يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتِيَ ٱلَّتِيٓ أَنۡعَمۡتُ عَلَيۡكُمۡ وَأَوۡفُواْ بِعَهۡدِيٓ أُوفِ بِعَهۡدِكُمۡ وَإِيَّـٰيَ فَٱرۡهَبُونِ
Ya ku ‘ya’yan Isra’ila, ku tuna ni’imata da Na yi muku, kuma ku cika alqawarina zan cika muku alkawarinku, kuma ku tsorace Ni Ni kaxai
وَءَامِنُواْ بِمَآ أَنزَلۡتُ مُصَدِّقٗا لِّمَا مَعَكُمۡ وَلَا تَكُونُوٓاْ أَوَّلَ كَافِرِۭ بِهِۦۖ وَلَا تَشۡتَرُواْ بِـَٔايَٰتِي ثَمَنٗا قَلِيلٗا وَإِيَّـٰيَ فَٱتَّقُونِ
Kuma ku yi imani da abin da Na saukar yana mai gaskata abin da yake tare da ku (na wahayi), kada kuma ku zama farkon (jinsinku) da zai kafirce masa, kuma kada ku sayar da ayoyina da xan kuxi kaxan, kuma ku kiyaye dokokina
ثُمَّ قَسَتۡ قُلُوبُكُم مِّنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ فَهِيَ كَٱلۡحِجَارَةِ أَوۡ أَشَدُّ قَسۡوَةٗۚ وَإِنَّ مِنَ ٱلۡحِجَارَةِ لَمَا يَتَفَجَّرُ مِنۡهُ ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ وَإِنَّ مِنۡهَا لَمَا يَشَّقَّقُ فَيَخۡرُجُ مِنۡهُ ٱلۡمَآءُۚ وَإِنَّ مِنۡهَا لَمَا يَهۡبِطُ مِنۡ خَشۡيَةِ ٱللَّهِۗ وَمَا ٱللَّهُ بِغَٰفِلٍ عَمَّا تَعۡمَلُونَ
Sannan sai zukatanku suka qeqashe bayan haka, suka zama kamar dutse ko ma fiye da dutse qeqashewa. Kuma lalle daga cikin duwatsu akwai waxanda qoramu suke vuvvugowa daga cikinsu; akwai kuma waxanda suke tsattsagewa ruwa ya fito daga cikinsu; akwai kuma waxanda suke faxowa saboda tsoron Allah. Allah ba marafkani ne ba game da abin da kuke aikatawa
وَمِنۡ حَيۡثُ خَرَجۡتَ فَوَلِّ وَجۡهَكَ شَطۡرَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۚ وَحَيۡثُ مَا كُنتُمۡ فَوَلُّواْ وُجُوهَكُمۡ شَطۡرَهُۥ لِئَلَّا يَكُونَ لِلنَّاسِ عَلَيۡكُمۡ حُجَّةٌ إِلَّا ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ مِنۡهُمۡ فَلَا تَخۡشَوۡهُمۡ وَٱخۡشَوۡنِي وَلِأُتِمَّ نِعۡمَتِي عَلَيۡكُمۡ وَلَعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ
Kuma duk inda ka fita, to ka juyar da fuskarka wajajen Masallaci mai alfarma. Ku ma duk inda kuke to ku juyar da fuskokinku wajajensa, don kada ya zama mutane suna da wata hujja a kanku, sai dai waxanda suka yi zalunci daga cikinsu, don haka kada ku ji tsoron su, ku ji tsorona, kuma domin in cika muku ni’imata, don ku shiriya
ٱلشَّهۡرُ ٱلۡحَرَامُ بِٱلشَّهۡرِ ٱلۡحَرَامِ وَٱلۡحُرُمَٰتُ قِصَاصٞۚ فَمَنِ ٱعۡتَدَىٰ عَلَيۡكُمۡ فَٱعۡتَدُواْ عَلَيۡهِ بِمِثۡلِ مَا ٱعۡتَدَىٰ عَلَيۡكُمۡۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ مَعَ ٱلۡمُتَّقِينَ
(Idan sun yaqe ku a) wata mai alfarma[1], (ku ma ku yaqe su a) wata mai alfarma, kuma a cikin abubuwa masu alfarma akwai qisasi. Don haka duk wanda ya yi muku ta’addanci, to ku ma ku rama ta’addancin gwargwadon yadda ya yi muku ta’addanci; kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku sani lalle Allah Yana tare da masu taqawa
1- Watanni masu alfarma huxu ne, su ne: Zulqi’ida, Zulhijja, Al-Muharram da Rajab.
ٱلۡحَجُّ أَشۡهُرٞ مَّعۡلُومَٰتٞۚ فَمَن فَرَضَ فِيهِنَّ ٱلۡحَجَّ فَلَا رَفَثَ وَلَا فُسُوقَ وَلَا جِدَالَ فِي ٱلۡحَجِّۗ وَمَا تَفۡعَلُواْ مِنۡ خَيۡرٖ يَعۡلَمۡهُ ٱللَّهُۗ وَتَزَوَّدُواْ فَإِنَّ خَيۡرَ ٱلزَّادِ ٱلتَّقۡوَىٰۖ وَٱتَّقُونِ يَـٰٓأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ
(Lokacin) hajji wasu watanni ne sanannu[1]. Don haka duk wanda ya wajabta wa kansa aikin Hajji cikin waxannan (watanni), to babu maganar saduwa da mace, kuma babu fasiqanci, kuma babu jayayya a cikin aikin Hajji. Kuma duk abin da kuka aikata na alheri, Allah Yana sane da shi. Kuma ku yi guzuri, amma mafificin guzuri shi ne taqawa, kuma ku kiyaye dokokina ya ku ma’abota hankula
1- Su ne: Shawwal da Zulqi’ida da Zulhijja.
بَلَىٰۚ مَنۡ أَوۡفَىٰ بِعَهۡدِهِۦ وَٱتَّقَىٰ فَإِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُتَّقِينَ
Ba haka ba ne, duk wanda ya cika alqawarinsa, kuma ya tsare dokar Allah, to lalle Allah Yana son masu taqawa
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ حَقَّ تُقَاتِهِۦ وَلَا تَمُوتُنَّ إِلَّا وَأَنتُم مُّسۡلِمُونَ
Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi taqawa ga Allah haqiqanin taqawa, kuma lalle kada ku mutu face kuna Musulmi
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَأۡكُلُواْ ٱلرِّبَوٰٓاْ أَضۡعَٰفٗا مُّضَٰعَفَةٗۖ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ
Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku ci riba ninki-ba-ninkin, kuma ku kiyaye dokokin Allah don ku rabauta
إِنَّمَا ذَٰلِكُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُ يُخَوِّفُ أَوۡلِيَآءَهُۥ فَلَا تَخَافُوهُمۡ وَخَافُونِ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ
Wannan (labarin), Shaixan ne kawai yake tsoratar da ku masoyansa, don haka kar ku ji tsoron su, amma ku ji tsoro Na in dai har ku muminai ne
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱصۡبِرُواْ وَصَابِرُواْ وَرَابِطُواْ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ
Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi haquri, kuma ku jure matuqa ga yin haquri, kuma ku tsare iyakokin qasa, kuma ku kiyaye dokokin Allah don ku sami rabauta
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱتَّقُواْ رَبَّكُمُ ٱلَّذِي خَلَقَكُم مِّن نَّفۡسٖ وَٰحِدَةٖ وَخَلَقَ مِنۡهَا زَوۡجَهَا وَبَثَّ مِنۡهُمَا رِجَالٗا كَثِيرٗا وَنِسَآءٗۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ ٱلَّذِي تَسَآءَلُونَ بِهِۦ وَٱلۡأَرۡحَامَۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلَيۡكُمۡ رَقِيبٗا
Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku Wanda Ya halicce ku daga rai guda xaya, kuma Ya halicci matarsa daga shi, kuma Ya yaxa maza da mata masu yawa daga gare su. Kuma ku kiyaye dokokin Allah Wanda kuke yi wa juna magiya da Shi, kuma ku kiyaye (yanke) zumunci. Lalle Allah Mai kula da ku ne
وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۗ وَلَقَدۡ وَصَّيۡنَا ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ مِن قَبۡلِكُمۡ وَإِيَّاكُمۡ أَنِ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَۚ وَإِن تَكۡفُرُواْ فَإِنَّ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ غَنِيًّا حَمِيدٗا
Kuma duk abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa na Allah ne. Kuma haqiqa Mun yi wasiyya ga waxanda Muka bai wa Littafi gabaninku da ku kanku cewa, ku ji tsoron Allah. Idan kuwa kuka kafirce, to lalle abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa duka na Allah ne. Kuma Allah Ya kasance Mawadaci ne, Sha-yabo
حُرِّمَتۡ عَلَيۡكُمُ ٱلۡمَيۡتَةُ وَٱلدَّمُ وَلَحۡمُ ٱلۡخِنزِيرِ وَمَآ أُهِلَّ لِغَيۡرِ ٱللَّهِ بِهِۦ وَٱلۡمُنۡخَنِقَةُ وَٱلۡمَوۡقُوذَةُ وَٱلۡمُتَرَدِّيَةُ وَٱلنَّطِيحَةُ وَمَآ أَكَلَ ٱلسَّبُعُ إِلَّا مَا ذَكَّيۡتُمۡ وَمَا ذُبِحَ عَلَى ٱلنُّصُبِ وَأَن تَسۡتَقۡسِمُواْ بِٱلۡأَزۡلَٰمِۚ ذَٰلِكُمۡ فِسۡقٌۗ ٱلۡيَوۡمَ يَئِسَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن دِينِكُمۡ فَلَا تَخۡشَوۡهُمۡ وَٱخۡشَوۡنِۚ ٱلۡيَوۡمَ أَكۡمَلۡتُ لَكُمۡ دِينَكُمۡ وَأَتۡمَمۡتُ عَلَيۡكُمۡ نِعۡمَتِي وَرَضِيتُ لَكُمُ ٱلۡإِسۡلَٰمَ دِينٗاۚ فَمَنِ ٱضۡطُرَّ فِي مَخۡمَصَةٍ غَيۡرَ مُتَجَانِفٖ لِّإِثۡمٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ
An haramta muku (cin) mushe da jini da naman alade da abin da aka yanka shi da sunan wanin Allah, da (dabbar) da ta shaqe, da wadda aka doke ta, da wadda ta gangaro (daga sama), da dabbar da aka tunkura da qaho, da kuma abin da namun daji masu farauta suka ci, sai dai abin da kuka samu damar yankawa (daga cikinsu), da kuma abin da aka yanka a kan gumaka, da kuma neman sanin sa’a da kibau. Wannan fasiqanci ne. A yau kafirai sun xebe tsammani daga (karya) addininku, don haka kar ku ji tsoron su, ku ji tsoro Na Ni kaxai. A yau Na cika muku addininku, kuma Na cika muku ni’imata, kuma Na yardar muku Musulunci ya zamo shi ne addininku. Duk wanda ya matsu (ya ci abin da aka ambata a baya) saboda yunwa, ba yana mai karkata zuwa ga zunubi ba, to lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai
لَئِنۢ بَسَطتَ إِلَيَّ يَدَكَ لِتَقۡتُلَنِي مَآ أَنَا۠ بِبَاسِطٖ يَدِيَ إِلَيۡكَ لِأَقۡتُلَكَۖ إِنِّيٓ أَخَافُ ٱللَّهَ رَبَّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
“Wallahi, idan har ka miqa hannunka gare ni domin ka kashe ni, ni kam ba zan miqa hannuna gare ka don in kashe ka ba; lalle ni ina jin tsoron Allah Ubangijin talikai
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱبۡتَغُوٓاْ إِلَيۡهِ ٱلۡوَسِيلَةَ وَجَٰهِدُواْ فِي سَبِيلِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ
Ya ku waxanda suka yi imani, ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku nemi abin da zai sada ku da shi, kuma ku yi jihadi wajen yaxa kalmarsa, don ku rabauta
