Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 85

وَإِلَىٰ مَدۡيَنَ أَخَاهُمۡ شُعَيۡبٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥۖ قَدۡ جَآءَتۡكُم بَيِّنَةٞ مِّن رَّبِّكُمۡۖ فَأَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَٱلۡمِيزَانَ وَلَا تَبۡخَسُواْ ٱلنَّاسَ أَشۡيَآءَهُمۡ وَلَا تُفۡسِدُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ بَعۡدَ إِصۡلَٰحِهَاۚ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Kuma (Mun) aika wa mutanen Madyana xan’uwansu Shu’aibu, ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi, haqiqa hujja ta zo muku daga Ubangijinku; don haka ku riqa cika mudu, kuma ku (kiyaye) ma’auni, kuma kada ku tauye wa mutane abubuwansu, kuma kada ku yi varna a bayan qasa bayan an gyara ta. Wannan shi ne mafi alheri a gare ku in kun kasance muminai



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 86

وَلَا تَقۡعُدُواْ بِكُلِّ صِرَٰطٖ تُوعِدُونَ وَتَصُدُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ مَنۡ ءَامَنَ بِهِۦ وَتَبۡغُونَهَا عِوَجٗاۚ وَٱذۡكُرُوٓاْ إِذۡ كُنتُمۡ قَلِيلٗا فَكَثَّرَكُمۡۖ وَٱنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُفۡسِدِينَ

“Kuma kada ku zauna a kan kowace hanya kuna tsoratar da (mutane), kuma kuna toshe hanyar Allah ga duk wanda ya yi imani da Shi, kuna kuma son ta zama karkatacciya. Kuma ku tuna (ni’imar Allah) lokacin da kuke ‘yan kaxan, sai Ya yawaita ku, kuma ku duba ku ga yaya qarshen mavarnata ya kasance?



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 87

وَإِن كَانَ طَآئِفَةٞ مِّنكُمۡ ءَامَنُواْ بِٱلَّذِيٓ أُرۡسِلۡتُ بِهِۦ وَطَآئِفَةٞ لَّمۡ يُؤۡمِنُواْ فَٱصۡبِرُواْ حَتَّىٰ يَحۡكُمَ ٱللَّهُ بَيۡنَنَاۚ وَهُوَ خَيۡرُ ٱلۡحَٰكِمِينَ

“Idan kuma an sami wata qungiya daga cikinku sun yi imani da abin da aka aiko ni da shi, wata qungiyar kuma ba su yi imani ba, to ku yi haquri har Allah Ya yi hukunci a tsakaninmu. Kuma Shi ne Fiyayyen masu hukunci.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 88

۞قَالَ ٱلۡمَلَأُ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُواْ مِن قَوۡمِهِۦ لَنُخۡرِجَنَّكَ يَٰشُعَيۡبُ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَكَ مِن قَرۡيَتِنَآ أَوۡ لَتَعُودُنَّ فِي مِلَّتِنَاۚ قَالَ أَوَلَوۡ كُنَّا كَٰرِهِينَ

Sai manyan gari, waxanda suka yi girman kai daga cikin mutanensa suka ce: “Lalle za mu fitar da kai, ya kai Shu’aibu, da waxanda suka yi imani tare da kai, daga alqaryarmu, ko kuma ku dawo cikin addininmu.” (Shu’aibu) ya ce: “Ko da muna qin (hakan)?”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 89

قَدِ ٱفۡتَرَيۡنَا عَلَى ٱللَّهِ كَذِبًا إِنۡ عُدۡنَا فِي مِلَّتِكُم بَعۡدَ إِذۡ نَجَّىٰنَا ٱللَّهُ مِنۡهَاۚ وَمَا يَكُونُ لَنَآ أَن نَّعُودَ فِيهَآ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّنَاۚ وَسِعَ رَبُّنَا كُلَّ شَيۡءٍ عِلۡمًاۚ عَلَى ٱللَّهِ تَوَكَّلۡنَاۚ رَبَّنَا ٱفۡتَحۡ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَ قَوۡمِنَا بِٱلۡحَقِّ وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلۡفَٰتِحِينَ

“Haqiqa mun qirqiri qarya, mun jingina wa Allah, in har muka komo cikin addininku, bayan kuwa Allah Ya tserar da mu daga gare shi. Kuma ba ma zai yiwu ba mu koma cikinsa sai dai idan Allah Ubangijinmu ne Ya ga dama. Kuma ilimin Ubangijinmu Ya yalwaci komai. Ga Allah kaxai muka dogara. Ya Ubangijinmu, Ka yi hukunci tsakaninmu da mutanenmu da gaskiya, kuma Kai ne Fiyayyen masu hukunci.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 90

