Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 37

فَتَلَقَّىٰٓ ءَادَمُ مِن رَّبِّهِۦ كَلِمَٰتٖ فَتَابَ عَلَيۡهِۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Sai Adamu ya karvi wasu kalmomi daga Ubangijinsa (na neman gafara), sai Ya yafe masa; lalle Shi ne Mai yawan karvar tuba kuma Mai yawan jin qai



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 160

إِلَّا ٱلَّذِينَ تَابُواْ وَأَصۡلَحُواْ وَبَيَّنُواْ فَأُوْلَـٰٓئِكَ أَتُوبُ عَلَيۡهِمۡ وَأَنَا ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Sai dai waxanda suka tuba kuma suka gyara kuma suka bayyana, to waxannan zan karvi tubansu, kuma lalle Ni Mai karvar tuba ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 89

إِلَّا ٱلَّذِينَ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ وَأَصۡلَحُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

Sai fa waxanda suka sake tuba bayan haka, kuma suka gyara (ayyukansu), to lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 136

أُوْلَـٰٓئِكَ جَزَآؤُهُم مَّغۡفِرَةٞ مِّن رَّبِّهِمۡ وَجَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ وَنِعۡمَ أَجۡرُ ٱلۡعَٰمِلِينَ

Waxannan sakamakonsu shi ne gafara ta musamman daga Ubangijinsu, da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dawwama a cikinsu. Kuma madalla da sakamakon masu aiki



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 17

إِنَّمَا ٱلتَّوۡبَةُ عَلَى ٱللَّهِ لِلَّذِينَ يَعۡمَلُونَ ٱلسُّوٓءَ بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ يَتُوبُونَ مِن قَرِيبٖ فَأُوْلَـٰٓئِكَ يَتُوبُ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمۡۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Tuban da Allah Yake karva kawai (ita ce) na waxanda suke aikata mummunan aiki da jahilci, sannan su gaggauta tuba, to waxannan Allah zai karvi tubansu. Allah kuma Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 18

وَلَيۡسَتِ ٱلتَّوۡبَةُ لِلَّذِينَ يَعۡمَلُونَ ٱلسَّيِّـَٔاتِ حَتَّىٰٓ إِذَا حَضَرَ أَحَدَهُمُ ٱلۡمَوۡتُ قَالَ إِنِّي تُبۡتُ ٱلۡـَٰٔنَ وَلَا ٱلَّذِينَ يَمُوتُونَ وَهُمۡ كُفَّارٌۚ أُوْلَـٰٓئِكَ أَعۡتَدۡنَا لَهُمۡ عَذَابًا أَلِيمٗا

Kuma ba a karvar tuba daga waxanda suke aikata munanan ayyuka har sai lokacin da mutuwa ta zo wa xayansu, sai ya ce: “Ni kam na tuba yanzu;” kuma ba a karvar tuban waxanda suke mutuwa alhalin suna kafirai. Waxannan Mun yi musu tanadin azaba mai raxaxi



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 48

إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَغۡفِرُ أَن يُشۡرَكَ بِهِۦ وَيَغۡفِرُ مَا دُونَ ذَٰلِكَ لِمَن يَشَآءُۚ وَمَن يُشۡرِكۡ بِٱللَّهِ فَقَدِ ٱفۡتَرَىٰٓ إِثۡمًا عَظِيمًا

Lalle Allah ba Ya gafarta a yi shirka da Shi, amma Yana gafarta abin da bai kai shirka ba ga wanda Ya ga dama. Kuma duk wanda ya yi shirka da Allah, to haqiqa ya qirqiri wani gagarumin laifi



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 64

وَمَآ أَرۡسَلۡنَا مِن رَّسُولٍ إِلَّا لِيُطَاعَ بِإِذۡنِ ٱللَّهِۚ وَلَوۡ أَنَّهُمۡ إِذ ظَّلَمُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ جَآءُوكَ فَٱسۡتَغۡفَرُواْ ٱللَّهَ وَٱسۡتَغۡفَرَ لَهُمُ ٱلرَّسُولُ لَوَجَدُواْ ٱللَّهَ تَوَّابٗا رَّحِيمٗا

Kuma ba Mu tava aiko wani manzo ba, face sai don a yi masa xa’a da izinin Allah. Kuma da a ce lokacin da suka zalunci kawunansu sun zo maka, sun nemi Allah Ya gafarta musu, sannan Manzo ya roqa musu gafara, to tabbas da sun sami Allah Yana Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 110

وَمَن يَعۡمَلۡ سُوٓءًا أَوۡ يَظۡلِمۡ نَفۡسَهُۥ ثُمَّ يَسۡتَغۡفِرِ ٱللَّهَ يَجِدِ ٱللَّهَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma duk wanda ya aikata mummunan aiki ko ya zalunci kansa, sannan ya nemi gafarar Allah, to zai sami Allah Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 116

إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَغۡفِرُ أَن يُشۡرَكَ بِهِۦ وَيَغۡفِرُ مَا دُونَ ذَٰلِكَ لِمَن يَشَآءُۚ وَمَن يُشۡرِكۡ بِٱللَّهِ فَقَدۡ ضَلَّ ضَلَٰلَۢا بَعِيدًا

Lalle Allah ba Ya gafartawa a yi masa shirka, Yana kuwa gafarta abin da bai kai shirka ba ga wanda Ya ga dama. Duk wanda ya yi wa Allah shirka, to haqiqa ya vata manisanciyar vata



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 146

إِلَّا ٱلَّذِينَ تَابُواْ وَأَصۡلَحُواْ وَٱعۡتَصَمُواْ بِٱللَّهِ وَأَخۡلَصُواْ دِينَهُمۡ لِلَّهِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ مَعَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۖ وَسَوۡفَ يُؤۡتِ ٱللَّهُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ أَجۡرًا عَظِيمٗا

Sai fa waxanda suka tuba, kuma suka gyara aikinsu, kuma suka yi riqo ga igiyar Allah; kuma suka tsantsanta addininsu don Allah; to waxannan suna tare da muminai; kuma Allah zai bai wa muminai lada mai girma



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 34

إِلَّا ٱلَّذِينَ تَابُواْ مِن قَبۡلِ أَن تَقۡدِرُواْ عَلَيۡهِمۡۖ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Sai dai waxanda suka tuba tun kafin ku sami damar kama su; to ku sani cewa, lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 39

فَمَن تَابَ مِنۢ بَعۡدِ ظُلۡمِهِۦ وَأَصۡلَحَ فَإِنَّ ٱللَّهَ يَتُوبُ عَلَيۡهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

To (amma) wanda ya tuba bayan zaluncinsa, kuma ya gyara aikinsa, to lalle Allah zai karvi tubansa. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 54

وَإِذَا جَآءَكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِـَٔايَٰتِنَا فَقُلۡ سَلَٰمٌ عَلَيۡكُمۡۖ كَتَبَ رَبُّكُمۡ عَلَىٰ نَفۡسِهِ ٱلرَّحۡمَةَ أَنَّهُۥ مَنۡ عَمِلَ مِنكُمۡ سُوٓءَۢا بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ تَابَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَصۡلَحَ فَأَنَّهُۥ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Kuma idan waxanda suke yin imani da ayoyinmu sun zo wurinka, to ka ce: “Sallama a gare ku;” Ubangijinku Ya wajabta wa kansa yin rahama cewa, lalle cikinku duk wanda ya aikata wani mummunan aiki bisa ga jahilci, sannan daga baya ya tuba kuma ya kyautata aiki, to Shi Mai gafara ne, Mai jin qai.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 153

وَٱلَّذِينَ عَمِلُواْ ٱلسَّيِّـَٔاتِ ثُمَّ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِهَا وَءَامَنُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Waxanda kuma suka aikata munanan ayyuka, sannan suka tuba daga baya, kuma suka yi imani, lalle Ubangijinka bayansa (tuban), tabbas Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 102

وَءَاخَرُونَ ٱعۡتَرَفُواْ بِذُنُوبِهِمۡ خَلَطُواْ عَمَلٗا صَٰلِحٗا وَءَاخَرَ سَيِّئًا عَسَى ٱللَّهُ أَن يَتُوبَ عَلَيۡهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

Wasu kuwa sun yi iqirari da laifinsu, sun gauraya kyakkyawan aiki da wani mummuna, to tabbas Allah zai karvi tubansu. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 104

أَلَمۡ يَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ هُوَ يَقۡبَلُ ٱلتَّوۡبَةَ عَنۡ عِبَادِهِۦ وَيَأۡخُذُ ٱلصَّدَقَٰتِ وَأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Shin yanzu ba su sani ba ne cewa Allah Shi Yake karvar tuba daga bayinsa Yake kuma karvar sadakoki, kuma lalle Shi ne Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai?



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 117

لَّقَد تَّابَ ٱللَّهُ عَلَى ٱلنَّبِيِّ وَٱلۡمُهَٰجِرِينَ وَٱلۡأَنصَارِ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُوهُ فِي سَاعَةِ ٱلۡعُسۡرَةِ مِنۢ بَعۡدِ مَا كَادَ يَزِيغُ قُلُوبُ فَرِيقٖ مِّنۡهُمۡ ثُمَّ تَابَ عَلَيۡهِمۡۚ إِنَّهُۥ بِهِمۡ رَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Tabbas haqiqa Allah Ya yafe wa Annabi da masu hijira da kuma Ansaru waxanda suka bi shi a lokacin tsanani bayan har zukatan wasu qungiyoyi daga cikinsu sun kusa su karkace, sannan (Allah) Ya karvi tubansu. Lalle Shi Mai tausasawa ne, Mai jin qai a gare su



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 118

وَعَلَى ٱلثَّلَٰثَةِ ٱلَّذِينَ خُلِّفُواْ حَتَّىٰٓ إِذَا ضَاقَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلۡأَرۡضُ بِمَا رَحُبَتۡ وَضَاقَتۡ عَلَيۡهِمۡ أَنفُسُهُمۡ وَظَنُّوٓاْ أَن لَّا مَلۡجَأَ مِنَ ٱللَّهِ إِلَّآ إِلَيۡهِ ثُمَّ تَابَ عَلَيۡهِمۡ لِيَتُوبُوٓاْۚ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma (Ya yafe wa) mutanen nan guda uku waxanda aka dakatar da karvar tubansu[1], har sai yayin da duniya ta yi musu qunci duk da yalwarta, kuma zukatansu suka quntata, suka tabbatar da cewa dai babu wata mafaka daga Allah sai dai a wajensa. Sannan sai Ya yi musu muwafaqar tuba don su tuba. Lalle Allah Shi ne Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai


1- Su ne sahabban nan uku, watau Ka’abu xan Maliku da Muraratu xan Rabi’atu da Hilal xan Umayyatu Al-Waqifi. Sun qi fita yaqin Tabuka tare da Annabi () ba tare da wani uzuri ba.


Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 49

۞نَبِّئۡ عِبَادِيٓ أَنِّيٓ أَنَا ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Ka bai wa bayina labarin cewa lalle Ni, Ni ne Mai gafara, Mai jin qai



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 110

ثُمَّ إِنَّ رَبَّكَ لِلَّذِينَ هَاجَرُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا فُتِنُواْ ثُمَّ جَٰهَدُواْ وَصَبَرُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Sannan lalle Ubangjinka (Mai gafara ne da jin qai) ga waxanda suka yi hijira bayan an fitine su, sannan suka yi jihadi suka kuma yi haquri, lalle Ubangijinka, bayansu (waxannan ayyuka) Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 119

ثُمَّ إِنَّ رَبَّكَ لِلَّذِينَ عَمِلُواْ ٱلسُّوٓءَ بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ وَأَصۡلَحُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٌ

Sannan lalle Ubangijinka (Mai gafara ne) ga waxanda suka aikata mummuna a cikin jahilci sannan suka tuba bayan haka suka kuma gyara, lalle Ubagijinka Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratu Xa Ha

Verso : 82

وَإِنِّي لَغَفَّارٞ لِّمَن تَابَ وَءَامَنَ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا ثُمَّ ٱهۡتَدَىٰ

Lalle Ni kuma Mai yawan gafara ne ga wanda ya tuba kuma ya yi aiki na gari sannan ya (tabbata bisa) shiriya



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 5

إِلَّا ٱلَّذِينَ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ وَأَصۡلَحُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Sai dai waxanda suka tuba bayan wannan suka kuma gyara, to haqiqa Allah Mai gafara ne, Mai jin qai ne



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 70

إِلَّا مَن تَابَ وَءَامَنَ وَعَمِلَ عَمَلٗا صَٰلِحٗا فَأُوْلَـٰٓئِكَ يُبَدِّلُ ٱللَّهُ سَيِّـَٔاتِهِمۡ حَسَنَٰتٖۗ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Sai dai wanda ya tuba ya kuma yi imani, kuma ya yi aiki na gari, to waxannan Allah zai musanya munanan ayyukansu da kyawawa. Allah kuwa ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 71

وَمَن تَابَ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَإِنَّهُۥ يَتُوبُ إِلَى ٱللَّهِ مَتَابٗا

Wanda kuwa ya tuba ya kuma yi aiki na gari, to lalle shi ne wanda yake tuba na gaskiya zuwa ga Allah



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 16

قَالَ رَبِّ إِنِّي ظَلَمۡتُ نَفۡسِي فَٱغۡفِرۡ لِي فَغَفَرَ لَهُۥٓۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni na zalunci kaina, sai Ka yi min gafara,” sai ko Ya yi masa gafara. Lalle Shi kuwa Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 67

فَأَمَّا مَن تَابَ وَءَامَنَ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَعَسَىٰٓ أَن يَكُونَ مِنَ ٱلۡمُفۡلِحِينَ

To amma wanda ya tuba ya kuma yi imani ya kuma yi aiki nagari, to ana fatan ya zama cikin masu samun babban rabo



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 73

لِّيُعَذِّبَ ٱللَّهُ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱلۡمُنَٰفِقَٰتِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ وَٱلۡمُشۡرِكَٰتِ وَيَتُوبَ ٱللَّهُ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِۗ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمَۢا

Don Allah Ya azabtar da munafukai maza da munafukai mata, da mushirikai maza da mushirikai mata, Ya kuma karvi tubar muminai maza da muminai mata. Allah kuwa Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 25

وَهُوَ ٱلَّذِي يَقۡبَلُ ٱلتَّوۡبَةَ عَنۡ عِبَادِهِۦ وَيَعۡفُواْ عَنِ ٱلسَّيِّـَٔاتِ وَيَعۡلَمُ مَا تَفۡعَلُونَ

Shi ne kuma wanda Yake karvar tuba daga bayinsa, Yake kuma yin afuwa game da munanan (ayyuka), Yana kuma sane da abin da kuke aikatawa