Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 41

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle Aljanna ita ce makoma



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 42

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا

Suna tambayar ka game da alqiyama, yaushe ne lokacinta?



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 43

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ

Me ya gama ka da ambaton lokacinta?



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 44

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ

Zuwa ga Ubangijinka ne iyakacin saninta yake[1]


1- Watau Allah ne kaxai ya san lokacin aukuwarta.


Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 45

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا

Kai dai kawai mai gargaxin wanda yake tsoron ta ne



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 46

كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا

Kai ka ce su ranar da za su gan ta ba su zauna ba (a duniya) face wani yammaci ko kuma hantsinta



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 33

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ

Sannan idan mai sa kurunta ta zo (watau busa ta farko)



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 34

يَوۡمَ يَفِرُّ ٱلۡمَرۡءُ مِنۡ أَخِيهِ

A ranar da mutum yake guje wa xan’uwansa



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 35

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

Da uwarsa da ubansa



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 36

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

Da matarsa da ‘ya’yansa



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 37

لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ

Kowane mutum daga cikinsu a wannan ranar yana da lamarin da ya sha kansa



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 38

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ

Wasu fuskoki a wannan ranar masu haske ne



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 39

ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ

Masu dariya, masu farin ciki



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 40

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ

Wasu fuskokin kuma a ranar akwai qura a kansu



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 41

تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ

Baqin ciki zai lulluve su



Capítulo: Suratu Abasa

Verso : 42

أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ

Waxannan su ne kafirai mavarnata



Capítulo: Suratul Infixar

Verso : 17

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Capítulo: Suratul Infixar

Verso : 18

ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Capítulo: Suratul Infixar

Verso : 19

يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ

(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 21

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا

Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا

Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu


1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.


Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 23

وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ

Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 24

يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي

Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 25

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ

To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ

Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata



Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 1

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta