Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 147

ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّكَ فَلَا تَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمُمۡتَرِينَ

Gaskiya kam daga Ubangijinka take, don haka lalle kada ka zama daga cikin masu shakka



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 213

كَانَ ٱلنَّاسُ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ فَبَعَثَ ٱللَّهُ ٱلنَّبِيِّـۧنَ مُبَشِّرِينَ وَمُنذِرِينَ وَأَنزَلَ مَعَهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ لِيَحۡكُمَ بَيۡنَ ٱلنَّاسِ فِيمَا ٱخۡتَلَفُواْ فِيهِۚ وَمَا ٱخۡتَلَفَ فِيهِ إِلَّا ٱلَّذِينَ أُوتُوهُ مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡهُمُ ٱلۡبَيِّنَٰتُ بَغۡيَۢا بَيۡنَهُمۡۖ فَهَدَى ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لِمَا ٱخۡتَلَفُواْ فِيهِ مِنَ ٱلۡحَقِّ بِإِذۡنِهِۦۗ وَٱللَّهُ يَهۡدِي مَن يَشَآءُ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٍ

Mutane sun kasance al’umma guda xaya, sai Allah Ya aiko da annabawa, suna masu albishir, kuma masu gargaxi, kuma Ya saukar da littafi tare da su da gaskiya, don ya yi hukunci tsakanin mutane cikin abin da suka yi savani a kansa. Kuma ba wasu ne suka yi savani a kansa ba sai waxanda aka ba wa shi, bayan hujjoji bayyanannu sun zo musu, don zalunci a tsakaninsu; sai Allah Ya shiryar da waxanda suka yi imani ga abin da (mutane) suka yi savani cikinsa na gaskiya da izininsa. Kuma Allah Yana shiryar da wanda Ya ga dama zuwa ga tafarki madaidaici



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 3

نَزَّلَ عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِ وَأَنزَلَ ٱلتَّوۡرَىٰةَ وَٱلۡإِنجِيلَ

Ya saukar maka da Littafi da gaskiya, yana mai gaskata abin da ya gabace shi, kuma Ya saukar da Attaura da Linjila



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 71

يَـٰٓأَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ لِمَ تَلۡبِسُونَ ٱلۡحَقَّ بِٱلۡبَٰطِلِ وَتَكۡتُمُونَ ٱلۡحَقَّ وَأَنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Ya ku Ma’abota Littafi, don me kuke cakuxa gaskiya da qarya, kuma kuke voye gaskiya, alhalin ku kuna sane?



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 108

تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱللَّهِ نَتۡلُوهَا عَلَيۡكَ بِٱلۡحَقِّۗ وَمَا ٱللَّهُ يُرِيدُ ظُلۡمٗا لِّلۡعَٰلَمِينَ

Waxannan ayoyin Allah ne Muke karanta maka su da gaskiya. Kuma Allah ba Ya nufin zalunci ga talikai



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 105

إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ لِتَحۡكُمَ بَيۡنَ ٱلنَّاسِ بِمَآ أَرَىٰكَ ٱللَّهُۚ وَلَا تَكُن لِّلۡخَآئِنِينَ خَصِيمٗا

Lalle Mu Mun saukar maka da Littafi da gaskiya domin ka yi hukunci a tsakanin mutane da abin da Allah Ya sanar da kai, kuma kada ka zamo mai ba da kariya ga maha’inta



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 122

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ سَنُدۡخِلُهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٗاۚ وَمَنۡ أَصۡدَقُ مِنَ ٱللَّهِ قِيلٗا

Kuma waxanda suka yi imani, kuma suka yi aiki nagari, za Mu shigar da su gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dawwama a cikinsu har abada; kuma alqawarin Allah tabbatacce ne. Kuma wane ne ya fi Allah gaskiyar zance?



