُۥٓ أَخٌ أَوۡ أُخۡتٞ فَلِكُلِّ وَٰحِدٖ مِّنۡهُمَا ٱلسُّدُسُۚ فَإِن كَانُوٓاْ أَكۡثَرَ مِن ذَٰلِكَ فَهُمۡ شُرَكَآءُ فِي ٱلثُّلُثِۚ مِنۢ بَعۡدِ وَصِيَّةٖ يُوصَىٰ بِهَآ أَوۡ دَيۡنٍ غَيۡرَ مُضَآرّٖۚ وَصِيَّةٗ مِّنَ ٱللَّهِۗ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَلِيمٞ

Kuma kuna da rabin abin da matanku suka bari in ya kasance ba su da xa ko ‘ya, amma idan sun kasance suna da xa ko ‘ya, to kuna da kaso xaya bisa huxu na abin da suka bari, bayan zartar da wasiyyar da suka yi ko kuma bashi. Kuma suna da kaso xaya bisa huxu[1] na abin da kuka bari, in ya kasance ba ku da xa ko ‘ya. Amma idan ya kasance kuna da xa ko ‘ya to (matanku) suna da kaso xaya cikin takwas na abin da kuka bari, bayan zartar da wasiyyar da kuka yi ko kuma bashi. Amma idan namiji ne za a gaje shi a matsayin kalala[2] ko mace, kuma yana da xan’uwa guda xaya ko ‘yar’uwa guda xaya, to kowanne xaya yana da kaso xaya bisa shida. Amma idan sun fi haka yawa, to za su yi tarayya cikin kaso xaya bisa uku, bayan zartar da wasiyyar da aka yi ko kuma bashi, ba wanda zai cutar da (magadansa) ba. Allah Yana yi muku wasiyya matuqar wasiyya. Allah kuma Mai cikakken sani ne, Mai haquri


1- Idan sama da mace xaya ce, to za su yi tarayya ne a cikin wannan kason.


2- Kalala shi ne mamaci; namiji ko mace da bai bar ‘ya’ya ko iyaye ba, sai ‘yan’uwa.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 33

وَلِكُلّٖ جَعَلۡنَا مَوَٰلِيَ مِمَّا تَرَكَ ٱلۡوَٰلِدَانِ وَٱلۡأَقۡرَبُونَۚ وَٱلَّذِينَ عَقَدَتۡ أَيۡمَٰنُكُمۡ فَـَٔاتُوهُمۡ نَصِيبَهُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدًا

Kuma kowa Mun sanya masa magadansa daga abin da mahaifa suka bari ko dangi mafiya kusanci[1]. Su kuma waxanda rantsuwar qulla (zumunci) ta haxa tsakaninku, to ku ba su rabonsu[2]. Lalle Allah Ya kasance Mai tsinkaye ne a kan komai


1- Ana nufin masu cin gado ta hanyar asibci.


2- An shafe wannan hukuncin da aya ta 75 ta Suratul Anfal.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 36

۞وَٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ وَلَا تُشۡرِكُواْ بِهِۦ شَيۡـٔٗاۖ وَبِٱلۡوَٰلِدَيۡنِ إِحۡسَٰنٗا وَبِذِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَٱلۡجَارِ ذِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡجَارِ ٱلۡجُنُبِ وَٱلصَّاحِبِ بِٱلۡجَنۢبِ وَٱبۡنِ ٱلسَّبِيلِ وَمَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُكُمۡۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُحِبُّ مَن كَانَ مُخۡتَالٗا فَخُورًا

Kuma ku bauta wa Allah (Shi kaxai), kada ku haxa Shi da komai; kuma ku kyautata wa iyaye da dangi makusanta da marayu da talakawa da maqwabci makusanci da maqwabci na nesa, da abokin da ake tare[1] da kuma matafiyi da bayinku. Lalle Allah ba Ya son duk wanda ya kasance mai taqama, mai yawan fariya


