Capítulo: Suratun Namli

Verso : 64

أَمَّن يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥ وَمَن يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِۗ أَءِلَٰهٞ مَّعَ ٱللَّهِۚ قُلۡ هَاتُواْ بُرۡهَٰنَكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Ko kuwa wane ne yake qagar halitta sannan ya dawo da ita (bayan mutuwa), kuma wane ne yake arzuta ku ta sama da qasa? Shin akwai wani abin bauta da gaskiya tare da Allah?” Ka ce (da su): “Ku kawo dalilinku idan kun kasance masu gaskiya.”



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 65

قُل لَّا يَعۡلَمُ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ ٱلۡغَيۡبَ إِلَّا ٱللَّهُۚ وَمَا يَشۡعُرُونَ أَيَّانَ يُبۡعَثُونَ

Ka ce (da su): “Duk wanda yake cikin sammai da qasa in ba Allah ba ba wanda ya san gaibu. Su kuma ba su san lokacin da za a tashe su ba.”



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 73

وَإِنَّ رَبَّكَ لَذُو فَضۡلٍ عَلَى ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَشۡكُرُونَ

Kuma lalle Ubangijinka Mai falala ne ga mutane, sai dai kuma yawancinsu ba sa godewa



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 74

وَإِنَّ رَبَّكَ لَيَعۡلَمُ مَا تُكِنُّ صُدُورُهُمۡ وَمَا يُعۡلِنُونَ

Lalle kuma Ubangijinka tabbas Yana sane da abin da zukatansu suke voyewa, da kuma abin da suke bayyanawa



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 79

فَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِۖ إِنَّكَ عَلَى ٱلۡحَقِّ ٱلۡمُبِينِ

To ka dogara ga Allah; lalle kai kana kan gaskiya mabayyaniya



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 88

وَتَرَى ٱلۡجِبَالَ تَحۡسَبُهَا جَامِدَةٗ وَهِيَ تَمُرُّ مَرَّ ٱلسَّحَابِۚ صُنۡعَ ٱللَّهِ ٱلَّذِيٓ أَتۡقَنَ كُلَّ شَيۡءٍۚ إِنَّهُۥ خَبِيرُۢ بِمَا تَفۡعَلُونَ

Kuma za ka ga duwatsu ka zaci a tsaye suke cak, alhali kuwa su suna tafiya ne irin tafiyar gizagizai. Aikin Allah kenan wanda Ya kyautata halittar kowane irin abu. Lalle Shi Masanin abin da kuke aikatawa ne



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 46

وَمَا كُنتَ بِجَانِبِ ٱلطُّورِ إِذۡ نَادَيۡنَا وَلَٰكِن رَّحۡمَةٗ مِّن رَّبِّكَ لِتُنذِرَ قَوۡمٗا مَّآ أَتَىٰهُم مِّن نَّذِيرٖ مِّن قَبۡلِكَ لَعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ

Kuma ba ka kasance a gefen (dutsen) Xuri ba, lokacin da Muka kirawo (Musa), sai dai wata rahama daga Ubangijinka, don ka gargaxi wasu mutane da mai gargaxi bai zo musu ba gabaninka ko sa wa’azantu



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 56

إِنَّكَ لَا تَهۡدِي مَنۡ أَحۡبَبۡتَ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ يَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ

Lalle kai ba ka iya shiryar da wanda ka so, sai dai Allah ne Yana shiryar da wanda Ya ga dama. Shi kuma ne Ya san masu shiryuwa



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 57

وَقَالُوٓاْ إِن نَّتَّبِعِ ٱلۡهُدَىٰ مَعَكَ نُتَخَطَّفۡ مِنۡ أَرۡضِنَآۚ أَوَلَمۡ نُمَكِّن لَّهُمۡ حَرَمًا ءَامِنٗا يُجۡبَىٰٓ إِلَيۡهِ ثَمَرَٰتُ كُلِّ شَيۡءٖ رِّزۡقٗا مِّن لَّدُنَّا وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Suka kuma ce: “Idan har Muka bi shiriya tare da kai, to za a kame mu (ribatattu) daga qasarmu[1]”. (Ka ce da su): “Yanzu ashe ba Mu ne Muka ba su ikon Harami amintacce ba da ake kawo kowanne irin (nau’i) na ‘ya’yan itace gare shi don arzutawa daga gare Mu?” Sai dai kuma yawancinsu ba sa sanin (haka)


1- Watau za a fincike su daga qasarsu Makka, su zama ribatattun yaqi a hannun maqiyansu.


Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 58

وَكَمۡ أَهۡلَكۡنَا مِن قَرۡيَةِۭ بَطِرَتۡ مَعِيشَتَهَاۖ فَتِلۡكَ مَسَٰكِنُهُمۡ لَمۡ تُسۡكَن مِّنۢ بَعۡدِهِمۡ إِلَّا قَلِيلٗاۖ وَكُنَّا نَحۡنُ ٱلۡوَٰرِثِينَ

Kuma al’umma nawa ce Muka hallakar wadda ta butulce wa rayuwarta? To ga gidajensu can ba a zaune su ba a bayansu sai kaxan[1]; Mu ne Muka kasance magadan


1- Watau daga matafiya da sukan ya da zango su zauna na xan lokaci.


Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 68

وَرَبُّكَ يَخۡلُقُ مَا يَشَآءُ وَيَخۡتَارُۗ مَا كَانَ لَهُمُ ٱلۡخِيَرَةُۚ سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ وَتَعَٰلَىٰ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Kuma Ubangijinka Yana halittar abin da Ya ga dama Yana kuma zavar (abin da Ya ga dama). Ba su suke da zavi ba. Tsarki ya tabbata ga Allah kuma Ya xaukaka daga abin da suke yin shirka (da shi)



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 69

وَرَبُّكَ يَعۡلَمُ مَا تُكِنُّ صُدُورُهُمۡ وَمَا يُعۡلِنُونَ

Kuma Ubangijinka Ya san abin da zukatansu suke voyewa da kuma abin da suke bayyanawa



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 73

وَمِن رَّحۡمَتِهِۦ جَعَلَ لَكُمُ ٱلَّيۡلَ وَٱلنَّهَارَ لِتَسۡكُنُواْ فِيهِ وَلِتَبۡتَغُواْ مِن فَضۡلِهِۦ وَلَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Daga rahamarsa ne kuma Ya sanya muku dare da rana don ku samu nutsuwa a cikinsa (wato dare) kuma don ku nema daga falalarsa (da rana), don kuma ku riqa yin godiya



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 85

إِنَّ ٱلَّذِي فَرَضَ عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ لَرَآدُّكَ إِلَىٰ مَعَادٖۚ قُل رَّبِّيٓ أَعۡلَمُ مَن جَآءَ بِٱلۡهُدَىٰ وَمَنۡ هُوَ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Lalle Wanda Ya saukar maka da Alqur’ani tabbas zai mayar da kai zuwa makomarka[1]. Ka ce: “Ubangijina Shi Ya san wanda ya zo da shiriya da kuma wanda yake cikin vata mabayyani.”


1- Watau zai mayar da shi mahaifarsa garin Makka; ko kuma zai mayar da shi makomarsa ta qarshe watau Aljanna.


Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 88

وَلَا تَدۡعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَۘ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۚ كُلُّ شَيۡءٍ هَالِكٌ إِلَّا وَجۡهَهُۥۚ لَهُ ٱلۡحُكۡمُ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Kuma kada ka bauta wa wani abin bauta daban tare da Allah. Babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Kowane abu mai halaka ne sai Fuskarsa kawai. Hukunci (duk) nasa ne, zuwa gare Shi kuma za a mayar da ku



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 10

وَمِنَ ٱلنَّاسِ مَن يَقُولُ ءَامَنَّا بِٱللَّهِ فَإِذَآ أُوذِيَ فِي ٱللَّهِ جَعَلَ فِتۡنَةَ ٱلنَّاسِ كَعَذَابِ ٱللَّهِۖ وَلَئِن جَآءَ نَصۡرٞ مِّن رَّبِّكَ لَيَقُولُنَّ إِنَّا كُنَّا مَعَكُمۡۚ أَوَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَعۡلَمَ بِمَا فِي صُدُورِ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma cikin mutane akwai mai cewa: “Mun yi imani da Allah,” to idan aka cuce shi a kan hanyar Allah sai yakan xauki fitinar mutane kamar azabar Allah, lalle kuwa idan wata nasara ta zo daga Ubangijinka, tabbas zai riqa cewa: “Lalle mu mun kasance tare da ku.” Yanzu Allah ba Shi Ya fi kowa sanin abin da ke cikin zukatan talikai ba?



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 17

إِنَّمَا تَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ أَوۡثَٰنٗا وَتَخۡلُقُونَ إِفۡكًاۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ تَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ لَا يَمۡلِكُونَ لَكُمۡ رِزۡقٗا فَٱبۡتَغُواْ عِندَ ٱللَّهِ ٱلرِّزۡقَ وَٱعۡبُدُوهُ وَٱشۡكُرُواْ لَهُۥٓۖ إِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Lalle abin da kuke bauta wa ba Allah ba gumaka ne kawai, kuna kuma qirqirar qarya ne[1]. Lalle waxanda kuke bauta wa ba Allah ba, ba su mallaki wani arziki ba gare ku, sai ku nemi arziki a wurin Allah, kuma ku bauta masa, ku kuma gode masa; gare Shi ne kawai za a mayar da ku


1- Domin su ne suke sassaqa su da hannayensu suke kuma sanya musu sunaye sannan su bauta musu.


Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 19

أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ كَيۡفَ يُبۡدِئُ ٱللَّهُ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥٓۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ

Yanzu ba su ga yadda Allah Yake farar halitta ba, sannan Shi ne kuma zai mayar da ita? Lalle wannan mai sauqi ne a wurin Allah



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 20

قُلۡ سِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَٱنظُرُواْ كَيۡفَ بَدَأَ ٱلۡخَلۡقَۚ ثُمَّ ٱللَّهُ يُنشِئُ ٱلنَّشۡأَةَ ٱلۡأٓخِرَةَۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Ka ce: “Ku yi tafiya a bayan qasa sai ku duba ku ga yadda Allah Ya fari halittu. Sannan Allah ne zai sake samar da su samarwar qarshe. Lalle Allah Mai iko ne a kan komai



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 42

إِنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ مَا يَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ مِن شَيۡءٖۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Lalle Allah Yana sane da kowane abu da suke bauta wa wanda ba Shi ba. Kuma Shi ne Mabuwayi, Mai hikima



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 45

ٱتۡلُ مَآ أُوحِيَ إِلَيۡكَ مِنَ ٱلۡكِتَٰبِ وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَۖ إِنَّ ٱلصَّلَوٰةَ تَنۡهَىٰ عَنِ ٱلۡفَحۡشَآءِ وَٱلۡمُنكَرِۗ وَلَذِكۡرُ ٱللَّهِ أَكۡبَرُۗ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ مَا تَصۡنَعُونَ

Ka karanta abin da ake yi maka wahayinsa na Alqur’ani, ka kuma tsai da salla; lalle salla tana hana alfasha da kuma abin qi. Kuma tabbas ambaton Allah shi ne mafi girma. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 46

۞وَلَا تُجَٰدِلُوٓاْ أَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ إِلَّا بِٱلَّتِي هِيَ أَحۡسَنُ إِلَّا ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ مِنۡهُمۡۖ وَقُولُوٓاْ ءَامَنَّا بِٱلَّذِيٓ أُنزِلَ إِلَيۡنَا وَأُنزِلَ إِلَيۡكُمۡ وَإِلَٰهُنَا وَإِلَٰهُكُمۡ وَٰحِدٞ وَنَحۡنُ لَهُۥ مُسۡلِمُونَ

Kuma kada ku yi jayayya da ma’abota littafi (Yahudu da Nasara) sai ta hanyar da ta fi kyau, sai dai waxanda suka yi zalunci daga cikinsu; kuma ku ce: “Mun yi imani da abin da aka saukar mana da kuma abin da aka saukar muku, kuma Abin bautarmu da Abin bautarku Xaya ne, kuma mu masu miqa wuya ne gare Shi.”



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 52

قُلۡ كَفَىٰ بِٱللَّهِ بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡ شَهِيدٗاۖ يَعۡلَمُ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۗ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱلۡبَٰطِلِ وَكَفَرُواْ بِٱللَّهِ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Ka ce (da su): “Allah Ya isa shaida tsakanina da ku; Yana sane da abin da yake cikin sammai da qasa. Waxanda kuwa suka yi imani da qarya suka kuma kafirce wa Allah, waxannan su ne asararru.”



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 59

ٱلَّذِينَ صَبَرُواْ وَعَلَىٰ رَبِّهِمۡ يَتَوَكَّلُونَ

(Su ne) waxanda suka yi haquri, kuma ga Ubangijinsu kawai suke dogara



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 60

وَكَأَيِّن مِّن دَآبَّةٖ لَّا تَحۡمِلُ رِزۡقَهَا ٱللَّهُ يَرۡزُقُهَا وَإِيَّاكُمۡۚ وَهُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Sau tari ga dabba nan da ba za ta iya xaukar arzikinta ba, Allah ne Yake arzuta ta har da ku. Shi ne Mai ji, Masani



Capítulo: Suratul Ankabut

Verso : 62

ٱللَّهُ يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦ وَيَقۡدِرُ لَهُۥٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Allah Yana shimfixa arziki ga wanda Ya ga dama daga bayinsa, Ya kuma quntata masa. Lalle Allah Masanin komai ne



Capítulo: Suratur Rum

Verso : 5

بِنَصۡرِ ٱللَّهِۚ يَنصُرُ مَن يَشَآءُۖ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Da samun nasar Allah (a kan Farisa). Shi Yake taimakon wanda Ya ga dama; domin kuwa Shi ne Mabuwayi, Mai rahama



Capítulo: Suratur Rum

Verso : 11

ٱللَّهُ يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥ ثُمَّ إِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Allah ne Yake farar halitta sannan Ya dawo da ita (bayan mutuwa), sannan kuma gare Shi za a komar da ku



Capítulo: Suratur Rum

Verso : 19

يُخۡرِجُ ٱلۡحَيَّ مِنَ ٱلۡمَيِّتِ وَيُخۡرِجُ ٱلۡمَيِّتَ مِنَ ٱلۡحَيِّ وَيُحۡيِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَاۚ وَكَذَٰلِكَ تُخۡرَجُونَ

Yana fitar da rayayye daga matacce, Yana kuma fitar da matacce daga rayayye, kuma Yana raya qasa bayan mutuwarta. Kamar haka ne kuma za a fito da ku (daga qaburburanku)



Capítulo: Suratur Rum

Verso : 20

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦٓ أَنۡ خَلَقَكُم مِّن تُرَابٖ ثُمَّ إِذَآ أَنتُم بَشَرٞ تَنتَشِرُونَ

Yana daga ayoyinsa cewa Ya halicce ku daga turvaya, sannan kuma sai ga ku mutane kun warwatsu (a ko’ina)