Capítulo: Suratun Nur

Verso : 31

وَقُل لِّلۡمُؤۡمِنَٰتِ يَغۡضُضۡنَ مِنۡ أَبۡصَٰرِهِنَّ وَيَحۡفَظۡنَ فُرُوجَهُنَّ وَلَا يُبۡدِينَ زِينَتَهُنَّ إِلَّا مَا ظَهَرَ مِنۡهَاۖ وَلۡيَضۡرِبۡنَ بِخُمُرِهِنَّ عَلَىٰ جُيُوبِهِنَّۖ وَلَا يُبۡدِينَ زِينَتَهُنَّ إِلَّا لِبُعُولَتِهِنَّ أَوۡ ءَابَآئِهِنَّ أَوۡ ءَابَآءِ بُعُولَتِهِنَّ أَوۡ أَبۡنَآئِهِنَّ أَوۡ أَبۡنَآءِ بُعُولَتِهِنَّ أَوۡ إِخۡوَٰنِهِنَّ أَوۡ بَنِيٓ إِخۡوَٰنِهِنَّ أَوۡ بَنِيٓ أَخَوَٰتِهِنَّ أَوۡ نِسَآئِهِنَّ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُنَّ أَوِ ٱلتَّـٰبِعِينَ غَيۡرِ أُوْلِي ٱلۡإِرۡبَةِ مِنَ ٱلرِّجَالِ أَوِ ٱلطِّفۡلِ ٱلَّذِينَ لَمۡ يَظۡهَرُواْ عَلَىٰ عَوۡرَٰتِ ٱلنِّسَآءِۖ وَلَا يَضۡرِبۡنَ بِأَرۡجُلِهِنَّ لِيُعۡلَمَ مَا يُخۡفِينَ مِن زِينَتِهِنَّۚ وَتُوبُوٓاْ إِلَى ٱللَّهِ جَمِيعًا أَيُّهَ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ

Kuma ka ce da muminai mata su kame idanuwansu[1] kuma su kiyaye farjinsu, kada kuma su fito da adonsu sai dai abin da ya bayyana daga gare shi[2]; kuma su sanya lulluvinsu a kan wuyan rigunansu[3]; kada kuma su fitar da adonsu sai ga mazajensu ko iyayensu ko iyayen mazajensu ko ‘ya’yansu ko ‘ya’yayen mazajensu ko ‘yan’uwansu maza ko kuma ‘ya’yan ‘yan’uwansu maza ko ‘ya’yan ‘yan’uwansu mata ko kuma mata ‘yan’uwansu ko kuma bayinsu ko kuma mazaje masu bin su (don neman abinci) ba kuma masu buqatar mata ba[4], ko kuma qananan yara waxanda ba su san sha’awar al’aurar mata ba; kada kuma su buga qafafuwansu don a gane abin da suka voye na adon qafafunsu (watau mundaye). Kuma ku tuba ga Allah gaba xayanku ya ku waxannan muminai don ku rabauta


1- Watau su kawar da idanuwansu daga kallon abin da bai halatta su kalla ba.


2- Watau abin da ba za a iya voye shi ba, kamar tufafi.


3- Watau domin a daina ganin gashinsu da wuyansu da adonsu na wuya.


4- Watau tsofaffi tukub waxanda sun daina sha’awar mata gaba xaya.


Capítulo: Suratun Nur

Verso : 32

وَأَنكِحُواْ ٱلۡأَيَٰمَىٰ مِنكُمۡ وَٱلصَّـٰلِحِينَ مِنۡ عِبَادِكُمۡ وَإِمَآئِكُمۡۚ إِن يَكُونُواْ فُقَرَآءَ يُغۡنِهِمُ ٱللَّهُ مِن فَضۡلِهِۦۗ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٞ

Kuma ku aurar da marasa aure daga cikinku da kuma na gari daga bayinku da kuyanginku. Idan sun zamanto matalauta to Allah zai wadata su daga falalarsa. Allah kuwa Mai yalwa ne, Masani



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 33

وَلۡيَسۡتَعۡفِفِ ٱلَّذِينَ لَا يَجِدُونَ نِكَاحًا حَتَّىٰ يُغۡنِيَهُمُ ٱللَّهُ مِن فَضۡلِهِۦۗ وَٱلَّذِينَ يَبۡتَغُونَ ٱلۡكِتَٰبَ مِمَّا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُكُمۡ فَكَاتِبُوهُمۡ إِنۡ عَلِمۡتُمۡ فِيهِمۡ خَيۡرٗاۖ وَءَاتُوهُم مِّن مَّالِ ٱللَّهِ ٱلَّذِيٓ ءَاتَىٰكُمۡۚ وَلَا تُكۡرِهُواْ فَتَيَٰتِكُمۡ عَلَى ٱلۡبِغَآءِ إِنۡ أَرَدۡنَ تَحَصُّنٗا لِّتَبۡتَغُواْ عَرَضَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۚ وَمَن يُكۡرِههُّنَّ فَإِنَّ ٱللَّهَ مِنۢ بَعۡدِ إِكۡرَٰهِهِنَّ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Waxanda kuma ba su sami wadatar yin aure ba su kame kansu har Allah Ya wadata su daga falalarsa. Waxanda kuwa suke neman fansar kansu daga bayinku[1], sai ku ba su damar fansar kansu, idan kun san suna da halin iya biya; kuma ku ba su wani abu daga dukiyar Allah da Ya ba ku. Kada kuma ku tilasta wa kuyanginku ‘yan mata a kan yin zina idan sun nemi kame kai, don ku nemi amfanin rayuwar duniya. Wanda duk kuwa ya tilasta su, to lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai bayan tilastawar da aka yi musu


1- Watau ta hanyar biyan wani kuxi da za a yanka musu idan sun biya sun zama ‘yantattun ‘ya’ya.


Capítulo: Suratun Nur

Verso : 60

وَٱلۡقَوَٰعِدُ مِنَ ٱلنِّسَآءِ ٱلَّـٰتِي لَا يَرۡجُونَ نِكَاحٗا فَلَيۡسَ عَلَيۡهِنَّ جُنَاحٌ أَن يَضَعۡنَ ثِيَابَهُنَّ غَيۡرَ مُتَبَرِّجَٰتِۭ بِزِينَةٖۖ وَأَن يَسۡتَعۡفِفۡنَ خَيۡرٞ لَّهُنَّۗ وَٱللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٞ

Tsofaffin mata kuwa waxanda ba sa tsammanin yin aure to babu laifi a kansu su sauke lulluvinsu, amma ba masu fitar da adonsu ba; amma kuma su yi lulluvi shi ya fi zama alheri a gare su. Allah kuwa Mai ji ne, Masani



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 4

مَّا جَعَلَ ٱللَّهُ لِرَجُلٖ مِّن قَلۡبَيۡنِ فِي جَوۡفِهِۦۚ وَمَا جَعَلَ أَزۡوَٰجَكُمُ ٱلَّـٰٓـِٔي تُظَٰهِرُونَ مِنۡهُنَّ أُمَّهَٰتِكُمۡۚ وَمَا جَعَلَ أَدۡعِيَآءَكُمۡ أَبۡنَآءَكُمۡۚ ذَٰلِكُمۡ قَوۡلُكُم بِأَفۡوَٰهِكُمۡۖ وَٱللَّهُ يَقُولُ ٱلۡحَقَّ وَهُوَ يَهۡدِي ٱلسَّبِيلَ

Allah bai sanya wa wani mutum zuciya biyu ba a cikinsa. Kuma bai sanya matanku waxanda kuke yi musu zihari[1] (su zama) iyayenku ba. Bai kuma sanya ‘ya’yan riqonku (su zama) ‘ya’yanku ba[2]. Wannan magana ce da kuke yi da bakunanku; Allah kuwa Yana faxar gaskiya ne, kuma Shi ne Yake shiryarwa ga hanya (ta gaskiya)


1- Zihari, shi ne miji ya kwatanta matarsa da mahaifiyarsa wajen haramci. Wannan wata al’ada ce ta Larabawa a jahiliyya da Musulunci ya haramta ta.


2- Gabanin zuwa Musulunci Larabawa sukan mayar da ‘ya’yansu na riqo kamar ‘ya’yan da suka haifa wajen hukunce-hukunce. Sai Allah ya haramta aikata haka.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 51

۞تُرۡجِي مَن تَشَآءُ مِنۡهُنَّ وَتُـٔۡوِيٓ إِلَيۡكَ مَن تَشَآءُۖ وَمَنِ ٱبۡتَغَيۡتَ مِمَّنۡ عَزَلۡتَ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكَۚ ذَٰلِكَ أَدۡنَىٰٓ أَن تَقَرَّ أَعۡيُنُهُنَّ وَلَا يَحۡزَنَّ وَيَرۡضَيۡنَ بِمَآ ءَاتَيۡتَهُنَّ كُلُّهُنَّۚ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ مَا فِي قُلُوبِكُمۡۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَلِيمٗا

Ka dakatar da duk wadda ka ga dama daga cikinsu, ka kuma jawo duk wadda ka ga dama[1]; (duk) wadda kuwa ka nema daga waxanda ka dakatar, to babu wani laifi a kanka. (Yin) wannan kuwa shi ya fi kusantar da kwanciyar ransu da kuma rashin yin baqin ciki, su kuma yarda da duk abin da ka ba su dukkansu[2]. Allah kuwa Yana sane da abin da yake cikin zukatanku. Allah kuwa Ya kasance Masani ne, Mai haquri


1- Watau Allah () bai wajabta masa rabon kwana a tsakanin matansa ba, yana iya dakatar da kwanan wadda ya ga dama ko ya jawo da kwananta.


2- Domin sun tabbatar ba zai hana musu haqqoqinsu ba ko ya qi yi musu adalci.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 55

لَّا جُنَاحَ عَلَيۡهِنَّ فِيٓ ءَابَآئِهِنَّ وَلَآ أَبۡنَآئِهِنَّ وَلَآ إِخۡوَٰنِهِنَّ وَلَآ أَبۡنَآءِ إِخۡوَٰنِهِنَّ وَلَآ أَبۡنَآءِ أَخَوَٰتِهِنَّ وَلَا نِسَآئِهِنَّ وَلَا مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُنَّۗ وَٱتَّقِينَ ٱللَّهَۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدًا

Babu laifi a kansu (matan) game da iyayensu maza (su gan su kuma su yi magana da su ba tare da shamaki ba) da kuma ‘ya’yansu maza da ‘ya’uwansu da ‘ya’yan ‘yan’uwansu maza da ‘ya’yan ‘yan’uwansu mata, da kuma matansu da bayinsu. Ku kiyaye dokokin Allah. Lalle Allah Ya kasance Mai ganin komai ne



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 59

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ قُل لِّأَزۡوَٰجِكَ وَبَنَاتِكَ وَنِسَآءِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ يُدۡنِينَ عَلَيۡهِنَّ مِن جَلَٰبِيبِهِنَّۚ ذَٰلِكَ أَدۡنَىٰٓ أَن يُعۡرَفۡنَ فَلَا يُؤۡذَيۡنَۗ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Ya kai wannan Annabi, faxa wa matanka da ‘ya’yanka mata da kuma matan muminai (cewa) su sanya lulluvinsu. Wannan shi ya fi sanya wa a gane su[1], don kada a cuce su. Allah kuma Ya kasance Mai gafara ne, Mai rahama


1- Watau a tantance tsakaninsu da mata marasa kamun kai.


Capítulo: Suratu Faxir

Verso : 11

وَٱللَّهُ خَلَقَكُم مِّن تُرَابٖ ثُمَّ مِن نُّطۡفَةٖ ثُمَّ جَعَلَكُمۡ أَزۡوَٰجٗاۚ وَمَا تَحۡمِلُ مِنۡ أُنثَىٰ وَلَا تَضَعُ إِلَّا بِعِلۡمِهِۦۚ وَمَا يُعَمَّرُ مِن مُّعَمَّرٖ وَلَا يُنقَصُ مِنۡ عُمُرِهِۦٓ إِلَّا فِي كِتَٰبٍۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ

Kuma Allah Ya halicce ku ne daga turvaya sannan daga maniyyi, sannan kuma Ya mayar da ku maza da mata. Kuma mace ba za ta xauki ciki ba, ba kuma za ta haifu ba sai da saninsa. Ba kuma wani mai tsawon rai da za a raya shi, ko kuma wani da za a rage tsawon ransa face yana (rubuce) a cikin Lauhul-Mahafuzu. Wannan kuwa a wurin Allah mai sauqi ne



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 16

أَمِ ٱتَّخَذَ مِمَّا يَخۡلُقُ بَنَاتٖ وَأَصۡفَىٰكُم بِٱلۡبَنِينَ

Yanzu Ya xauki `ya`ya mata daga abubuwan da Yake halitta, ku kuma Ya zava muku `ya`ya maza?



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 17

وَإِذَا بُشِّرَ أَحَدُهُم بِمَا ضَرَبَ لِلرَّحۡمَٰنِ مَثَلٗا ظَلَّ وَجۡهُهُۥ مُسۡوَدّٗا وَهُوَ كَظِيمٌ

Idan kuma aka yi wa xayansu albishir da abin da ya buga misali cewa na (Allah) Arrahmanu ne, sai fuskarsa ta yini a murtuke yana cike da baqin ciki



Capítulo: Suratul Mujadila

Verso : 1

قَدۡ سَمِعَ ٱللَّهُ قَوۡلَ ٱلَّتِي تُجَٰدِلُكَ فِي زَوۡجِهَا وَتَشۡتَكِيٓ إِلَى ٱللَّهِ وَٱللَّهُ يَسۡمَعُ تَحَاوُرَكُمَآۚ إِنَّ ٱللَّهَ سَمِيعُۢ بَصِيرٌ

Haqiqa Allah ya ji zancen wadda take muhawara da kai game da (lamarin) mijinta[1], tana kuma kai qara zuwa ga Allah, Allah kuma Yana jin muhawararku. Lalle Allah Mai ji ne, Mai gani


1- Ita ce Khaulatu ‘yar Sa’alaba (), mijinta kuwa shi ne Ausu xan Samit ().


Capítulo: Suratul Mujadila

Verso : 2

ٱلَّذِينَ يُظَٰهِرُونَ مِنكُم مِّن نِّسَآئِهِم مَّا هُنَّ أُمَّهَٰتِهِمۡۖ إِنۡ أُمَّهَٰتُهُمۡ إِلَّا ٱلَّـٰٓـِٔي وَلَدۡنَهُمۡۚ وَإِنَّهُمۡ لَيَقُولُونَ مُنكَرٗا مِّنَ ٱلۡقَوۡلِ وَزُورٗاۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ لَعَفُوٌّ غَفُورٞ

Waxanda suke yin zihari[1] daga cikinku ga matansu, su ba iyayensu mata ba ne; iyayensu mata su ne waxanda kawai suka haife su. Lalle kuma su tabbas suna faxar muguwar magana ne da tsagwaron qarya. Kuma lalle Allah tabbas Mai afuwa ne, Mai gafara


1- Shi ne miji ya kwatanta matarsa da mahaifiyarsa ya ce: “Ke a wurina kamar bayan mahaifiyata ne”. A zamanin jahiliyya idan miji ya faxa wa matarsa haka, to ta haramta a gare shi har abada.


Capítulo: Suratul Mujadila

Verso : 3

وَٱلَّذِينَ يُظَٰهِرُونَ مِن نِّسَآئِهِمۡ ثُمَّ يَعُودُونَ لِمَا قَالُواْ فَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مِّن قَبۡلِ أَن يَتَمَآسَّاۚ ذَٰلِكُمۡ تُوعَظُونَ بِهِۦۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٞ

Waxanda kuwa suke yin zihari ga matansu sannan suka yi niyyar janye abin da suka faxa, to sai su ‘yanta wuyaye (bawa namiji ko mace), tun kafin su sadu. Wannan (shi ne abin da) ake yi muku wa’azi da shi. Allah kuma Masanin abin da kuke aikatawa ne



Capítulo: Suratul Mujadila

Verso : 4

فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ شَهۡرَيۡنِ مُتَتَابِعَيۡنِ مِن قَبۡلِ أَن يَتَمَآسَّاۖ فَمَن لَّمۡ يَسۡتَطِعۡ فَإِطۡعَامُ سِتِّينَ مِسۡكِينٗاۚ ذَٰلِكَ لِتُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦۚ وَتِلۡكَ حُدُودُ ٱللَّهِۗ وَلِلۡكَٰفِرِينَ عَذَابٌ أَلِيمٌ

Sannan wanda bai samu ba, to sai ya yi azumin wata biyu a jere tun kafin su sadu; sannan wanda bai sami iko ba sai ya ciyar da miskini sittin. Wannan kuwa don ku yi imani da Allah da Manzonsa. Waxannan kuma su ne iyakokin Allah. Kafirai kuma suna da azaba mai raxaxi