1- Watau wanda tafiya ta haxa mutun da shi ko kuma matarsa.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 127

وَيَسۡتَفۡتُونَكَ فِي ٱلنِّسَآءِۖ قُلِ ٱللَّهُ يُفۡتِيكُمۡ فِيهِنَّ وَمَا يُتۡلَىٰ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ فِي يَتَٰمَى ٱلنِّسَآءِ ٱلَّـٰتِي لَا تُؤۡتُونَهُنَّ مَا كُتِبَ لَهُنَّ وَتَرۡغَبُونَ أَن تَنكِحُوهُنَّ وَٱلۡمُسۡتَضۡعَفِينَ مِنَ ٱلۡوِلۡدَٰنِ وَأَن تَقُومُواْ لِلۡيَتَٰمَىٰ بِٱلۡقِسۡطِۚ وَمَا تَفۡعَلُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِهِۦ عَلِيمٗا

Kuma suna neman fatawarka game da lamarin mata. Ka ce: “Allah ne Yake ba ku fatawa game da lamarinsu da kuma abin da ake karanta muku a cikin Littafi dangane da marayu mata waxanda ba kwa iya ba su sadakinsu cikakke, ga shi kuma kuna kwaxayin ku aure su; hakanan da kuma (dukiyar) yara masu rauni. Kuma ku tsaya wajen kula da (dukiyar) marayu ta hanyar adalci. Kuma duk abin da kuka aikata na alheri, to lalle Allah Yana sane da shi.”



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 135

۞يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ كُونُواْ قَوَّـٰمِينَ بِٱلۡقِسۡطِ شُهَدَآءَ لِلَّهِ وَلَوۡ عَلَىٰٓ أَنفُسِكُمۡ أَوِ ٱلۡوَٰلِدَيۡنِ وَٱلۡأَقۡرَبِينَۚ إِن يَكُنۡ غَنِيًّا أَوۡ فَقِيرٗا فَٱللَّهُ أَوۡلَىٰ بِهِمَاۖ فَلَا تَتَّبِعُواْ ٱلۡهَوَىٰٓ أَن تَعۡدِلُواْۚ وَإِن تَلۡوُۥٓاْ أَوۡ تُعۡرِضُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku zamo masu tsayawa da adalci, kuna masu ba da shaida don Allah, ko da kuwa a kan kawunanku ne ko a kan mahaifanku ko a kan dangi makusanta. Idan ya kasance mawadaci ne ko matalauci, to Allah Shi ne Ya fi sanin abin da ya fi cancanta gare su[1]; don haka kada ku bi son zuciyarku ku qi yin adalci. Idan kuwa kuka karkatar da shaida ko kuka qi ba da ita, to lalle Allah Ya kasance Mai cikakken sanin abin da kuke aikatawa ne


1- Watau da mai wadata da matalauci duk al'amuransu na ga Allah, ya fi kowa sanin abin da ya fi zama maslaha a gare su.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 176

يَسۡتَفۡتُونَكَ قُلِ ٱللَّهُ يُفۡتِيكُمۡ فِي ٱلۡكَلَٰلَةِۚ إِنِ ٱمۡرُؤٌاْ هَلَكَ لَيۡسَ لَهُۥ وَلَدٞ وَلَهُۥٓ أُخۡتٞ فَلَهَا نِصۡفُ مَا تَرَكَۚ وَهُوَ يَرِثُهَآ إِن لَّمۡ يَكُن لَّهَا وَلَدٞۚ فَإِن كَانَتَا ٱثۡنَتَيۡنِ فَلَهُمَا ٱلثُّلُثَانِ مِمَّا تَرَكَۚ وَإِن كَانُوٓاْ إِخۡوَةٗ رِّجَالٗا وَنِسَآءٗ فَلِلذَّكَرِ مِثۡلُ حَظِّ ٱلۡأُنثَيَيۡنِۗ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمۡ أَن تَضِلُّواْۗ وَٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمُۢ

Suna neman ka yi musu fatawa, ka ce: “Allah ne zai yi muku fatawa game da kalala. Idan mutum ya mutu ba shi da xa ko ‘ya, amma yana da ‘yar’uwa mace, to za a ba ta rabin abin da ya bari. Shi kuwa zai gaje (dukiyar) ta gaba xaya idan ya kasance ba ta da xa ko ‘ya. Amma idan suka kasance mata ne su biyu, to suna da biyu bisa uku na abin da ya bari. Idan kuwa sun kasance ‘yan’uwa masu yawa maza da mata, to duk namiji xaya yana da rabon mata biyu.” Allah Yana bayyana muku wannan ne don kar ku vace. Kuma Allah Masanin komai ne



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 106

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ شَهَٰدَةُ بَيۡنِكُمۡ إِذَا حَضَرَ أَحَدَكُمُ ٱلۡمَوۡتُ حِينَ ٱلۡوَصِيَّةِ ٱثۡنَانِ ذَوَا عَدۡلٖ مِّنكُمۡ أَوۡ ءَاخَرَانِ مِنۡ غَيۡرِكُمۡ إِنۡ أَنتُمۡ ضَرَبۡتُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَأَصَٰبَتۡكُم مُّصِيبَةُ ٱلۡمَوۡتِۚ تَحۡبِسُونَهُمَا مِنۢ بَعۡدِ ٱلصَّلَوٰةِ فَيُقۡسِمَانِ بِٱللَّهِ إِنِ ٱرۡتَبۡتُمۡ لَا نَشۡتَرِي بِهِۦ ثَمَنٗا وَلَوۡ كَانَ ذَا قُرۡبَىٰ وَلَا نَكۡتُمُ شَهَٰدَةَ ٱللَّهِ إِنَّآ إِذٗا لَّمِنَ ٱلۡأٓثِمِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, shaidar da take tsakaninku idan alamun mutuwa suka zo wa xaya daga cikinku, yayin da ya so ya yi wasiyya, shi ne a samu mutum biyu masu adalci daga cikinku ko kuma waxansu biyu daga wasunku (kafirai), yayin da kuka yi tafiya a bayan qasa, sai musibar mutuwa ta same ku. Za ku tsayar da su (shaidun) biyun ne bayan an kammala salla, sai su rantse da Allah- idan har kun yi shakka game da su-: “Wallahi, ba za mu musanya shi da wani farashi ba, ko da kuwa ya zamo ma’abocin kusanci ne, kuma ba za mu voye shaidar Allah ba, lalle kuwa idan har muka yi haka, tabbas muna cikin masu laifi.”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 151

۞قُلۡ تَعَالَوۡاْ أَتۡلُ مَا حَرَّمَ رَبُّكُمۡ عَلَيۡكُمۡۖ أَلَّا تُشۡرِكُواْ بِهِۦ شَيۡـٔٗاۖ وَبِٱلۡوَٰلِدَيۡنِ إِحۡسَٰنٗاۖ وَلَا تَقۡتُلُوٓاْ أَوۡلَٰدَكُم مِّنۡ إِمۡلَٰقٖ نَّحۡنُ نَرۡزُقُكُمۡ وَإِيَّاهُمۡۖ وَلَا تَقۡرَبُواْ ٱلۡفَوَٰحِشَ مَا ظَهَرَ مِنۡهَا وَمَا بَطَنَۖ وَلَا تَقۡتُلُواْ ٱلنَّفۡسَ ٱلَّتِي حَرَّمَ ٱللَّهُ إِلَّا بِٱلۡحَقِّۚ ذَٰلِكُمۡ وَصَّىٰكُم بِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Ka ce: “Ku taho in karanta muku abin da Ubangijinku Ya haramta muku; kada ku haxa Shi da wani; kuma ku kyautata wa mahaifa; kuma kar ku kashe ‘ya’yanku saboda talauci; Mu ne za Mu arzuta ku har da su; kuma kada ku kusanci munanan (ayyuka) na sarari da na voye; kuma kada ku kashe ran da Allah Ya haramta (a kashe shi), sai idan da wani hakki. Wannan shi ne abin da (Allah) Ya yi muku wasiyya da shi, don ku zamo masu hankali



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 152

وَلَا تَقۡرَبُواْ مَالَ ٱلۡيَتِيمِ إِلَّا بِٱلَّتِي هِيَ أَحۡسَنُ حَتَّىٰ يَبۡلُغَ أَشُدَّهُۥۚ وَأَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَٱلۡمِيزَانَ بِٱلۡقِسۡطِۖ لَا نُكَلِّفُ نَفۡسًا إِلَّا وُسۡعَهَاۖ وَإِذَا قُلۡتُمۡ فَٱعۡدِلُواْ وَلَوۡ كَانَ ذَا قُرۡبَىٰۖ وَبِعَهۡدِ ٱللَّهِ أَوۡفُواْۚ ذَٰلِكُمۡ وَصَّىٰكُم بِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تَذَكَّرُونَ

“Kuma kada ku kusanci dukiyar maraya sai da kyakkyawar niyya, har sai qarfinsa ya kawo; kuma ku cika ma’auni na mudu da na nauyi bisa adalci; ba ma xora wa rai sai abin da zai iya. Kuma idan za ku yi magana to ku yi adalci, ko da kuwa a kan xan’uwa ne na kusa; kuma lalle ku cika alqawarin Allah. Wannan ne abin da (Allah) Yake yi muku wasicci da shi, don ku wa’azantu.”



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 113

مَا كَانَ لِلنَّبِيِّ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَن يَسۡتَغۡفِرُواْ لِلۡمُشۡرِكِينَ وَلَوۡ كَانُوٓاْ أُوْلِي قُرۡبَىٰ مِنۢ بَعۡدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمۡ أَنَّهُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡجَحِيمِ

Bai kamata ba ga Annabi da waxanda suka yi imani su nema wa mushrikai gafara, ko da kuwa sun kasance dangi ne na kusa, bayan kuwa ya riga ya bayyana gare su cewa lalle su ‘yan wuta ne



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 114

وَمَا كَانَ ٱسۡتِغۡفَارُ إِبۡرَٰهِيمَ لِأَبِيهِ إِلَّا عَن مَّوۡعِدَةٖ وَعَدَهَآ إِيَّاهُ فَلَمَّا تَبَيَّنَ لَهُۥٓ أَنَّهُۥ عَدُوّٞ لِّلَّهِ تَبَرَّأَ مِنۡهُۚ إِنَّ إِبۡرَٰهِيمَ لَأَوَّـٰهٌ حَلِيمٞ

Neman gafarar Ibrahimu kuwa ga babansa bai kasance ba sai don kawai alqawarin da ya yi masa ne. To lokacin da ya bayyana gare shi cewa shi maqiyin Allah ne sai ya nesanta kansa da shi. Lalle Ibrahimu ya tabbata mai yawan bautar Allah ne, mai haquri



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 90

۞إِنَّ ٱللَّهَ يَأۡمُرُ بِٱلۡعَدۡلِ وَٱلۡإِحۡسَٰنِ وَإِيتَآيِٕ ذِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَيَنۡهَىٰ عَنِ ٱلۡفَحۡشَآءِ وَٱلۡمُنكَرِ وَٱلۡبَغۡيِۚ يَعِظُكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَذَكَّرُونَ

Lalle Allah Yana umarni da yin adalci da kyautatawa da kuma bai wa makusanta (taimako), Yana kuma hana alfasha da mummunan aiki da zalunci. Yana gargaxin ku don ku wa’azantu



