Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 183

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ كُتِبَ عَلَيۡكُمُ ٱلصِّيَامُ كَمَا كُتِبَ عَلَى ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَتَّقُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabta wa waxanda suke gabaninku, don ku samu taqawa



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 184

أَيَّامٗا مَّعۡدُودَٰتٖۚ فَمَن كَانَ مِنكُم مَّرِيضًا أَوۡ عَلَىٰ سَفَرٖ فَعِدَّةٞ مِّنۡ أَيَّامٍ أُخَرَۚ وَعَلَى ٱلَّذِينَ يُطِيقُونَهُۥ فِدۡيَةٞ طَعَامُ مِسۡكِينٖۖ فَمَن تَطَوَّعَ خَيۡرٗا فَهُوَ خَيۡرٞ لَّهُۥۚ وَأَن تَصُومُواْ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Waxansu kwanaki ne qididdigaggu. To duk wanda ya kasance marar lafiya a cikinku ko a kan wata tafiya, to (idan ya sha azumi) sai ya rama a waxansu kwanakin na daban. Kuma waxanda za su yi azumi da wahala su ba da fansa ta ciyar da miskini; to duk wanda ya qara (a kan abincin miskini), to wannan alheri ne gare shi. Amma ku yi azumin shi ne ya fi muku alheri, in har kun kusance kuna sani



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 185

شَهۡرُ رَمَضَانَ ٱلَّذِيٓ أُنزِلَ فِيهِ ٱلۡقُرۡءَانُ هُدٗى لِّلنَّاسِ وَبَيِّنَٰتٖ مِّنَ ٱلۡهُدَىٰ وَٱلۡفُرۡقَانِۚ فَمَن شَهِدَ مِنكُمُ ٱلشَّهۡرَ فَلۡيَصُمۡهُۖ وَمَن كَانَ مَرِيضًا أَوۡ عَلَىٰ سَفَرٖ فَعِدَّةٞ مِّنۡ أَيَّامٍ أُخَرَۗ يُرِيدُ ٱللَّهُ بِكُمُ ٱلۡيُسۡرَ وَلَا يُرِيدُ بِكُمُ ٱلۡعُسۡرَ وَلِتُكۡمِلُواْ ٱلۡعِدَّةَ وَلِتُكَبِّرُواْ ٱللَّهَ عَلَىٰ مَا هَدَىٰكُمۡ وَلَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Watan Ramadan shi ne wanda aka saukar da Alqur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane kuma ayoyi ne bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa (tsakanin qarya da gaskiya). Don haka duk wanda ya halarci wannan watan daga cikinku, to ya azumce shi, kuma wanda ya kasance marar lafiya ko a kan wata tafiya, to (idan ya sha azumi) sai ya rama a waxansu kwanakin na daban. Allah Yana nufin sauqi a gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani a gare ku, don ku cika adadin (kwanakin Ramadan), kuma domin ku girmama Allah bisa ga shiryar da ku da Ya yi, don ku yi godiya



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 187

أُحِلَّ لَكُمۡ لَيۡلَةَ ٱلصِّيَامِ ٱلرَّفَثُ إِلَىٰ نِسَآئِكُمۡۚ هُنَّ لِبَاسٞ لَّكُمۡ وَأَنتُمۡ لِبَاسٞ لَّهُنَّۗ عَلِمَ ٱللَّهُ أَنَّكُمۡ كُنتُمۡ تَخۡتَانُونَ أَنفُسَكُمۡ فَتَابَ عَلَيۡكُمۡ وَعَفَا عَنكُمۡۖ فَٱلۡـَٰٔنَ بَٰشِرُوهُنَّ وَٱبۡتَغُواْ مَا كَتَبَ ٱللَّهُ لَكُمۡۚ وَكُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ حَتَّىٰ يَتَبَيَّنَ لَكُمُ ٱلۡخَيۡطُ ٱلۡأَبۡيَضُ مِنَ ٱلۡخَيۡطِ ٱلۡأَسۡوَدِ مِنَ ٱلۡفَجۡرِۖ ثُمَّ أَتِمُّواْ ٱلصِّيَامَ إِلَى ٱلَّيۡلِۚ وَلَا تُبَٰشِرُوهُنَّ وَأَنتُمۡ عَٰكِفُونَ فِي ٱلۡمَسَٰجِدِۗ تِلۡكَ حُدُودُ ٱللَّهِ فَلَا تَقۡرَبُوهَاۗ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ ءَايَٰتِهِۦ لِلنَّاسِ لَعَلَّهُمۡ يَتَّقُونَ

