وَٱلۡوَزۡنُ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡحَقُّۚ فَمَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ
Awo kuma a wannan ranar gaskiya ne. Don haka duk wanda ma’aunansa suka yi nauyi, to waxannan su ne masu rabauta
Compartir :
وَمَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُم بِمَا كَانُواْ بِـَٔايَٰتِنَا يَظۡلِمُونَ
Wanda kuwa ma’aunansa suka yi sakayau, to waxannan su ne waxanda suka yi hasarar kawunansu, saboda abin da suka kasance suna yi na zalunci da ayoyinmu
فَمَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ
To waxanda ma’aunansu suka yi nauyi waxannan su ne masu babban rabo
وَمَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فِي جَهَنَّمَ خَٰلِدُونَ
Waxanda kuwa ma’aunansu suka yi sakayau waxannan su ne waxanda suka yi asarar kawunansu, suna masu dawwama a cikin (wutar) Jahannama
فَأَمَّا مَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ
To amma wanda ma’aunan ayyukansa suka yi nauyi
فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ
To shi kam yana cikin rayuwa mai gamsarwa
وَأَمَّا مَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ
Amma kuma duk wanda ma’aunan ayyukansa suka yi shafal
فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٞ
To shi makomarsa (wutar) Hawiya ce