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 23

۞وَقَضَىٰ رَبُّكَ أَلَّا تَعۡبُدُوٓاْ إِلَّآ إِيَّاهُ وَبِٱلۡوَٰلِدَيۡنِ إِحۡسَٰنًاۚ إِمَّا يَبۡلُغَنَّ عِندَكَ ٱلۡكِبَرَ أَحَدُهُمَآ أَوۡ كِلَاهُمَا فَلَا تَقُل لَّهُمَآ أُفّٖ وَلَا تَنۡهَرۡهُمَا وَقُل لَّهُمَا قَوۡلٗا كَرِيمٗا

Ubangijinka kuwa Ya hukunta cewa, kada ku bauta wa (wani) sai Shi kaxai, kuma ku kyautatawa iyaye. Ko dai ya zamanto xayansu ne ya manyanta tare da kai, ko kuma dukkansu, to kada ka nuna qosawarka da su, kada kuma ka daka musu tsawa; ka yi musu magana ta girmamawa



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 24

وَٱخۡفِضۡ لَهُمَا جَنَاحَ ٱلذُّلِّ مِنَ ٱلرَّحۡمَةِ وَقُل رَّبِّ ٱرۡحَمۡهُمَا كَمَا رَبَّيَانِي صَغِيرٗا

Ka kuma qasqantar da kai gare su don tausayawa, ka kuma ce: “Ubangijina Ka ji qan su kamar yadda suka raine ni ina xan qarami.”



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 26

وَءَاتِ ذَا ٱلۡقُرۡبَىٰ حَقَّهُۥ وَٱلۡمِسۡكِينَ وَٱبۡنَ ٱلسَّبِيلِ وَلَا تُبَذِّرۡ تَبۡذِيرًا

Kuma ka bai wa makusanci haqqinsa, da miskini da matafiyi, kada kuma ka yi kowane irin almubazzaranci



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 31

وَلَا تَقۡتُلُوٓاْ أَوۡلَٰدَكُمۡ خَشۡيَةَ إِمۡلَٰقٖۖ نَّحۡنُ نَرۡزُقُهُمۡ وَإِيَّاكُمۡۚ إِنَّ قَتۡلَهُمۡ كَانَ خِطۡـٔٗا كَبِيرٗا

Kada kuma ku kashe ‘ya’yayenku don tsoron talauci: Mu ne Muke arzuta su har ma da ku. Lalle kashe su kuskure ne babba



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 22

وَلَا يَأۡتَلِ أُوْلُواْ ٱلۡفَضۡلِ مِنكُمۡ وَٱلسَّعَةِ أَن يُؤۡتُوٓاْ أُوْلِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينَ وَٱلۡمُهَٰجِرِينَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ وَلۡيَعۡفُواْ وَلۡيَصۡفَحُوٓاْۗ أَلَا تُحِبُّونَ أَن يَغۡفِرَ ٱللَّهُ لَكُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

Kuma kada masu hali da wadata daga cikinku su rantse a kan qin ba da (abin hannunsu) ga makusanta da miskinai da masu hijira saboda Allah. Su kuma yi afuwa su yafe. Shin ku ba kwa so ne Allah Ya gafarta muku? Allah kuwa Mai gafara ne, Mai jin qai[1]


1- Ayar tana magana ne a kan Abubakar () lokacin da ya yi rantsuwa ba zai ci gaba da taimaka wa xan innarsa Misxahu xan Usasa ba domin ya zama cikin masu kwaza qagen da aka yi wa Nana A’isha (RAH)..


Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 8

وَوَصَّيۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ بِوَٰلِدَيۡهِ حُسۡنٗاۖ وَإِن جَٰهَدَاكَ لِتُشۡرِكَ بِي مَا لَيۡسَ لَكَ بِهِۦ عِلۡمٞ فَلَا تُطِعۡهُمَآۚ إِلَيَّ مَرۡجِعُكُمۡ فَأُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Kuma Mun yi wa mutum wasiyya da kyautata wa iyayensa; idan kuma suka yaqe ka kan ka yi shirka da Ni game da abin da ba ka da sani a kansa, to kada ka bi su. Wurina ne makomarku take kawai, sannan zan ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa