مَثَلُهُمۡ كَمَثَلِ ٱلَّذِي ٱسۡتَوۡقَدَ نَارٗا فَلَمَّآ أَضَآءَتۡ مَا حَوۡلَهُۥ ذَهَبَ ٱللَّهُ بِنُورِهِمۡ وَتَرَكَهُمۡ فِي ظُلُمَٰتٖ لَّا يُبۡصِرُونَ
Misalinsu kamar misalin wanda ya wahala har ya kunna wuta ne, yayin da ta haskaka abin da yake daura da shi, sai Allah Ya tafiyar da haskensu Ya bar su cikin duffai ba sa gani
صُمُّۢ بُكۡمٌ عُمۡيٞ فَهُمۡ لَا يَرۡجِعُونَ
( Su ) kurame ne, bebaye ne, makafi ne, don haka ba za su tava dawowa (kan gaskiya) ba
أَوۡ كَصَيِّبٖ مِّنَ ٱلسَّمَآءِ فِيهِ ظُلُمَٰتٞ وَرَعۡدٞ وَبَرۡقٞ يَجۡعَلُونَ أَصَٰبِعَهُمۡ فِيٓ ءَاذَانِهِم مِّنَ ٱلصَّوَٰعِقِ حَذَرَ ٱلۡمَوۡتِۚ وَٱللَّهُ مُحِيطُۢ بِٱلۡكَٰفِرِينَ
Ko kuma (misalinsu) kamar wani mamakon ruwan sama ne, wanda yake xauke da duffai da tsawa da walqiya, har ta kai suna sanya ‘yan yatsunsu cikin kunnuwansu don tsananin tsawarwaki saboda tsoron mutuwa. Allah Kuma Yana kewaye da kafirai (da iliminsa)
يَكَادُ ٱلۡبَرۡقُ يَخۡطَفُ أَبۡصَٰرَهُمۡۖ كُلَّمَآ أَضَآءَ لَهُم مَّشَوۡاْ فِيهِ وَإِذَآ أَظۡلَمَ عَلَيۡهِمۡ قَامُواْۚ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَذَهَبَ بِسَمۡعِهِمۡ وَأَبۡصَٰرِهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ
Walqiyar ta kusa ta fauce idanuwansu. Duk sa›adda ta haska musu sai su ci gaba da tafiya cikin (haskenta); idan kuma ta rufe su da duhu sai su tsaya cak. Da kuwa Allah Ya ga dama da sai Ya tafiyar da jinsu da ganinsu. Lalle Allah Mai iko ne a kan komai
۞إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَسۡتَحۡيِۦٓ أَن يَضۡرِبَ مَثَلٗا مَّا بَعُوضَةٗ فَمَا فَوۡقَهَاۚ فَأَمَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ فَيَعۡلَمُونَ أَنَّهُ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّهِمۡۖ وَأَمَّا ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَيَقُولُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۘ يُضِلُّ بِهِۦ كَثِيرٗا وَيَهۡدِي بِهِۦ كَثِيرٗاۚ وَمَا يُضِلُّ بِهِۦٓ إِلَّا ٱلۡفَٰسِقِينَ
Lalle Allah ba Ya jin kunyar buga kowanne irin misali komai qanqantarsa, sauro da abin da ya fi shi. To amma waxanda suka yi imani suna sanin cewa, lalle shi (wannan misali) gaskiya ne daga Ubangijinsu. Amma waxanda suka kafirta sai su riqa cewa: “Me Allah Yake nufi da wannan misalin?” Yana kuwa vatar da mutane da yawa da shi, kuma Ya shiryar da mutane da yawa da shi, kuma ba kowa Yake vatarwa da shi ba sai fasiqai
وَمَثَلُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ كَمَثَلِ ٱلَّذِي يَنۡعِقُ بِمَا لَا يَسۡمَعُ إِلَّا دُعَآءٗ وَنِدَآءٗۚ صُمُّۢ بُكۡمٌ عُمۡيٞ فَهُمۡ لَا يَعۡقِلُونَ
Misalin wadanda suka kafirta kamar misalin wanda yake daga sauti ne ga wanda ba ya jin (komai) sai kira da sowa. Kurame ne, bebaye ne, makafi ne, don haka su ba sa hankalta
أَوۡ كَٱلَّذِي مَرَّ عَلَىٰ قَرۡيَةٖ وَهِيَ خَاوِيَةٌ عَلَىٰ عُرُوشِهَا قَالَ أَنَّىٰ يُحۡيِۦ هَٰذِهِ ٱللَّهُ بَعۡدَ مَوۡتِهَاۖ فَأَمَاتَهُ ٱللَّهُ مِاْئَةَ عَامٖ ثُمَّ بَعَثَهُۥۖ قَالَ كَمۡ لَبِثۡتَۖ قَالَ لَبِثۡتُ يَوۡمًا أَوۡ بَعۡضَ يَوۡمٖۖ قَالَ بَل لَّبِثۡتَ مِاْئَةَ عَامٖ فَٱنظُرۡ إِلَىٰ طَعَامِكَ وَشَرَابِكَ لَمۡ يَتَسَنَّهۡۖ وَٱنظُرۡ إِلَىٰ حِمَارِكَ وَلِنَجۡعَلَكَ ءَايَةٗ لِّلنَّاسِۖ وَٱنظُرۡ إِلَى ٱلۡعِظَامِ كَيۡفَ نُنشِزُهَا ثُمَّ نَكۡسُوهَا لَحۡمٗاۚ فَلَمَّا تَبَيَّنَ لَهُۥ قَالَ أَعۡلَمُ أَنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ
Ko kuma kamar mutumin da ya wuce ta wata alqarya alhalin ta zama kango, sai ya ce: “Ta yaya Allah zai raya wannan bayan mutuwarta?” Sai Allah Ya karvi rayuwarsa tsawon shekara xari, sannan Ya tashe shi, Ya ce: “Mene ne tsawon lokacin da ka zauna?” Sai ya ce: “Ai na zauna yini xaya ne ko ma wani sashi na yinin.” Sai Ya ce: “Ai ka zauna tsawon shekara xari ne, don haka dubi abincinka da abin shanka bai canja ba, kuma ka dubi jakinka mana, don Mu sanya ka ka zamanto aya ga mutane, kuma ka dubi qasusuwan ka gani yadda za Mu haxa su, sannan Mu lulluve su da nama.”To lokacin da komai ya bayyana a gare shi, sai ya ce: “Na sani lalle Allah Mai iko ne a kan komai.”
مَّثَلُ ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ كَمَثَلِ حَبَّةٍ أَنۢبَتَتۡ سَبۡعَ سَنَابِلَ فِي كُلِّ سُنۢبُلَةٖ مِّاْئَةُ حَبَّةٖۗ وَٱللَّهُ يُضَٰعِفُ لِمَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٌ
Misalin waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu a hanyar Allah, kamar misalin qwaya xaya ce da ta fitar da zangarniya bakwai, a cikinta kowace zangarniya kuma (aka sami) qwaya xari. Kuma Allah Yana ninninkawa ga wanda Ya ga dama, kuma Allah Mai yalwa ne, Masani
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تُبۡطِلُواْ صَدَقَٰتِكُم بِٱلۡمَنِّ وَٱلۡأَذَىٰ كَٱلَّذِي يُنفِقُ مَالَهُۥ رِئَآءَ ٱلنَّاسِ وَلَا يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۖ فَمَثَلُهُۥ كَمَثَلِ صَفۡوَانٍ عَلَيۡهِ تُرَابٞ فَأَصَابَهُۥ وَابِلٞ فَتَرَكَهُۥ صَلۡدٗاۖ لَّا يَقۡدِرُونَ عَلَىٰ شَيۡءٖ مِّمَّا كَسَبُواْۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡكَٰفِرِينَ
Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku vata sadaqoqinku da gori da cutarwa, kamar wanda yake ciyar da dukiyarsa don mutane su gani, kuma ba ya imani da Allah da ranar lahira; to misalinsa kamar misalin kamfa ne da turvaya take a kansa sai ruwan sama mamako ya same shi, sai ya bar shi tatas. Ba za su amfana da komai daga abin da suka aikata ba. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane kafirai
وَمَثَلُ ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمُ ٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِ ٱللَّهِ وَتَثۡبِيتٗا مِّنۡ أَنفُسِهِمۡ كَمَثَلِ جَنَّةِۭ بِرَبۡوَةٍ أَصَابَهَا وَابِلٞ فَـَٔاتَتۡ أُكُلَهَا ضِعۡفَيۡنِ فَإِن لَّمۡ يُصِبۡهَا وَابِلٞ فَطَلّٞۗ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٌ
Kuma misalin waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu don neman yardar Allah da tabbatar da (imani) a zukatansu, kamar misalin gona ce a kan jigawa sai ruwan sama mamako ya same ta, sai ta ba da amfaninta rivi-biyu. To idan mamakon ruwan bai same ta ba, sai yayyafi (ya wadatar da ita). Kuma Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne
أَيَوَدُّ أَحَدُكُمۡ أَن تَكُونَ لَهُۥ جَنَّةٞ مِّن نَّخِيلٖ وَأَعۡنَابٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ لَهُۥ فِيهَا مِن كُلِّ ٱلثَّمَرَٰتِ وَأَصَابَهُ ٱلۡكِبَرُ وَلَهُۥ ذُرِّيَّةٞ ضُعَفَآءُ فَأَصَابَهَآ إِعۡصَارٞ فِيهِ نَارٞ فَٱحۡتَرَقَتۡۗ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّكُمۡ تَتَفَكَّرُونَ
Shin yanzu xayanku zai yi fatan a ce yana da wata gona ta itacen dabino da kuma inabai, wadda qoramu suke gudana a qarqashinta, yana da dukkan wasu nau’uka na ‘ya’yan itace a cikinta, sai kuma girma ya kama shi, kuma ga shi yana da yara raunana, sai kuma wata irin guguwa mai xauke da wuta ta same ta, sai (gonar gaba xaya) ta qone? Kamar haka ne Allah Yake bayyana muku ayoyi don ku riqa yin tunani
مَثَلُ مَا يُنفِقُونَ فِي هَٰذِهِ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا كَمَثَلِ رِيحٖ فِيهَا صِرٌّ أَصَابَتۡ حَرۡثَ قَوۡمٖ ظَلَمُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فَأَهۡلَكَتۡهُۚ وَمَا ظَلَمَهُمُ ٱللَّهُ وَلَٰكِنۡ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ
Misalin abin da suke ciyarwa a wannan rayuwa ta duniya kamar misalin iska ce mai tsananin sanyi, wadda ta auka kan shukar waxansu mutanen da suka zalunci kawunansu, sai ta lalata ta. Kuma Allah bai zalunce su ba, sai dai kawunansu suke zalunta
وَلَوۡ شِئۡنَا لَرَفَعۡنَٰهُ بِهَا وَلَٰكِنَّهُۥٓ أَخۡلَدَ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُۚ فَمَثَلُهُۥ كَمَثَلِ ٱلۡكَلۡبِ إِن تَحۡمِلۡ عَلَيۡهِ يَلۡهَثۡ أَوۡ تَتۡرُكۡهُ يَلۡهَثۚ ذَّـٰلِكَ مَثَلُ ٱلۡقَوۡمِ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَاۚ فَٱقۡصُصِ ٱلۡقَصَصَ لَعَلَّهُمۡ يَتَفَكَّرُونَ
Kuma da Mun ga dama da Mun xaukaka shi a sanadiyyarsu, amma kuma shi ya karkata zuwa ga duniya, don haka ya biye wa son zuciyarsa. To misalinsa kamar misalin kare ne, idan ka kai masa xauki ya yi lallage, idan ma ka qyale shi zai yi lallage, wannan shi ne misalin waxanda suka qaryata ayoyinmu. Don haka ka ba da labari don su yi tunani
سَآءَ مَثَلًا ٱلۡقَوۡمُ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا وَأَنفُسَهُمۡ كَانُواْ يَظۡلِمُونَ
Misalin waxanda suka qaryata ayoyinmu ya munana, kuma kawunansu suka kasance suna zalunta
أَفَمَنۡ أَسَّسَ بُنۡيَٰنَهُۥ عَلَىٰ تَقۡوَىٰ مِنَ ٱللَّهِ وَرِضۡوَٰنٍ خَيۡرٌ أَم مَّنۡ أَسَّسَ بُنۡيَٰنَهُۥ عَلَىٰ شَفَا جُرُفٍ هَارٖ فَٱنۡهَارَ بِهِۦ فِي نَارِ جَهَنَّمَۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ
Yanzu wanda ya sanya harsashin gininsa a kan taqawa ga Allah da (neman) yardarsa[1] shi ya fi ko kuwa wanda ya sanya harshashin gininsa a gefen rami mai zabtarewa, sai ya rubta da shi cikin wutar Jahannama? Allah kuwa ba Ya shiryar da mutane azzalumai
1- Shi ne masallacin Manzon Allah (). Da yawa daga cikin malaman tafsiri suna ganin shi ne masallacin Quba. Wasu kuma sun ce ana nufin duka biyun.
لَا يَزَالُ بُنۡيَٰنُهُمُ ٱلَّذِي بَنَوۡاْ رِيبَةٗ فِي قُلُوبِهِمۡ إِلَّآ أَن تَقَطَّعَ قُلُوبُهُمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٌ
Ginin nasu da suka yi ba zai daina zama abin kokwanto a zukatansu ba har sai zukatan nasu sun tsittsinke. Allah kuwa Masani ne, Mai hikima
إِنَّمَا مَثَلُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا كَمَآءٍ أَنزَلۡنَٰهُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ فَٱخۡتَلَطَ بِهِۦ نَبَاتُ ٱلۡأَرۡضِ مِمَّا يَأۡكُلُ ٱلنَّاسُ وَٱلۡأَنۡعَٰمُ حَتَّىٰٓ إِذَآ أَخَذَتِ ٱلۡأَرۡضُ زُخۡرُفَهَا وَٱزَّيَّنَتۡ وَظَنَّ أَهۡلُهَآ أَنَّهُمۡ قَٰدِرُونَ عَلَيۡهَآ أَتَىٰهَآ أَمۡرُنَا لَيۡلًا أَوۡ نَهَارٗا فَجَعَلۡنَٰهَا حَصِيدٗا كَأَن لَّمۡ تَغۡنَ بِٱلۡأَمۡسِۚ كَذَٰلِكَ نُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ لِقَوۡمٖ يَتَفَكَّرُونَ
Misalin rayuwar duniya kawai kamar ruwa ne da Muka saukar da shi daga sama, to sai shukokin da suke kan qasa suka cuxanya da shi daga abin da mutane da dabbobi suke ci; har lokacin da qasa ta qawata (da shi) ta kuma yi ado; masu ita kuma suka sakankance cewa su masu ikon cin amfaninta ne, sai qaddararmu ta zo mata cikin dare ko rana, sai Muka mayar da ita girbabbiya kamar daxai ba ta rayu ba a jiya. Kamar haka Muke bayyana ayoyi ga mutanen da suke tunani
۞مَثَلُ ٱلۡفَرِيقَيۡنِ كَٱلۡأَعۡمَىٰ وَٱلۡأَصَمِّ وَٱلۡبَصِيرِ وَٱلسَّمِيعِۚ هَلۡ يَسۡتَوِيَانِ مَثَلًاۚ أَفَلَا تَذَكَّرُونَ
Misalin jama’ar nan guda biyu (mumini da kafiri) kamar makaho ne da kurma da kuma mai gani da mai ji. Shin ga misali za su zama daidai kuwa? To me ya sa ba za ku wa’azantu ba?
مَّثَلُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِرَبِّهِمۡۖ أَعۡمَٰلُهُمۡ كَرَمَادٍ ٱشۡتَدَّتۡ بِهِ ٱلرِّيحُ فِي يَوۡمٍ عَاصِفٖۖ لَّا يَقۡدِرُونَ مِمَّا كَسَبُواْ عَلَىٰ شَيۡءٖۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلضَّلَٰلُ ٱلۡبَعِيدُ
Misalin waxanda suka kafirce wa Ubangijnsu; ayyukansu sun yi kama da toka wadda iska mai tsananin qarfi ta kwasa a wata rana mai guguwa; ba za su sami iko a kan komai ba dangane da abin da suka aikata (na kirki). Wannan shi ne vata mai nisa
أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ ضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا كَلِمَةٗ طَيِّبَةٗ كَشَجَرَةٖ طَيِّبَةٍ أَصۡلُهَا ثَابِتٞ وَفَرۡعُهَا فِي ٱلسَّمَآءِ
Shin ba ka ga yadda Allah Ya ba da misali ba? Daddaxar kalma[1] kamar daddaxar bishiya ce[2] wadda tushenta kafaffe ne (a qasa) reshenta kuma yana sama
1- Daddaxar kalma ita ce kalmar shahada, watau shaidawa babu abin bauta da gaskiya sai Allah.
2- Daddaxar bishiya kuwa ita ce bishiyar dabino. A nan ana nufin mumini. Kalmar shahada tana kafa tushenta a ciki zuciyar mumini.
تُؤۡتِيٓ أُكُلَهَا كُلَّ حِينِۭ بِإِذۡنِ رَبِّهَاۗ وَيَضۡرِبُ ٱللَّهُ ٱلۡأَمۡثَالَ لِلنَّاسِ لَعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ
Tana bayar da ‘ya’yanta ko da yaushe da izinin Ubangijinta. Allah kuwa Yana ba da misalai ne ga mutane don su wa’azantu
وَمَثَلُ كَلِمَةٍ خَبِيثَةٖ كَشَجَرَةٍ خَبِيثَةٍ ٱجۡتُثَّتۡ مِن فَوۡقِ ٱلۡأَرۡضِ مَا لَهَا مِن قَرَارٖ
Misalin kuma mummunar kalma kamar mummunar bishiya ce da aka tumvuke daga kan qasa, ba ta da wata matabbata
يُثَبِّتُ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱلۡقَوۡلِ ٱلثَّابِتِ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَفِي ٱلۡأٓخِرَةِۖ وَيُضِلُّ ٱللَّهُ ٱلظَّـٰلِمِينَۚ وَيَفۡعَلُ ٱللَّهُ مَا يَشَآءُ
Allah Yana tabbatar da waxanda suka yi imani a kan magana tabbatacciya a rayuwar duniya da kuma a lahira; Yana kuma vatar da azzalumai. Allah kuma Yana aikata abin da Ya ga dama
۞ضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلًا عَبۡدٗا مَّمۡلُوكٗا لَّا يَقۡدِرُ عَلَىٰ شَيۡءٖ وَمَن رَّزَقۡنَٰهُ مِنَّا رِزۡقًا حَسَنٗا فَهُوَ يُنفِقُ مِنۡهُ سِرّٗا وَجَهۡرًاۖ هَلۡ يَسۡتَوُۥنَۚ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِۚ بَلۡ أَكۡثَرُهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ
Allah kuma Ya ba da misali da bawan da aka mallaka, ba shi da iko a kan komai, da kuma wanda Muka bai wa arziki nagari daga gare Mu, to shi kuma yana ciyarwa daga shi (arzikin) a voye da kuma sarari; yanzu za su yi daidai? (Ai ba za su yi daidai ba). To godiya ta tabbata ga Allah. A’a, yawancinsu dai ba su san (haka) ba ne
وَضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا رَّجُلَيۡنِ أَحَدُهُمَآ أَبۡكَمُ لَا يَقۡدِرُ عَلَىٰ شَيۡءٖ وَهُوَ كَلٌّ عَلَىٰ مَوۡلَىٰهُ أَيۡنَمَا يُوَجِّههُّ لَا يَأۡتِ بِخَيۡرٍ هَلۡ يَسۡتَوِي هُوَ وَمَن يَأۡمُرُ بِٱلۡعَدۡلِ وَهُوَ عَلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ
Allah kuma Ya ba da wani misali da mutum biyu, xayansu bebe ne ba ya iya yin komai, kuma ya zama nauyi a kan mai gidansa, duk inda ya fuskantar da shi ba zai zo da wani alheri ba. Yanzu shi zai yi daidai da wanda yake umarni da adalci kuma yana bisa tafarki madaidaici?
وَلَا تَكُونُواْ كَٱلَّتِي نَقَضَتۡ غَزۡلَهَا مِنۢ بَعۡدِ قُوَّةٍ أَنكَٰثٗا تَتَّخِذُونَ أَيۡمَٰنَكُمۡ دَخَلَۢا بَيۡنَكُمۡ أَن تَكُونَ أُمَّةٌ هِيَ أَرۡبَىٰ مِنۡ أُمَّةٍۚ إِنَّمَا يَبۡلُوكُمُ ٱللَّهُ بِهِۦۚ وَلَيُبَيِّنَنَّ لَكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ مَا كُنتُمۡ فِيهِ تَخۡتَلِفُونَ
Kada kuma ku zamanto kamar (mace) wadda ta warware kaxinta wara-wara bayan qarfinsa, kuna xaukar rantse-rantsenku yaudara a tsakaninku, don ganin kasancewar wata al’umma ta fi wata yawa da qarfi. Allah dai Yana jarabtar ku da shi (cika alqawari) ne. Don kuma a ranar alqiyama Ya bayyana muku abin da kuka kasance kuna savani a game da shi
وَضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا قَرۡيَةٗ كَانَتۡ ءَامِنَةٗ مُّطۡمَئِنَّةٗ يَأۡتِيهَا رِزۡقُهَا رَغَدٗا مِّن كُلِّ مَكَانٖ فَكَفَرَتۡ بِأَنۡعُمِ ٱللَّهِ فَأَذَٰقَهَا ٱللَّهُ لِبَاسَ ٱلۡجُوعِ وَٱلۡخَوۡفِ بِمَا كَانُواْ يَصۡنَعُونَ
Allah kuma Ya ba da misali da wata alqarya[1] wadda ta kasance cikin aminci da kwanciyar hankali, arzikinta yana zo mata a yalwace ta kowanne wuri, sai ta kafirce wa ni’imomin Allah, to sai Allah Ya xanxana mata masifar yunwa da tsoro saboda abin da suka kasance suna aikatawa
1- Watau garin Makka.
وَلَقَدۡ جَآءَهُمۡ رَسُولٞ مِّنۡهُمۡ فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمُ ٱلۡعَذَابُ وَهُمۡ ظَٰلِمُونَ
Haqiqa kuma Manzo ya zo musu daga cikinsu, sai suka qaryata shi, to sai azaba ta afka musu alhali suna azzalumai
وَٱضۡرِبۡ لَهُم مَّثَلَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا كَمَآءٍ أَنزَلۡنَٰهُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ فَٱخۡتَلَطَ بِهِۦ نَبَاتُ ٱلۡأَرۡضِ فَأَصۡبَحَ هَشِيمٗا تَذۡرُوهُ ٱلرِّيَٰحُۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ مُّقۡتَدِرًا
Kuma ka ba su misalin rayuwar duniya (wadda take) kamar ruwa ne da Muka saukar da shi daga sama, sai tsirran qasa suka cakuxa da shi, sannan ya zama busasshe, iska tana xaixaita shi. Allah kuwa Ya kasance Mai iko ne a kan komai
حُنَفَآءَ لِلَّهِ غَيۡرَ مُشۡرِكِينَ بِهِۦۚ وَمَن يُشۡرِكۡ بِٱللَّهِ فَكَأَنَّمَا خَرَّ مِنَ ٱلسَّمَآءِ فَتَخۡطَفُهُ ٱلطَّيۡرُ أَوۡ تَهۡوِي بِهِ ٱلرِّيحُ فِي مَكَانٖ سَحِيقٖ
Kuna masu kauce wa varna don Allah, ba masu haxa shi da wasu ba. Duk wanda kuwa ya haxa Allah da wani, to kamar ya faxo ne daga sama, sai tsuntsaye suka fauce shi, (suka yagalgala shi) ko kuma iska ta jefa shi cikin wani wuri mai zurfi (ta rugurguza shi)