Capítulo: Suratux Xalaq

Verso : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ إِذَا طَلَّقۡتُمُ ٱلنِّسَآءَ فَطَلِّقُوهُنَّ لِعِدَّتِهِنَّ وَأَحۡصُواْ ٱلۡعِدَّةَۖ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ رَبَّكُمۡۖ لَا تُخۡرِجُوهُنَّ مِنۢ بُيُوتِهِنَّ وَلَا يَخۡرُجۡنَ إِلَّآ أَن يَأۡتِينَ بِفَٰحِشَةٖ مُّبَيِّنَةٖۚ وَتِلۡكَ حُدُودُ ٱللَّهِۚ وَمَن يَتَعَدَّ حُدُودَ ٱللَّهِ فَقَدۡ ظَلَمَ نَفۡسَهُۥۚ لَا تَدۡرِي لَعَلَّ ٱللَّهَ يُحۡدِثُ بَعۡدَ ذَٰلِكَ أَمۡرٗا

Ya kai wannan Annabi, (ka ce da jama’arka): “Idan za ku saki mata sai ku sake su a farkon iddarsu[1], kuma ku kula da kiyaye qidaya idda[2]; kuma ku kiyaye dokokin Ubangijinku; kada ku fitar da su daga xakunansu, su ma kada su fita sai dai idan sun aikata alfasha bayayyananna. Waxannan kuwa su ne iyakokin Allah. Wanda kuwa duk ya qetare iyakokin Allah, to haqiqa ya zalunci kansa. Ba ka sani ba ko Allah zai farar da wani al’amari bayan wannan[3]


1- Watau lokacin da suka yi tsarkin haila wanda kuma ba su sadu da su ba a cikinsa, ko kuma idan ciki ya bayyana.


2- Domin su iya dawo da matansu kafin qarewarta idan suna buqatar yin haka.


3- Watau Allah ya sake kawo jituwa a tsakanin mijin da matar su fahimci juna su mayar da aurensu.


Capítulo: Suratux Xalaq

Verso : 2

فَإِذَا بَلَغۡنَ أَجَلَهُنَّ فَأَمۡسِكُوهُنَّ بِمَعۡرُوفٍ أَوۡ فَارِقُوهُنَّ بِمَعۡرُوفٖ وَأَشۡهِدُواْ ذَوَيۡ عَدۡلٖ مِّنكُمۡ وَأَقِيمُواْ ٱلشَّهَٰدَةَ لِلَّهِۚ ذَٰلِكُمۡ يُوعَظُ بِهِۦ مَن كَانَ يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۚ وَمَن يَتَّقِ ٱللَّهَ يَجۡعَل لَّهُۥ مَخۡرَجٗا

Idan kuma sun kusa isa qarshen iddarsu, to ku riqe su da kyautatawa (ku yi kome), ko kuma ku rabu da su da kyautatawa, kuma ku kafa shaidar adilai guda biyu daga cikinku, ku kuma tsayar da shaidarku saboda Allah. Wannan shi ne ake yin wa’azi da shi ga wanda ya kasance yana yin imani da Allah da ranar lahira. Wanda kuma ya kiyaye dokokin Allah to zai sanya masa mafita



Capítulo: Suratux Xalaq

Verso : 6

أَسۡكِنُوهُنَّ مِنۡ حَيۡثُ سَكَنتُم مِّن وُجۡدِكُمۡ وَلَا تُضَآرُّوهُنَّ لِتُضَيِّقُواْ عَلَيۡهِنَّۚ وَإِن كُنَّ أُوْلَٰتِ حَمۡلٖ فَأَنفِقُواْ عَلَيۡهِنَّ حَتَّىٰ يَضَعۡنَ حَمۡلَهُنَّۚ فَإِنۡ أَرۡضَعۡنَ لَكُمۡ فَـَٔاتُوهُنَّ أُجُورَهُنَّ وَأۡتَمِرُواْ بَيۡنَكُم بِمَعۡرُوفٖۖ وَإِن تَعَاسَرۡتُمۡ فَسَتُرۡضِعُ لَهُۥٓ أُخۡرَىٰ

Ku zaunar da su (matayen) a inda kuka zauna daidai da samunku, kada kuma ku cuce su don ku quntata musu. Idan kuwa sun kasance masu ciki to sai ku ciyar da su har sai sun haife cikinsu. Sannan idan sun shayar muku da (‘ya’yanku) sai ku ba su ladansu; ku kuma daidaita a tsakaninku ta hanya tagari; idan kuma kuka kasa daidaitawa, to wata mai shayarwar sai ta shayar masa