وَقَالَ ٱلۡمَلَأُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن قَوۡمِهِۦ لَئِنِ ٱتَّبَعۡتُمۡ شُعَيۡبًا إِنَّكُمۡ إِذٗا لَّخَٰسِرُونَ

Sai manyan gari waxanda suka kafirce daga cikin mutanensa, suka ce: “Wallahi idan kun bi Shu’aibu fa, lalle ku tabbas kuna cikin hasararru.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 91

فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلرَّجۡفَةُ فَأَصۡبَحُواْ فِي دَارِهِمۡ جَٰثِمِينَ

Sai girgizar qasa ta kama su, suka wayi gari a gidajensu gurfane a kan gwiwoyinsu (matattu)



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 92

ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ شُعَيۡبٗا كَأَن لَّمۡ يَغۡنَوۡاْ فِيهَاۚ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ شُعَيۡبٗا كَانُواْ هُمُ ٱلۡخَٰسِرِينَ

Waxanda suka qaryata Shu’aibu, kai ka ce ba su tava zama a cikinsu (gidajensu) ba, lalle waxanda suka qaryata Shu’aibu sun kasance su ne hasararru



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 93

فَتَوَلَّىٰ عَنۡهُمۡ وَقَالَ يَٰقَوۡمِ لَقَدۡ أَبۡلَغۡتُكُمۡ رِسَٰلَٰتِ رَبِّي وَنَصَحۡتُ لَكُمۡۖ فَكَيۡفَ ءَاسَىٰ عَلَىٰ قَوۡمٖ كَٰفِرِينَ

Sai ya juya ya bar su, kuma ya ce: “Ya ku mutanena, lalle haqiqa na isar muku da saqonnin Ubangijina, na kuma yi muku nasiha; to saboda me zan ji takaici a kan mutane kafirai?”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 84

۞وَإِلَىٰ مَدۡيَنَ أَخَاهُمۡ شُعَيۡبٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥۖ وَلَا تَنقُصُواْ ٱلۡمِكۡيَالَ وَٱلۡمِيزَانَۖ إِنِّيٓ أَرَىٰكُم بِخَيۡرٖ وَإِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٖ مُّحِيطٖ

Kuma Mun aiko wa (mutanen) Madyana xan’uwansu Shu’aibu, ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta ba shi ba, kada kuma ku tauye mudu da sikeli; lalle ni ina ganin ku da alheri (wato wadata), kuma lalle ni ina jiye muku tsoron azabar wata rana mai kewayewa



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 85

وَيَٰقَوۡمِ أَوۡفُواْ ٱلۡمِكۡيَالَ وَٱلۡمِيزَانَ بِٱلۡقِسۡطِۖ وَلَا تَبۡخَسُواْ ٱلنَّاسَ أَشۡيَآءَهُمۡ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

“Kuma ya ku mutanena, ku cika mudu da sikeli da adalci; kada kuwa ku tauye wa mutane abubuwansu, kada kuma ku yaxa varna a bayan qasa



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 86

بَقِيَّتُ ٱللَّهِ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَۚ وَمَآ أَنَا۠ عَلَيۡكُم بِحَفِيظٖ

“Abin da zai wanzu a gare ku na alheri a wurin Allah shi ya fi muku in kun kasance muminai. Ni kuma ba mai tsaron ku ba ne.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 87

قَالُواْ يَٰشُعَيۡبُ أَصَلَوٰتُكَ تَأۡمُرُكَ أَن نَّتۡرُكَ مَا يَعۡبُدُ ءَابَآؤُنَآ أَوۡ أَن نَّفۡعَلَ فِيٓ أَمۡوَٰلِنَا مَا نَشَـٰٓؤُاْۖ إِنَّكَ لَأَنتَ ٱلۡحَلِيمُ ٱلرَّشِيدُ

Suka ce: “Ya kai Shu’aibu, yanzu sallarka ce[1] take umartar ka da (ka sa) mu bar abin da iyayenmu suke bauta wa, kada kuma mu aikata abin da muka ga dama da dukiyoyinmu? Lalle tabbas kai ne mai haquri mai hankali!”


1- Annabi Shu’aibu mutum ne mai yawan salla har ya shahara da haka a tsakanin mutanensa.


Capítulo: Suratu Hud

Verso : 88

قَالَ يَٰقَوۡمِ أَرَءَيۡتُمۡ إِن كُنتُ عَلَىٰ بَيِّنَةٖ مِّن رَّبِّي وَرَزَقَنِي مِنۡهُ رِزۡقًا حَسَنٗاۚ وَمَآ أُرِيدُ أَنۡ أُخَالِفَكُمۡ إِلَىٰ مَآ أَنۡهَىٰكُمۡ عَنۡهُۚ إِنۡ أُرِيدُ إِلَّا ٱلۡإِصۡلَٰحَ مَا ٱسۡتَطَعۡتُۚ وَمَا تَوۡفِيقِيٓ إِلَّا بِٱللَّهِۚ عَلَيۡهِ تَوَكَّلۡتُ وَإِلَيۡهِ أُنِيبُ

Ya ce: “Ya ku mutanena, me kuke gani ne, idan na kasance a kan bayyananniyar hujja daga Ubangijina, Ya kuma arzuta ni da kyakkyawan arziki daga gare Shi. Ba na kuma nufin in aikata abin da nake hana ku aikata shi. Ba komai nake nufi ba sai gyara iyakacin ikona. Kuma dacewata daga Allah kaxai take. A gare Shi na dogara, kuma zuwa gare Shi ne zan koma



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 89

وَيَٰقَوۡمِ لَا يَجۡرِمَنَّكُمۡ شِقَاقِيٓ أَن يُصِيبَكُم مِّثۡلُ مَآ أَصَابَ قَوۡمَ نُوحٍ أَوۡ قَوۡمَ هُودٍ أَوۡ قَوۡمَ صَٰلِحٖۚ وَمَا قَوۡمُ لُوطٖ مِّنكُم بِبَعِيدٖ

“Kuma ya mutanena, kada sava mini ya jawo muku irin abin da ya sami mutanen Nuhu ko mutanen Hudu ko kuma mutanen Salihu, ku ma ya same ku. Mutanen Luxu kuwa ba nesa suke da ku ba



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 90

وَٱسۡتَغۡفِرُواْ رَبَّكُمۡ ثُمَّ تُوبُوٓاْ إِلَيۡهِۚ إِنَّ رَبِّي رَحِيمٞ وَدُودٞ

“Kuma ku nemi gafarar Ubangijinku, sannan ku tuba gare Shi. Lalle Ubangijina Mai yawan rahama ne Mai nuna qauna.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 91

قَالُواْ يَٰشُعَيۡبُ مَا نَفۡقَهُ كَثِيرٗا مِّمَّا تَقُولُ وَإِنَّا لَنَرَىٰكَ فِينَا ضَعِيفٗاۖ وَلَوۡلَا رَهۡطُكَ لَرَجَمۡنَٰكَۖ وَمَآ أَنتَ عَلَيۡنَا بِعَزِيزٖ

Suka ce: “Ya kai Shu’aibu, ba ma fahimtar da yawa daga abin da kake faxa; lalle kuma tabbas muna ganin ka rarrauna a cikinmu, kuma ba don danginka ba da mun jefe ka; ba kuwa za ka gagare mu ba.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 92

قَالَ يَٰقَوۡمِ أَرَهۡطِيٓ أَعَزُّ عَلَيۡكُم مِّنَ ٱللَّهِ وَٱتَّخَذۡتُمُوهُ وَرَآءَكُمۡ ظِهۡرِيًّاۖ إِنَّ رَبِّي بِمَا تَعۡمَلُونَ مُحِيطٞ

Ya ce: “Ya ku mutanena, yanzu dangin nawa ne suka fi Allah girma a wurinku, kuka kuma xauke shi abin jefarwa a can bayanku? Lalle Ubangijina a kewaye Yake da (sanin) abin da kuke aikatawa



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 93

وَيَٰقَوۡمِ ٱعۡمَلُواْ عَلَىٰ مَكَانَتِكُمۡ إِنِّي عَٰمِلٞۖ سَوۡفَ تَعۡلَمُونَ مَن يَأۡتِيهِ عَذَابٞ يُخۡزِيهِ وَمَنۡ هُوَ كَٰذِبٞۖ وَٱرۡتَقِبُوٓاْ إِنِّي مَعَكُمۡ رَقِيبٞ

“Kuma ya ku mutanena, ku yi aiki a kan irin hanyarku; ni ma lalle mai yin aiki ne (a kan tawa). Ba da daxewa ba za ku san wanda azaba mai wulakantawa za ta zo masa, da kuma wanda yake maqaryaci. Ku saurara, ni ma lalle mai sauraro ne tare da ku.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 94