An halatta muku saduwa da matanku a daren azumi. Su sutura ne a gare ku, ku ma kuma sutura ne a gare su. Allah Ya san cewa ku lalle kun kasance kuna ha’intar kawunanku, sai Ya karvi tubanku kuma Ya yi muku afuwa; to a yanzu ku sadu da su (da daddare), kuma ku nemi abin da Allah Ya rubuta muku, kuma ku ci, kuma ku sha har farin zare ya bayyana a gare ku daga baqin zare na alfijir (wato ketowar Alfijir), sannan kuma ku cika azumi zuwa dare, kuma kar ku sadu da su alhali kuna i’itikafi a masallatai. Waxannan iyakoki ne na Allah, kada ku kusance su. Kamar haka ne Allah Yake bayyana ayoyinsa ga mutane, don su samu taqawa



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 196

وَأَتِمُّواْ ٱلۡحَجَّ وَٱلۡعُمۡرَةَ لِلَّهِۚ فَإِنۡ أُحۡصِرۡتُمۡ فَمَا ٱسۡتَيۡسَرَ مِنَ ٱلۡهَدۡيِۖ وَلَا تَحۡلِقُواْ رُءُوسَكُمۡ حَتَّىٰ يَبۡلُغَ ٱلۡهَدۡيُ مَحِلَّهُۥۚ فَمَن كَانَ مِنكُم مَّرِيضًا أَوۡ بِهِۦٓ أَذٗى مِّن رَّأۡسِهِۦ فَفِدۡيَةٞ مِّن صِيَامٍ أَوۡ صَدَقَةٍ أَوۡ نُسُكٖۚ فَإِذَآ أَمِنتُمۡ فَمَن تَمَتَّعَ بِٱلۡعُمۡرَةِ إِلَى ٱلۡحَجِّ فَمَا ٱسۡتَيۡسَرَ مِنَ ٱلۡهَدۡيِۚ فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ ثَلَٰثَةِ أَيَّامٖ فِي ٱلۡحَجِّ وَسَبۡعَةٍ إِذَا رَجَعۡتُمۡۗ تِلۡكَ عَشَرَةٞ كَامِلَةٞۗ ذَٰلِكَ لِمَن لَّمۡ يَكُنۡ أَهۡلُهُۥ حَاضِرِي ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Kuma ku cika aikin Hajji da umara domin Allah. To idan an tsare ku, sai ku gabatar da abin da ya sawwaqa na hadaya, kuma kada ku aske kawunanku har sai hadaya ta kai wurin yankanta. To wanda ya kasance a cikinku mara lafiya ko akwai wata cuta a kansa, (idan yayi aski) to sai ya yi fidiya ta (hanyar) yin azumi ko sadaqa ko yanka[1]. Idan kuwa kun amintu, to duk wanda ya yi tamattu’i da yin umara tare da Hajji, to sai ya yanka abin da ya sawwaqa na hadaya; amma wanda bai samu ba, sai ya yi azumin kwana uku a lokacin aikin Hajji, da kuma na kwana bakwai idan kun dawo gida. Waxannan kwana goma ke nan cikakku. Wannan hukuncin yana ga wanda iyalinsa ba sa cikin hurumin Makka ne. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, ku sani cewa, lalle Allah Mai tsananin uquba ne


1- Watau ya yi azumi na kwana uku, ko ya ciyar da miskinai shida, kowanne ya ba shi rabin mudu ko ya yanka akuya.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 92

وَمَا كَانَ لِمُؤۡمِنٍ أَن يَقۡتُلَ مُؤۡمِنًا إِلَّا خَطَـٔٗاۚ وَمَن قَتَلَ مُؤۡمِنًا خَطَـٔٗا فَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖ وَدِيَةٞ مُّسَلَّمَةٌ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦٓ إِلَّآ أَن يَصَّدَّقُواْۚ فَإِن كَانَ مِن قَوۡمٍ عَدُوّٖ لَّكُمۡ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖۖ وَإِن كَانَ مِن قَوۡمِۭ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَهُم مِّيثَٰقٞ فَدِيَةٞ مُّسَلَّمَةٌ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ وَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖۖ فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ شَهۡرَيۡنِ مُتَتَابِعَيۡنِ تَوۡبَةٗ مِّنَ ٱللَّهِۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Kuma bai dace ga mumini ya kashe wani mumini ba, sai bisa kuskure. Wanda ya kashe mumini bisa ga kuskure, to zai ‘yanta bawa ko baiwa mumina da kuma diyya wadda za a miqa wa iyalinsa, sai fa idan sun yafe. Amma idan wanda aka kashe yana cikin mutanen da suke maqiyanku, alhalin kuma shi mumini ne, to za ku ‘yanta bawa ko baiwa mumina; idan kuwa ya kasance yana cikin mutanen da kuke da yarjejeniyar zaman lafiya da su, to za a bayar da diyya wadda za a miqa wa iyalinsa, sannan za ku ‘yanta bawa ko baiwa mumina; wanda kuwa bai sami ikon haka ba, to sai ya yi azumin wata biyu a jere[1] don tuba zuwa ga Allah. Allah kuwa Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima


1- Watau sai dai idan akwai wani uzuri na rashin lafiya, ko na shari’a kamar shigowar Ramadana ko a ranar salla.


Capítulo: Suratul Ma’ida

Verso : 89

لَا يُؤَاخِذُكُمُ ٱللَّهُ بِٱللَّغۡوِ فِيٓ أَيۡمَٰنِكُمۡ وَلَٰكِن يُؤَاخِذُكُم بِمَا عَقَّدتُّمُ ٱلۡأَيۡمَٰنَۖ فَكَفَّـٰرَتُهُۥٓ إِطۡعَامُ عَشَرَةِ مَسَٰكِينَ مِنۡ أَوۡسَطِ مَا تُطۡعِمُونَ أَهۡلِيكُمۡ أَوۡ كِسۡوَتُهُمۡ أَوۡ تَحۡرِيرُ رَقَبَةٖۖ فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ ثَلَٰثَةِ أَيَّامٖۚ ذَٰلِكَ كَفَّـٰرَةُ أَيۡمَٰنِكُمۡ إِذَا حَلَفۡتُمۡۚ وَٱحۡفَظُوٓاْ أَيۡمَٰنَكُمۡۚ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمۡ ءَايَٰتِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Allah ba zai kama ku da yasassun rantse-rantsenku ba[1], sai dai Yana kama ku ne da laifin abin da kuka qudurce na rantsuwa[2]; to kaffararsa ita ce ciyar da miskinai goma daga matsakaicin abin da kuke ciyar da iyalinku ko kuma tufatar da su ko ‘yantar da bawa; wanda kuwa bai sami iko ba, to sai ya yi azumin kwana uku. Wannan shi ne kaffarar rantsuwarku, in kun yi rantsuwa. Kuma ku kiyaye rantse-rantsenku. Kamar haka ne Allah Yake bayyana muku ayoyinsa don ku zamo masu godiya


1- Yasasshiyar rantsuwa ita ce rantsuwar da mutum yake yi ba da niyya ba.


2- Watau yana kama mutum da rantsuwar da ya qudurci niyya a kanta.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 35

إِنَّ ٱلۡمُسۡلِمِينَ وَٱلۡمُسۡلِمَٰتِ وَٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ وَٱلۡقَٰنِتِينَ وَٱلۡقَٰنِتَٰتِ وَٱلصَّـٰدِقِينَ وَٱلصَّـٰدِقَٰتِ وَٱلصَّـٰبِرِينَ وَٱلصَّـٰبِرَٰتِ وَٱلۡخَٰشِعِينَ وَٱلۡخَٰشِعَٰتِ وَٱلۡمُتَصَدِّقِينَ وَٱلۡمُتَصَدِّقَٰتِ وَٱلصَّـٰٓئِمِينَ وَٱلصَّـٰٓئِمَٰتِ وَٱلۡحَٰفِظِينَ فُرُوجَهُمۡ وَٱلۡحَٰفِظَٰتِ وَٱلذَّـٰكِرِينَ ٱللَّهَ كَثِيرٗا وَٱلذَّـٰكِرَٰتِ أَعَدَّ ٱللَّهُ لَهُم مَّغۡفِرَةٗ وَأَجۡرًا عَظِيمٗا

Lalle Musulmi maza da Musulmi mata, da muminai maza da muminai mata, da masu biyayya maza da masu biyayya mata, da masu gaskiya maza da masu gaskiya mata, da masu haquri maza da masu haquri mata, da masu qasqantar da kai maza da masu qasqantar da kai mata, da masu sadaka maza da masu sadaka mata, da masu azumi maza da masu azumi mata, da maza masu kiyaye farjinsu da mata masu kiyaye farjinsu, da maza masu ambaton Allah da yawa da mata masu ambaton Allah (da yawa, dukkaninsu) Allah ya tanadar musu gafara da lada mai girma



Capítulo: Suratul Mujadila

Verso : 4

فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ شَهۡرَيۡنِ مُتَتَابِعَيۡنِ مِن قَبۡلِ أَن يَتَمَآسَّاۖ فَمَن لَّمۡ يَسۡتَطِعۡ فَإِطۡعَامُ سِتِّينَ مِسۡكِينٗاۚ ذَٰلِكَ لِتُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦۚ وَتِلۡكَ حُدُودُ ٱللَّهِۗ وَلِلۡكَٰفِرِينَ عَذَابٌ أَلِيمٌ

Sannan wanda bai samu ba, to sai ya yi azumin wata biyu a jere tun kafin su sadu; sannan wanda bai sami iko ba sai ya ciyar da miskini sittin. Wannan kuwa don ku yi imani da Allah da Manzonsa. Waxannan kuma su ne iyakokin Allah. Kafirai kuma suna da azaba mai raxaxi