Capítulo: Suratux Xalaq

Verso : 7

لِيُنفِقۡ ذُو سَعَةٖ مِّن سَعَتِهِۦۖ وَمَن قُدِرَ عَلَيۡهِ رِزۡقُهُۥ فَلۡيُنفِقۡ مِمَّآ ءَاتَىٰهُ ٱللَّهُۚ لَا يُكَلِّفُ ٱللَّهُ نَفۡسًا إِلَّا مَآ ءَاتَىٰهَاۚ سَيَجۡعَلُ ٱللَّهُ بَعۡدَ عُسۡرٖ يُسۡرٗا

Mawadaci ya ciyar daidai da wadatarsa; wanda kuwa aka quntata masa arzikinsa, to ya ciyar daidai da abin da Allah Ya ba shi. Allah ba Ya xora wa rai sai gwargwadon abin da Ya ba shi. Kuma da sannu Allah zai sanya sauqi bayan tsanani



Capítulo: Suratut Tahrim

Verso : 10

ضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱمۡرَأَتَ نُوحٖ وَٱمۡرَأَتَ لُوطٖۖ كَانَتَا تَحۡتَ عَبۡدَيۡنِ مِنۡ عِبَادِنَا صَٰلِحَيۡنِ فَخَانَتَاهُمَا فَلَمۡ يُغۡنِيَا عَنۡهُمَا مِنَ ٱللَّهِ شَيۡـٔٗا وَقِيلَ ٱدۡخُلَا ٱلنَّارَ مَعَ ٱلدَّـٰخِلِينَ

Allah Ya ba da wani misali ga waxanda suka kafirta da matar Nuhu da matar Luxu; sun kasance qarqashin (igiyar auren) wasu bayi su biyu salihai daga bayinmu, sai suka ha’ince su[1], saboda haka ba su wadatar musu komai ba (daga azabar) Allah, aka kuma ce: “Ku shiga wuta tare da masu shiga.”


1- Watau suka kafirce musu, suka riqa hana mutane bin addinin Allah, suka kuma riqa goyon bayan kafirai.


Capítulo: Suratut Tahrim

Verso : 11

وَضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا لِّلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱمۡرَأَتَ فِرۡعَوۡنَ إِذۡ قَالَتۡ رَبِّ ٱبۡنِ لِي عِندَكَ بَيۡتٗا فِي ٱلۡجَنَّةِ وَنَجِّنِي مِن فِرۡعَوۡنَ وَعَمَلِهِۦ وَنَجِّنِي مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Allah kuma Ya ba da wani misali ga waxanda suka yi imani da matar Fir’auna lokacin da ta ce: “Ya Ubangijina, Ka gina min gida a wurinka cikin Aljanna, Ka kuma tserar da ni daga Fir’auna da aikinsa, kuma Ka tserar da ni daga azzaluman mutane.”



Capítulo: Suratut Tahrim

Verso : 12

وَمَرۡيَمَ ٱبۡنَتَ عِمۡرَٰنَ ٱلَّتِيٓ أَحۡصَنَتۡ فَرۡجَهَا فَنَفَخۡنَا فِيهِ مِن رُّوحِنَا وَصَدَّقَتۡ بِكَلِمَٰتِ رَبِّهَا وَكُتُبِهِۦ وَكَانَتۡ مِنَ ٱلۡقَٰنِتِينَ

Da kuma Maryamu ‘yar Imrana wadda ta kiyaye matuncinta, sai Muka masa busa daga Ruhinmu[1], ta kuma gaskata ayoyin Ubangijinta da littattafansa, ta kuma kasance daga masu biyayya ga Allah


1- Watau Allah ya umarci Mala’ika Jibrilu () ya yi busa a gare ta.


Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne



Capítulo: Suratut Takwir

Verso : 7

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتۡ

Idan kuma rayuka aka haxa su (da jinsinsu)



Capítulo: Suratut Takwir

Verso : 8

وَإِذَا ٱلۡمَوۡءُۥدَةُ سُئِلَتۡ

Idan kuma yarinyar da aka binne da rai aka tambaye ta



Capítulo: Suratut Takwir

Verso : 9

بِأَيِّ ذَنۢبٖ قُتِلَتۡ

Da wane laifi ne aka kashe ta?



Capítulo: Suratut Takwir

Verso : 14

عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّآ أَحۡضَرَتۡ

To kowane rai ya san abin da ya halarto (da shi na ayyuka)