Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 13

وَمَا ذَرَأَ لَكُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُخۡتَلِفًا أَلۡوَٰنُهُۥٓۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّقَوۡمٖ يَذَّكَّرُونَ

Da kuma abubuwan da Ya halitta muku a qasa masu launi iri daban-daban. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga mutanen da suke wa’azantuwa



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 65

وَٱللَّهُ أَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَحۡيَا بِهِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَآۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّقَوۡمٖ يَسۡمَعُونَ

Allah kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sai Ya raya qasa da shi bayan mutuwarta. Lalle a game da wannan akwai aya ga mutanen da suke ji



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 66

وَإِنَّ لَكُمۡ فِي ٱلۡأَنۡعَٰمِ لَعِبۡرَةٗۖ نُّسۡقِيكُم مِّمَّا فِي بُطُونِهِۦ مِنۢ بَيۡنِ فَرۡثٖ وَدَمٖ لَّبَنًا خَالِصٗا سَآئِغٗا لِّلشَّـٰرِبِينَ

Lalle kuma kuna da wata izina a game da dabbobin ni’ima; Muna shayar da ku da abin da yake cikin cikkunansu (mai fitowa) ta tsakankanin uwar hanji da jinni; nono tatacce mai daxin kwankwaxa ga masu sha



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 67

وَمِن ثَمَرَٰتِ ٱلنَّخِيلِ وَٱلۡأَعۡنَٰبِ تَتَّخِذُونَ مِنۡهُ سَكَرٗا وَرِزۡقًا حَسَنًاۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّقَوۡمٖ يَعۡقِلُونَ

Daga kuma ‘ya’yan dabinai da na inabai kuna yin giya da shi[1], da kuma arziki mai kyau. Lalle a game da wannan akwai aya ga mutanen da suke hankalta


1- Wannan ayar ta sauka kafin a haramta shan giya. Daga baya Allah () ya haramta duk wani abu mai gusar da hankali.


Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 68

وَأَوۡحَىٰ رَبُّكَ إِلَى ٱلنَّحۡلِ أَنِ ٱتَّخِذِي مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتٗا وَمِنَ ٱلشَّجَرِ وَمِمَّا يَعۡرِشُونَ

Ubangijinka kuma Ya kimsa wa qudan zuma cewa,: “Ki gina gidaje a duwatsu da kan bishiyoyi da kuma rufin da (mutane) suke yi”



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 69

ثُمَّ كُلِي مِن كُلِّ ٱلثَّمَرَٰتِ فَٱسۡلُكِي سُبُلَ رَبِّكِ ذُلُلٗاۚ يَخۡرُجُ مِنۢ بُطُونِهَا شَرَابٞ مُّخۡتَلِفٌ أَلۡوَٰنُهُۥ فِيهِ شِفَآءٞ لِّلنَّاسِۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّقَوۡمٖ يَتَفَكَّرُونَ

“Sannan kuma ki ci daga kowanne ‘ya’yan itace, kuma ki shiga hanyoyin Ubangijinki horarru (gare ki).” Abin sha mai launi daban-daban yana fitowa daga cikin cikinta; a cikinsa (kuma) da akwai waraka ga mutane. Lalle a game da wannan akwai aya ga mutane masu tunani



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 79

أَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَى ٱلطَّيۡرِ مُسَخَّرَٰتٖ فِي جَوِّ ٱلسَّمَآءِ مَا يُمۡسِكُهُنَّ إِلَّا ٱللَّهُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

Yanzu ba sa ganin tsuntsaye da aka lamunce wa (tashi) a sararin sama, ba mai riqe su sai Allah? Lalle a game da wannan akwai ayoyi ga mutane masu yin imani



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 12

وَجَعَلۡنَا ٱلَّيۡلَ وَٱلنَّهَارَ ءَايَتَيۡنِۖ فَمَحَوۡنَآ ءَايَةَ ٱلَّيۡلِ وَجَعَلۡنَآ ءَايَةَ ٱلنَّهَارِ مُبۡصِرَةٗ لِّتَبۡتَغُواْ فَضۡلٗا مِّن رَّبِّكُمۡ وَلِتَعۡلَمُواْ عَدَدَ ٱلسِّنِينَ وَٱلۡحِسَابَۚ وَكُلَّ شَيۡءٖ فَصَّلۡنَٰهُ تَفۡصِيلٗا

Muka kuma sanya dare da rana su zama ayoyi guda biyu; sai Muka shafe ayar dare (ta zama duhu) Muka kuma sanya ayar rana ta zama mai haskakawa, don ku nemi falala daga Ubangijinku, don kuma ku san yawan shekaru da lissafi. Kowane abu kuwa Mun rarrabe shi filla-filla



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 101

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَىٰ تِسۡعَ ءَايَٰتِۭ بَيِّنَٰتٖۖ فَسۡـَٔلۡ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ إِذۡ جَآءَهُمۡ فَقَالَ لَهُۥ فِرۡعَوۡنُ إِنِّي لَأَظُنُّكَ يَٰمُوسَىٰ مَسۡحُورٗا

Kuma haqiqa Mun bai wa Musa ayoyi tara bayyanannu; to ka tambayi Banu Isra’ila lokacin da ya zo musu, sai Fir’auna ya ce da shi: “Lalle ni fa ina tsammanin kai Musa sihirtacce ne!”



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 102

قَالَ لَقَدۡ عَلِمۡتَ مَآ أَنزَلَ هَـٰٓؤُلَآءِ إِلَّا رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ بَصَآئِرَ وَإِنِّي لَأَظُنُّكَ يَٰفِرۡعَوۡنُ مَثۡبُورٗا

(Musa) ya ce: “Haqiqa ka sani ba wanda ya saukar da waxannan (ayoyin) sai Ubangijin sammai da qasa don su zama hujjoji, kuma lalle ina tsammanin kai Fir’auna halakakke ne.”



Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 17

۞وَتَرَى ٱلشَّمۡسَ إِذَا طَلَعَت تَّزَٰوَرُ عَن كَهۡفِهِمۡ ذَاتَ ٱلۡيَمِينِ وَإِذَا غَرَبَت تَّقۡرِضُهُمۡ ذَاتَ ٱلشِّمَالِ وَهُمۡ فِي فَجۡوَةٖ مِّنۡهُۚ ذَٰلِكَ مِنۡ ءَايَٰتِ ٱللَّهِۗ مَن يَهۡدِ ٱللَّهُ فَهُوَ ٱلۡمُهۡتَدِۖ وَمَن يُضۡلِلۡ فَلَن تَجِدَ لَهُۥ وَلِيّٗا مُّرۡشِدٗا

(Sai) kuma ka ga rana idan za ta vullo tana kauce wa kogonsu ta vangaren dama, idan kuma za ta faxi sai ta riqa kauce musu ta vangaren hagu, su kuwa suna tsakiyarsa. Wannan yana daga ayoyin Allah. Wanda Allah Ya shiryar to shi ne shiryayye, wanda kuwa Ya vatar to ba za ka sami wani majivinci da zai shirye shi ba



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 10

قَالَ رَبِّ ٱجۡعَل لِّيٓ ءَايَةٗۖ قَالَ ءَايَتُكَ أَلَّا تُكَلِّمَ ٱلنَّاسَ ثَلَٰثَ لَيَالٖ سَوِيّٗا

Ya ce: “Ubangijina Ka sanya mini wata alama.” Sai (Allah) Ya ce: “Alamarka ita ce ka kasa yi wa mutane magana (tsawon) kwana uku daidai.”



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 20

قَالَتۡ أَنَّىٰ يَكُونُ لِي غُلَٰمٞ وَلَمۡ يَمۡسَسۡنِي بَشَرٞ وَلَمۡ أَكُ بَغِيّٗا

Ta ce: “Ta qaqa zan samu xa, alhalin kuwa wani namiji bai tava shafa ta ba, kuma ni ban zamanto mazinaciya ba?”



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 21

قَالَ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِ هُوَ عَلَيَّ هَيِّنٞۖ وَلِنَجۡعَلَهُۥٓ ءَايَةٗ لِّلنَّاسِ وَرَحۡمَةٗ مِّنَّاۚ وَكَانَ أَمۡرٗا مَّقۡضِيّٗا

(Mala’ika) ya ce: “Kamar haka ne Ubangijinki Ya faxa (cewa): “Shi (wannan) mai sauqi ne a wurina, kuma don Mu mayar da shi aya ga mutane da kuma rahama daga gare Mu, kuma (yin haka) ya zamanto al’amari ne tabbatacce (rubuce a Lauhul-Mahafuzu).”



Capítulo: Suratu Xa Ha

Verso : 53

ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ مَهۡدٗا وَسَلَكَ لَكُمۡ فِيهَا سُبُلٗا وَأَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَخۡرَجۡنَا بِهِۦٓ أَزۡوَٰجٗا مِّن نَّبَاتٖ شَتَّىٰ

“(Shi ne) Wanda Ya sanya muku qasa a shimfixe, Ya kuma sanya muku hanyoyi na tafiya cikinta, kuma Ya saukar da ruwa daga sama”, sannan Muka fitar da dangogin shuke-shuke iri-iri da shi (ruwa)



Capítulo: Suratu Xa Ha

Verso : 54

كُلُواْ وَٱرۡعَوۡاْ أَنۡعَٰمَكُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّأُوْلِي ٱلنُّهَىٰ

Ku ci (daga tsirran) kuma ku yi kiwon dabbobinku. Lalle a game da wannan akwai ayoyi ga ma’abota hankula



Capítulo: Suratu Xa Ha

Verso : 128

أَفَلَمۡ يَهۡدِ لَهُمۡ كَمۡ أَهۡلَكۡنَا قَبۡلَهُم مِّنَ ٱلۡقُرُونِ يَمۡشُونَ فِي مَسَٰكِنِهِمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّأُوْلِي ٱلنُّهَىٰ