إِنَّآ أَنزَلۡنَا ٱلتَّوۡرَىٰةَ فِيهَا هُدٗى وَنُورٞۚ يَحۡكُمُ بِهَا ٱلنَّبِيُّونَ ٱلَّذِينَ أَسۡلَمُواْ لِلَّذِينَ هَادُواْ وَٱلرَّبَّـٰنِيُّونَ وَٱلۡأَحۡبَارُ بِمَا ٱسۡتُحۡفِظُواْ مِن كِتَٰبِ ٱللَّهِ وَكَانُواْ عَلَيۡهِ شُهَدَآءَۚ فَلَا تَخۡشَوُاْ ٱلنَّاسَ وَٱخۡشَوۡنِ وَلَا تَشۡتَرُواْ بِـَٔايَٰتِي ثَمَنٗا قَلِيلٗاۚ وَمَن لَّمۡ يَحۡكُم بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَٰفِرُونَ
Lalle Mu Muka saukar da Attaura, (wadda) a cikinta akwai shiriya da haske. Annabawa waxanda suka miqa wuya suna hukunci da ita, ga waxanda suke Yahudawa, da malamai na-Allah da malamai masana, saboda abin da aka xora musu na kiyaye Littafin Allah, kuma sun kasance masu ba da shaida a kansa. Don haka kada ku ji tsoron mutane, ku ji tsoro Na Ni kaxai, kuma kada ku musanya ayoyina da wani xan farashi qanqani. Duk wanda bai yi hukunci da abin da Allah Ya saukar ba kuwa, to waxannan su ne kafirai
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَيَبۡلُوَنَّكُمُ ٱللَّهُ بِشَيۡءٖ مِّنَ ٱلصَّيۡدِ تَنَالُهُۥٓ أَيۡدِيكُمۡ وَرِمَاحُكُمۡ لِيَعۡلَمَ ٱللَّهُ مَن يَخَافُهُۥ بِٱلۡغَيۡبِۚ فَمَنِ ٱعۡتَدَىٰ بَعۡدَ ذَٰلِكَ فَلَهُۥ عَذَابٌ أَلِيمٞ
Ya ku waxanda suka yi imani, lalle Allah zai jarrabe ku da wani abu na farauta, wanda hannayenku da masunku za su kai gare shi, don Allah Ya bayyana wanda yake jin tsoron Sa alhalin bai gan Shi ba. Don haka duk wanda ya qetare iyaka bayan haka, to lalle yana da azaba mai raxaxi
وَأَنذِرۡ بِهِ ٱلَّذِينَ يَخَافُونَ أَن يُحۡشَرُوٓاْ إِلَىٰ رَبِّهِمۡ لَيۡسَ لَهُم مِّن دُونِهِۦ وَلِيّٞ وَلَا شَفِيعٞ لَّعَلَّهُمۡ يَتَّقُونَ
Kuma ka yi gargaxi da shi (Alqur’ani) ga waxanda suke jin tsoron a tattara su a gaban Ubangijinsu, ba su da wani majivincin lamari in ba Shi ba, kuma ba su da wani mai ceto, don su kiyaye dokokin Allah
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِن تَتَّقُواْ ٱللَّهَ يَجۡعَل لَّكُمۡ فُرۡقَانٗا وَيُكَفِّرۡ عَنكُمۡ سَيِّـَٔاتِكُمۡ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡۗ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ
Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka kiyaye dokokin Allah, to zai sanya muku (hanyar) tsira Ya kuma kankare muku munanan ayyukanku kuma Ya gafarta muku. Allah kuwa Ma’abocin babbar falala ne
وَإِذۡ زَيَّنَ لَهُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُ أَعۡمَٰلَهُمۡ وَقَالَ لَا غَالِبَ لَكُمُ ٱلۡيَوۡمَ مِنَ ٱلنَّاسِ وَإِنِّي جَارٞ لَّكُمۡۖ فَلَمَّا تَرَآءَتِ ٱلۡفِئَتَانِ نَكَصَ عَلَىٰ عَقِبَيۡهِ وَقَالَ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّنكُمۡ إِنِّيٓ أَرَىٰ مَا لَا تَرَوۡنَ إِنِّيٓ أَخَافُ ٱللَّهَۚ وَٱللَّهُ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ
Kuma ku tuna lokacin da Shaixan ya qawata musu ayyukansu, ya kuma ce: “Babu wasu mutane a yau da za su yi galaba a kanku, lalle kuma ni maqocinku ne.” Saboda haka lokacin da qungiyoyin biyu suka haxu sai ya tsere a guje, ya kuma ce: “Lalle ni ba ruwana da ku, lalle ni ina ganin abin da ku ba kwa gani, lalle ni ina tsoron Allah. Allah kuwa Mai tsananin azaba ne.”