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 170

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ قَدۡ جَآءَكُمُ ٱلرَّسُولُ بِٱلۡحَقِّ مِن رَّبِّكُمۡ فَـَٔامِنُواْ خَيۡرٗا لَّكُمۡۚ وَإِن تَكۡفُرُواْ فَإِنَّ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Ya ku mutane, haqiqa Manzo ya zo muku da gaskiya daga wajen Ubangijinku, don haka ku yi imani shi ya fi alheri a gare ku. Idan kuwa kuka kafirce, to lalle abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa duk na Allah ne. kuma Allah Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 48

وَأَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِ مِنَ ٱلۡكِتَٰبِ وَمُهَيۡمِنًا عَلَيۡهِۖ فَٱحۡكُم بَيۡنَهُم بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُۖ وَلَا تَتَّبِعۡ أَهۡوَآءَهُمۡ عَمَّا جَآءَكَ مِنَ ٱلۡحَقِّۚ لِكُلّٖ جَعَلۡنَا مِنكُمۡ شِرۡعَةٗ وَمِنۡهَاجٗاۚ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَجَعَلَكُمۡ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ وَلَٰكِن لِّيَبۡلُوَكُمۡ فِي مَآ ءَاتَىٰكُمۡۖ فَٱسۡتَبِقُواْ ٱلۡخَيۡرَٰتِۚ إِلَى ٱللَّهِ مَرۡجِعُكُمۡ جَمِيعٗا فَيُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ فِيهِ تَخۡتَلِفُونَ

Kuma Mun saukar maka da Littafin (Alqur’ani) da gaskiya, yana mai gaskata abin da ya gabace shi na sauran littattafai, kuma mai xaukaka a kansu; don haka ka yi hukunci a tsakaninsu da abin da Allah Ya saukar; kuma kada ka bi soye-soyen zukatansu ka bar abin da ya zo maka na gaskiya don bin son zuciyarsu. Kowanne daga cikinku Mun sanya musu tsari na shari’a da tsari na rayuwa. Kuma in da Allah Ya ga dama, da sai Ya sanya ku ku zamo al’umma xaya, sai dai kuma don Ya jarrabe ku cikin abin da Ya ba ku; don haka sai ku yi gaggawar aikata ayyuka na alheri. Gaba xaya makomarku zuwa ga Allah take, kuma zai ba ku labarin abin da kuka kasance kuna savani a kansa



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 83

وَإِذَا سَمِعُواْ مَآ أُنزِلَ إِلَى ٱلرَّسُولِ تَرَىٰٓ أَعۡيُنَهُمۡ تَفِيضُ مِنَ ٱلدَّمۡعِ مِمَّا عَرَفُواْ مِنَ ٱلۡحَقِّۖ يَقُولُونَ رَبَّنَآ ءَامَنَّا فَٱكۡتُبۡنَا مَعَ ٱلشَّـٰهِدِينَ

Kuma idan sun ji abin da aka saukar wa wannan Manzo, za ka ga idanunsu suna zubar da hawaye, saboda abin da suka gane na gaskiya; suna cewa: “Ya Ubangijinmu, mun yi imani, don haka Ka rubuta mu cikin masu shaidawa



Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 84

وَمَا لَنَا لَا نُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَمَا جَآءَنَا مِنَ ٱلۡحَقِّ وَنَطۡمَعُ أَن يُدۡخِلَنَا رَبُّنَا مَعَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلصَّـٰلِحِينَ

“Kuma me muke da shi da ba za mu yi imani da Allah da abin da ya zo mana na gaskiya ba, muna kuwa sa rai Ubangijinmu Ya shigar da mu cikin salihan bayi?”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 73

وَهُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۖ وَيَوۡمَ يَقُولُ كُن فَيَكُونُۚ قَوۡلُهُ ٱلۡحَقُّۚ وَلَهُ ٱلۡمُلۡكُ يَوۡمَ يُنفَخُ فِي ٱلصُّورِۚ عَٰلِمُ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِۚ وَهُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡخَبِيرُ

“Kuma Shi ne Wanda ya halicci sammai da qasa da gaskiya; kuma (ku tuna) ranar da zai ce da abu: ‘Kasance!’ Nan take sai ya kasance. Maganarsa gaskiya ce. Kuma Shi ne Yake da cikakken mulki a ranar da za a busa qaho Masanin gaibu da sarari, kuma Shi ne Mai hikima, Mai cikakken sani.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 181

وَمِمَّنۡ خَلَقۡنَآ أُمَّةٞ يَهۡدُونَ بِٱلۡحَقِّ وَبِهِۦ يَعۡدِلُونَ

Kuma akwai wata al’umma daga cikin waxanda Muka halitta suna shiryarwa da gaskiya, kuma da ita suke adalci



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 32

يُرِيدُونَ أَن يُطۡفِـُٔواْ نُورَ ٱللَّهِ بِأَفۡوَٰهِهِمۡ وَيَأۡبَى ٱللَّهُ إِلَّآ أَن يُتِمَّ نُورَهُۥ وَلَوۡ كَرِهَ ٱلۡكَٰفِرُونَ

Suna nufi ne su dushashe hasken Allah da bakunansu, Allah kuwa ba zai qyale ba har sai Ya cika haskensa ko da kuwa kafirai sun qi



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 33

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَرۡسَلَ رَسُولَهُۥ بِٱلۡهُدَىٰ وَدِينِ ٱلۡحَقِّ لِيُظۡهِرَهُۥ عَلَى ٱلدِّينِ كُلِّهِۦ وَلَوۡ كَرِهَ ٱلۡمُشۡرِكُونَ

Shi ne wanda Ya aiko Manzonsa da shiriya da kuma addini na gaskiya don Ya xora shi a kan dukkanin addinai, ko da kuwa mushrikai sun qi



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 4

إِلَيۡهِ مَرۡجِعُكُمۡ جَمِيعٗاۖ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقًّاۚ إِنَّهُۥ يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥ لِيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ بِٱلۡقِسۡطِۚ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَهُمۡ شَرَابٞ مِّنۡ حَمِيمٖ وَعَذَابٌ أَلِيمُۢ بِمَا كَانُواْ يَكۡفُرُونَ

Zuwa gare Shi ne makomarku take gaba xaya; alqawarin Allah ne da gaske. Lalle Shi ne Yake farar da halitta sannan Ya maido da ita (bayan mutuwa) don Ya saka wa waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki nagari da adalci. Waxanda suka kafirce kuwa suna da abin sha mai tsananin quna da kuma azaba mai raxaxi saboda kafircewa da suke yi



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 5

هُوَ ٱلَّذِي جَعَلَ ٱلشَّمۡسَ ضِيَآءٗ وَٱلۡقَمَرَ نُورٗا وَقَدَّرَهُۥ مَنَازِلَ لِتَعۡلَمُواْ عَدَدَ ٱلسِّنِينَ وَٱلۡحِسَابَۚ مَا خَلَقَ ٱللَّهُ ذَٰلِكَ إِلَّا بِٱلۡحَقِّۚ يُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ لِقَوۡمٖ يَعۡلَمُونَ

Shi ne Wanda Ya sanya muku rana ta zamo mai haske da kuma wata ya zamo mai haskakawa, Ya kuma sanya shi mai masaukai don ku san adadin shekaru da kuma (sanin) lissafi (na lokuta). Allah bai halicci wannan ba sai da gaskiya. Yana bayyana ayoyi ne ga mutanen da suke da sani



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 23

فَلَمَّآ أَنجَىٰهُمۡ إِذَا هُمۡ يَبۡغُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ بِغَيۡرِ ٱلۡحَقِّۗ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ إِنَّمَا بَغۡيُكُمۡ عَلَىٰٓ أَنفُسِكُمۖ مَّتَٰعَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ ثُمَّ إِلَيۡنَا مَرۡجِعُكُمۡ فَنُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

To lokacin da Ya tserar da su sai ga su suna varna a bayan qasa ba da gaskiya ba. Ya ku mutane, haqiqa (sakamakon) varnarku a kanku kawai yake; ku xan ji daxin rayuwar duniya; sannan (daga qarshe) zuwa gare Mu ne makomarku take, sannan mu ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 35

قُلۡ هَلۡ مِن شُرَكَآئِكُم مَّن يَهۡدِيٓ إِلَى ٱلۡحَقِّۚ قُلِ ٱللَّهُ يَهۡدِي لِلۡحَقِّۗ أَفَمَن يَهۡدِيٓ إِلَى ٱلۡحَقِّ أَحَقُّ أَن يُتَّبَعَ أَمَّن لَّا يَهِدِّيٓ إِلَّآ أَن يُهۡدَىٰۖ فَمَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ

Ka ce: “Shin daga abokan tarayyarku ko akwai wanda yake shiryarwa zuwa gaskiya?” Ka ce: “Allah Shi ne Yake shiryarwa zuwa ga gaskiya. To yanzu wanda yake shiryarwa zuwa gaskiya shi ya fi cancanta a bi, ko kuwa wanda ba ya shiryarwa sai dai a shiryar da shi? To me ya same ku ne? Yaya kuke wannan hukuncin?



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 36

وَمَا يَتَّبِعُ أَكۡثَرُهُمۡ إِلَّا ظَنًّاۚ إِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـًٔاۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِمَا يَفۡعَلُونَ

Yawancinsu kuma ba abin da suke bi sai zato. Lalle zato ba ya wadatar da komai game da gaskiya. Lalle Allah Masanin abin da suke aikatawa ne



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 53

۞وَيَسۡتَنۢبِـُٔونَكَ أَحَقٌّ هُوَۖ قُلۡ إِي وَرَبِّيٓ إِنَّهُۥ لَحَقّٞۖ وَمَآ أَنتُم بِمُعۡجِزِينَ

Suna kuma tambayar ka cewa: “Yanzu (batun azabar nan) gaskiya ne kuwa?” Ka ce: “I mana, na ko ranste da Allah lalle shi gaskiya ne; ba kuma za ku kuvuce ba.”



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 55

أَلَآ إِنَّ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۗ أَلَآ إِنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

A saurara, lalle duk abin da yake sammai da qasa na Allah ne. A saurara, lalle alqwarin Allah gaskiya ne, sai dai kuma yawancin mutane ba su sani ba



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 94

فَإِن كُنتَ فِي شَكّٖ مِّمَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ فَسۡـَٔلِ ٱلَّذِينَ يَقۡرَءُونَ ٱلۡكِتَٰبَ مِن قَبۡلِكَۚ لَقَدۡ جَآءَكَ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّكَ فَلَا تَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمُمۡتَرِينَ

To idan kana tababa[1] game da abin da Muka saukar maka to sai ka tambayi waxanda suke karanta littafi gabaninka. Haqiqa gaskiya ta zo maka daga Ubangijinka; to kada ka zama daga cikin masu kokwanto


1- Annabi () ba tava yin tababa ba game da wahayin da Allah () ya yi masa, amma abin nufi a nan shi ne kafa hujja ga Ahlulkitab a kan gaskiyar Annabi ().


Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 108

قُلۡ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ قَدۡ جَآءَكُمُ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّكُمۡۖ فَمَنِ ٱهۡتَدَىٰ فَإِنَّمَا يَهۡتَدِي لِنَفۡسِهِۦۖ وَمَن ضَلَّ فَإِنَّمَا يَضِلُّ عَلَيۡهَاۖ وَمَآ أَنَا۠ عَلَيۡكُم بِوَكِيلٖ

Ka ce: “Ya ku mutane, haqiqa gaskiya ta zo muku daga Ubangijinku; duk wanda ya shiriya to ya shiriya ne don kansa; wanda kuma ya vace to lalle ya vace don kansa ne; ni kuwa ba wakili ne a kanku ba.”