Yanzu (mutanen Makka) ba su gane cewa al’ummu nawa muka hallaka a gabaninsu ba waxanda suna wucewa ta gidajensu? Lalle a game da wannan akwai ayoyi ga ma’abota hankali



Capítulo: Suratul Anbiya

Verso : 91

وَٱلَّتِيٓ أَحۡصَنَتۡ فَرۡجَهَا فَنَفَخۡنَا فِيهَا مِن رُّوحِنَا وَجَعَلۡنَٰهَا وَٱبۡنَهَآ ءَايَةٗ لِّلۡعَٰلَمِينَ

(Ka tuna) kuma wadda ta tsare matancinta, sai Muka yi busa a cikinta daga Ruhinmu, Muka kuma sanya ta ita da xanta aya ga talikai



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 27

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡهِ أَنِ ٱصۡنَعِ ٱلۡفُلۡكَ بِأَعۡيُنِنَا وَوَحۡيِنَا فَإِذَا جَآءَ أَمۡرُنَا وَفَارَ ٱلتَّنُّورُ فَٱسۡلُكۡ فِيهَا مِن كُلّٖ زَوۡجَيۡنِ ٱثۡنَيۡنِ وَأَهۡلَكَ إِلَّا مَن سَبَقَ عَلَيۡهِ ٱلۡقَوۡلُ مِنۡهُمۡۖ وَلَا تُخَٰطِبۡنِي فِي ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ إِنَّهُم مُّغۡرَقُونَ

Sai Muka yiwo masa wahayi cewa: “Ka sassaqa jirgin ruwa a qarqashin kulawarmu da umarninmu, sannan idan umarninmu (na hallaka su) ya zo, kuma tanderu ya vuvvugo da ruwa, sai ka saka ma’aurata guda biyu daga kowane jinsi a cikinsa, da kuma iyalanka, sai wanda kalmar (halaka) ta rigaya a kansa daga cikinsu; kuma kada ka ce min komai game da waxanda suka kafirta; lalle su waxanda za a nutsar ne



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 28

فَإِذَا ٱسۡتَوَيۡتَ أَنتَ وَمَن مَّعَكَ عَلَى ٱلۡفُلۡكِ فَقُلِ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي نَجَّىٰنَا مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

“To idan kai da waxanda suke tare da kai kuka daidaita a kan jirgin, sai ka ce: “Na gode wa Allah wanda Ya tserar da mu daga mutane azzalumai.”



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 29

وَقُل رَّبِّ أَنزِلۡنِي مُنزَلٗا مُّبَارَكٗا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلۡمُنزِلِينَ

Kuma ka ce: “Ubangijina Ka saukar da ni masauki mai albarka, Kai ne kuwa Fiyayyen masu saukarwa.”



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 30

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ وَإِن كُنَّا لَمُبۡتَلِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi, Mu kuma haqiqa Mun kasance Masu jarrabawa ne



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 50

وَجَعَلۡنَا ٱبۡنَ مَرۡيَمَ وَأُمَّهُۥٓ ءَايَةٗ وَءَاوَيۡنَٰهُمَآ إِلَىٰ رَبۡوَةٖ ذَاتِ قَرَارٖ وَمَعِينٖ

Muka kuma sanya Xan Maryamu da mahaifiyarsa (don su zama) aya, Muka kuma zaunar da su a wata jigawa ta hutawa da kuma ruwa mai gudana



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 4

إِن نَّشَأۡ نُنَزِّلۡ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةٗ فَظَلَّتۡ أَعۡنَٰقُهُمۡ لَهَا خَٰضِعِينَ

Da Mun ga dama da sai Mu saukar musu da aya daga sama sai wuyoyinsu su zamo masu qanqan da kai gare ta[1]


1- Watau mu’ujizar da za ta tilasta musu su miqa wuya ko ba sa so.


Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 7

أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَمۡ أَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجٖ كَرِيمٍ

Shin ba su yi duba zuwa ga qasa ba, (su ga) dangogin tsirrai masu kyau nawa ne Muka tsirar daga cikinta?



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 8

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya (mai nuna cikar ikon Allah); kuma yawancinsu ba su zamanto masu imani ba



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 63

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡبَحۡرَۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرۡقٖ كَٱلطَّوۡدِ ٱلۡعَظِيمِ

Sai Muka yi wahayi ga Musa cewa: “Ka bugi kogin da sandarka;” (da ya buge shi) sai ya dare, kowanne yanki sai ya zama kamar qaton dutse



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 64

وَأَزۡلَفۡنَا ثَمَّ ٱلۡأٓخَرِينَ

Muka kuma kusantar da waxancan (watau mutanen Fir’auna) zuwa can (kusa da kogin)



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 65

وَأَنجَيۡنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

Muka kuma tserar da Musa da waxanda suke tare da shi gaba xaya



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 66

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka nutsar da sauran mutanen (watau Fir’auna da mutanensa)