أَلَا تُقَٰتِلُونَ قَوۡمٗا نَّكَثُوٓاْ أَيۡمَٰنَهُمۡ وَهَمُّواْ بِإِخۡرَاجِ ٱلرَّسُولِ وَهُم بَدَءُوكُمۡ أَوَّلَ مَرَّةٍۚ أَتَخۡشَوۡنَهُمۡۚ فَٱللَّهُ أَحَقُّ أَن تَخۡشَوۡهُ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ
Yanzu ba za ku yaqi mutanen da suka warware alqawarinsu ba, kuma (tun farko) sun yi nufin fitar da Manzo (daga Makka), su ne kuma suka fara far muku da yaqi? Yanzu kwa riqa tsoron su? To Allah ne Ya fi cancantar ku ji tsoron Sa idan kun kasance muminai
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَكُونُواْ مَعَ ٱلصَّـٰدِقِينَ
Ya ku waxanda suka yi imani, ku kiyaye dokokin Allah kuma ku zama tare da masu gaskiya
وَيُسَبِّحُ ٱلرَّعۡدُ بِحَمۡدِهِۦ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ مِنۡ خِيفَتِهِۦ وَيُرۡسِلُ ٱلصَّوَٰعِقَ فَيُصِيبُ بِهَا مَن يَشَآءُ وَهُمۡ يُجَٰدِلُونَ فِي ٱللَّهِ وَهُوَ شَدِيدُ ٱلۡمِحَالِ
Tsawa tana tsarkake (Shi) tare da gode masa, mala’iku ma (suna tasbihi) saboda tsoron Sa, Yana kuma aiko da tsawawwaki sai Ya sami wanda Ya ga dama da su, kuma su (kafirai) ga su suna jayayya game da (sha’anin) Allah. Shi kuwa Mai tsananin qarfi ne
وَٱلَّذِينَ يَصِلُونَ مَآ أَمَرَ ٱللَّهُ بِهِۦٓ أَن يُوصَلَ وَيَخۡشَوۡنَ رَبَّهُمۡ وَيَخَافُونَ سُوٓءَ ٱلۡحِسَابِ
Waxanda kuma suke sadar da abin da Allah Ya yi umarni a sadar da shi (na zumunci), suke kuma tsoron Ubangijinsu, kuma suke tsoron mummunan hisabi
يُنَزِّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ بِٱلرُّوحِ مِنۡ أَمۡرِهِۦ عَلَىٰ مَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦٓ أَنۡ أَنذِرُوٓاْ أَنَّهُۥ لَآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱتَّقُونِ
Yana saukar da mala’iku da wahayi na umarninsa ga waxanda Ya ga dama daga bayinsa da cewa,: “Ku yi gargaxi cewa,, lalle ba wani abin bauta sai Ni, to sai ku kiyaye dokokina.”
وَلِلَّهِۤ يَسۡجُدُۤ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ مِن دَآبَّةٖ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَهُمۡ لَا يَسۡتَكۡبِرُونَ
Abin da yake cikin sammai da abin da yake bayan qasa na kowace dabba da mala’iku suna yin sujjada ne ga Allah, su kuma ba sa girman kai
يَخَافُونَ رَبَّهُم مِّن فَوۡقِهِمۡ وَيَفۡعَلُونَ مَا يُؤۡمَرُونَ۩
Suna tsoron Ubangijnsu daga samansu kuma suna aikata abin da ake umartar su da shi
۞وَقَالَ ٱللَّهُ لَا تَتَّخِذُوٓاْ إِلَٰهَيۡنِ ٱثۡنَيۡنِۖ إِنَّمَا هُوَ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞ فَإِيَّـٰيَ فَٱرۡهَبُونِ
Allah kuma Ya ce: “Kada ku riqi abubuwan bauta guda biyu[1]. Abin bauta Xaya Yake Tilo; to sai ku ji tsoro na Ni kaxai.”
1- Watau kamar Majusawa masu cewa, wai akwai ubangijin alheri shi ne haske, akwai kuma na sharri shi ne duhu.
يَعۡلَمُ مَا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُمۡ وَلَا يَشۡفَعُونَ إِلَّا لِمَنِ ٱرۡتَضَىٰ وَهُم مِّنۡ خَشۡيَتِهِۦ مُشۡفِقُونَ
Yana sane da ayyukansu da suka gabatar da na nan gaba, ba kuma za su yi ceto ba sai ga wanda Ya yarda (daga bayinsa), suna kuwa masu kaffa-kaffa don tsoron Sa