Capítulo: Suratu Hud

Verso : 120

وَكُلّٗا نَّقُصُّ عَلَيۡكَ مِنۡ أَنۢبَآءِ ٱلرُّسُلِ مَا نُثَبِّتُ بِهِۦ فُؤَادَكَۚ وَجَآءَكَ فِي هَٰذِهِ ٱلۡحَقُّ وَمَوۡعِظَةٞ وَذِكۡرَىٰ لِلۡمُؤۡمِنِينَ

Muna labarta maka kowanne daga labarun manzanni, abin da za Mu kwantar da zuciyarka da shi. Gaskiya kuwa ta zo maka cikin wannan (Surar) da izina da gargaxi ga muminai



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 1

الٓمٓرۚ تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِۗ وَٱلَّذِيٓ أُنزِلَ إِلَيۡكَ مِن رَّبِّكَ ٱلۡحَقُّ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يُؤۡمِنُونَ

ALIF LAM MIM RA[1]. Waxannan ayoyi ne na Littafi (wato Alqur’ani). Wanda kuma aka saukar maka daga Ubangijinka gaskiya ne, sai dai lalle yawancin mutane ba sa yin imani


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 17

أَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَسَالَتۡ أَوۡدِيَةُۢ بِقَدَرِهَا فَٱحۡتَمَلَ ٱلسَّيۡلُ زَبَدٗا رَّابِيٗاۖ وَمِمَّا يُوقِدُونَ عَلَيۡهِ فِي ٱلنَّارِ ٱبۡتِغَآءَ حِلۡيَةٍ أَوۡ مَتَٰعٖ زَبَدٞ مِّثۡلُهُۥۚ كَذَٰلِكَ يَضۡرِبُ ٱللَّهُ ٱلۡحَقَّ وَٱلۡبَٰطِلَۚ فَأَمَّا ٱلزَّبَدُ فَيَذۡهَبُ جُفَآءٗۖ وَأَمَّا مَا يَنفَعُ ٱلنَّاسَ فَيَمۡكُثُ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ كَذَٰلِكَ يَضۡرِبُ ٱللَّهُ ٱلۡأَمۡثَالَ

Ya saukar da ruwa daga sama, sai magudanai suka kwarara daidai gwargwadon abin da za su iya xauka, sai (shi ruwan) mai kwarara ya xauko kumfa a samansa. Akwai kuma wata kumfar kamarta daga abin da kuke narkawa a wuta don samun abin ado ko kuwa (qera) abin jin daxi. Kamar haka ne Allah Yake ba da misalin gaskiya da varna. To amma kumfar sai ta tafi ta bi iska; amma kuma abin da zai amfani mutane sai ya zauna a qasa. Kamar haka ne Allah Yake ba da misali



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 8

مَا نُنَزِّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ إِلَّا بِٱلۡحَقِّ وَمَا كَانُوٓاْ إِذٗا مُّنظَرِينَ

(Allah ya ce): “Ba ma saukar da mala’iku sai da gaskiya[1]; inda kuwa haka ya faru, to ba za a saurara musu ba.”


1- Watau sai idan lokacin da za a hallaka su ya zo.


Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 85

وَمَا خَلَقۡنَا ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَآ إِلَّا بِٱلۡحَقِّۗ وَإِنَّ ٱلسَّاعَةَ لَأٓتِيَةٞۖ فَٱصۡفَحِ ٱلصَّفۡحَ ٱلۡجَمِيلَ

Ba Mu kuma halicci sammai da qasa ba sai da gaskiya. Kuma lalle alqiyama tabbas mai zuwa ce, sai ka yi afuwa kyakkyawar afuwa[1]


1- Watau afuwar da babu cutarwa a cikinta sai dai kyautatawa ga wanda ya munana.


Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 3

خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۚ تَعَٰلَىٰ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Ya halicci sammai da qasa da gaskiya. Ya xaukaka daga abin da suke tara (Shi da shi)