وَلَمَّا جَآءَ أَمۡرُنَا نَجَّيۡنَا شُعَيۡبٗا وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ بِرَحۡمَةٖ مِّنَّا وَأَخَذَتِ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ ٱلصَّيۡحَةُ فَأَصۡبَحُواْ فِي دِيَٰرِهِمۡ جَٰثِمِينَ

Lokacin kuwa da umarninmu ya zo Muka tserar da Shu’aibu tare da waxanda suka yi imani da shi da wata rahama daga gare mu; tsawa kuma ta kama waxanda suka kafirta, sai suka wayi gari cikin gidajensu a duddurqushe, (ba rai)



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 95

كَأَن لَّمۡ يَغۡنَوۡاْ فِيهَآۗ أَلَا بُعۡدٗا لِّمَدۡيَنَ كَمَا بَعِدَتۡ ثَمُودُ

Kamar daxai ba su tava zama ba a cikinsu (gidajen) ba. Ku saurara; halaka ta tabbata ga (mutanen) Madyana kamar yadda Samudawa suka halaka



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 25

فَجَآءَتۡهُ إِحۡدَىٰهُمَا تَمۡشِي عَلَى ٱسۡتِحۡيَآءٖ قَالَتۡ إِنَّ أَبِي يَدۡعُوكَ لِيَجۡزِيَكَ أَجۡرَ مَا سَقَيۡتَ لَنَاۚ فَلَمَّا جَآءَهُۥ وَقَصَّ عَلَيۡهِ ٱلۡقَصَصَ قَالَ لَا تَخَفۡۖ نَجَوۡتَ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Sai xayarsu ta zo masa tana tafiya cikin jin kunya ta ce: “Babana yana kiran ka don ya saka maka ladan shayarwar da ka yi mana.” To lokacin da ya zo wurinsa ya kuma ba shi labarin(sa) sai ya ce da shi: “Kada ka ji tsoro, ka tsira daga azzaluman mutane.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 26

قَالَتۡ إِحۡدَىٰهُمَا يَـٰٓأَبَتِ ٱسۡتَـٔۡجِرۡهُۖ إِنَّ خَيۡرَ مَنِ ٱسۡتَـٔۡجَرۡتَ ٱلۡقَوِيُّ ٱلۡأَمِينُ

Sai xayarsu ta ce: “Babana, ka xauke shi aiki mana; don kuwa lalle ba wanda ya fi dacewa ka xauka aiki sai qaqqarfa, amintacce.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 27

قَالَ إِنِّيٓ أُرِيدُ أَنۡ أُنكِحَكَ إِحۡدَى ٱبۡنَتَيَّ هَٰتَيۡنِ عَلَىٰٓ أَن تَأۡجُرَنِي ثَمَٰنِيَ حِجَجٖۖ فَإِنۡ أَتۡمَمۡتَ عَشۡرٗا فَمِنۡ عِندِكَۖ وَمَآ أُرِيدُ أَنۡ أَشُقَّ عَلَيۡكَۚ سَتَجِدُنِيٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Sai ya ce da (Musa): “Ina so in aura maka xaya daga ‘ya’yayen nan nawa guda biyu, a kan ka yi min aiki na shekara takwas; to amma idan ka cika goma to wannan raxin kanka ne; ba na kuwa nufin in quntata maka. Za ka same ni kuwa in Allah Ya yarda daga cikin nagartattun mutane.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 28

قَالَ ذَٰلِكَ بَيۡنِي وَبَيۡنَكَۖ أَيَّمَا ٱلۡأَجَلَيۡنِ قَضَيۡتُ فَلَا عُدۡوَٰنَ عَلَيَّۖ وَٱللَّهُ عَلَىٰ مَا نَقُولُ وَكِيلٞ

(Musa) ya ce: “Wannan tsakanina da kai ne; kowanne xayan lokatan biyu na cika to kada a qware ni; Allah kuwa shaida ne game da abin da muke faxa.”



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 36

وَإِلَىٰ مَدۡيَنَ أَخَاهُمۡ شُعَيۡبٗا فَقَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ وَٱرۡجُواْ ٱلۡيَوۡمَ ٱلۡأٓخِرَ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

Mun kuma (aika wa mutanen) Madyana xan’uwansu Shu’aibu, sai ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, kuma ku yi fatan (kyakkyawan samakon) ranar lahira, kada kuma ku riqa yaxa varna a bayan qasa.”



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 37

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلرَّجۡفَةُ فَأَصۡبَحُواْ فِي دَارِهِمۡ جَٰثِمِينَ

Sai suka qaryata shi, sai girgizar qasa ta kama su, suka wayi gari duddurqushe (matattu) cikin gidajensu