يَعۡلَمُ مَا يَلِجُ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا يَخۡرُجُ مِنۡهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ وَمَا يَعۡرُجُ فِيهَاۚ وَهُوَ ٱلرَّحِيمُ ٱلۡغَفُورُ
Yana sane da abin da yake shiga cikin qasa da abin da yake fitowa daga cikinta, da kuma abin da yake sauka daga sama da abin da yake hawa cikinta. Kuma Shi Mai rahama ne, Mai gafara
۞قُلۡ مَن يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ قُلِ ٱللَّهُۖ وَإِنَّآ أَوۡ إِيَّاكُمۡ لَعَلَىٰ هُدًى أَوۡ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ
Ka ce: “Wane ne yake arzuta ku daga sammai da qasa?” Ka ce: “Allah ne; kuma mu ko ku (xaya daga cikinmu) lalle yana a kan shiriya ko kuma yana cikin vata mabayyani.”
قُلۡ إِنَّ رَبِّي يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ وَيَقۡدِرُ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ
Ka ce: “Lalle Ubangijina Yana shimfixa arziki ga wanda Ya ga dama, Ya kuma quntata, sai dai kuma yawancin mutane ba su san (haka) ba.”
قُلۡ إِنَّ رَبِّي يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦ وَيَقۡدِرُ لَهُۥۚ وَمَآ أَنفَقۡتُم مِّن شَيۡءٖ فَهُوَ يُخۡلِفُهُۥۖ وَهُوَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰزِقِينَ
Ka ce: “Lalle Ubangijna Yana shimfixa arziki ga wanda ya ga dama cikin bayinsa, Yana kuma quntata masa. Kuma duk abin da kuka ciyar (don Allah), to Shi ne zai ba ku madadinsa, Shi ne kuwa Fiyayyen masu arzutawa.”
ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ فَاطِرِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ جَاعِلِ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ رُسُلًا أُوْلِيٓ أَجۡنِحَةٖ مَّثۡنَىٰ وَثُلَٰثَ وَرُبَٰعَۚ يَزِيدُ فِي ٱلۡخَلۡقِ مَا يَشَآءُۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ
Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Mahaliccin sammai da qasa Mai sanya mala’iku manzanni masu fukafukai bibbiyu da masu uku-uku da kuma masu huxu-huxu. Yakan kuma qara abin da Ya ga dama ga halittar[1]. Lalle Allah Mai iko ne a kan komai
1- Don haka akwai mala’iku masu fukafukai fiye da huxu, ya kuma qara wa wanda ya ga dama kyau ko wata gava.
مَّا يَفۡتَحِ ٱللَّهُ لِلنَّاسِ مِن رَّحۡمَةٖ فَلَا مُمۡسِكَ لَهَاۖ وَمَا يُمۡسِكۡ فَلَا مُرۡسِلَ لَهُۥ مِنۢ بَعۡدِهِۦۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ
Abin da Allah Yake yi wa mutane buxi da shi na rahama ba mai iya riqe shi; abin da kuma Yake riqewa ba mai iya sakin sa bayansa. Shi kuma Mabuwayi ne, Mai hikima
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡۚ هَلۡ مِنۡ خَٰلِقٍ غَيۡرُ ٱللَّهِ يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِۚ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ فَأَنَّىٰ تُؤۡفَكُونَ
Ya ku mutane, ku tuna ni’imar Allah a gare ku. Yanzu akwai wani mahalicci ban da Allah wanda zai arzuta ku daga sama da qasa? Babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. To ta yaya ake karkatar da ku?
أَفَمَن زُيِّنَ لَهُۥ سُوٓءُ عَمَلِهِۦ فَرَءَاهُ حَسَنٗاۖ فَإِنَّ ٱللَّهَ يُضِلُّ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۖ فَلَا تَذۡهَبۡ نَفۡسُكَ عَلَيۡهِمۡ حَسَرَٰتٍۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِمَا يَصۡنَعُونَ
Yanzu wanda aka qawata wa mummunan aikinsa ya gan shi kyakkyawa (zai yi daidai da wanda Allah Ya shiryar)? To lalle Allah Yana vatar da wanda Ya ga dama Ya shiryi wanda Ya ga dama; saboda haka kada ka halakar da kanka don baqin ciki game da su. Lalle Allah Masanin abin da suke aikatawa ne
مَن كَانَ يُرِيدُ ٱلۡعِزَّةَ فَلِلَّهِ ٱلۡعِزَّةُ جَمِيعًاۚ إِلَيۡهِ يَصۡعَدُ ٱلۡكَلِمُ ٱلطَّيِّبُ وَٱلۡعَمَلُ ٱلصَّـٰلِحُ يَرۡفَعُهُۥۚ وَٱلَّذِينَ يَمۡكُرُونَ ٱلسَّيِّـَٔاتِ لَهُمۡ عَذَابٞ شَدِيدٞۖ وَمَكۡرُ أُوْلَـٰٓئِكَ هُوَ يَبُورُ
Wanda ya zamanto yana nufin xaukaka, to xaukaka gaba xayanta ta Allah ce. Daxaxan kalmomi[1] zuwa wurinsa suke hawa, kyakkyawan aiki kuwa shi yake xaukaka shi. Waxanda kuwa suke shirya makirci suna da (sakamakon) azaba mai tsanani, kuma makircin waxannan shi ne yake lalacewa
1- Watau kamar kalmar shahada da karatun Alqur’ani da ambaton Allah.
وَٱللَّهُ خَلَقَكُم مِّن تُرَابٖ ثُمَّ مِن نُّطۡفَةٖ ثُمَّ جَعَلَكُمۡ أَزۡوَٰجٗاۚ وَمَا تَحۡمِلُ مِنۡ أُنثَىٰ وَلَا تَضَعُ إِلَّا بِعِلۡمِهِۦۚ وَمَا يُعَمَّرُ مِن مُّعَمَّرٖ وَلَا يُنقَصُ مِنۡ عُمُرِهِۦٓ إِلَّا فِي كِتَٰبٍۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ
Kuma Allah Ya halicce ku ne daga turvaya sannan daga maniyyi, sannan kuma Ya mayar da ku maza da mata. Kuma mace ba za ta xauki ciki ba, ba kuma za ta haifu ba sai da saninsa. Ba kuma wani mai tsawon rai da za a raya shi, ko kuma wani da za a rage tsawon ransa face yana (rubuce) a cikin Lauhul-Mahafuzu. Wannan kuwa a wurin Allah mai sauqi ne
يُولِجُ ٱلَّيۡلَ فِي ٱلنَّهَارِ وَيُولِجُ ٱلنَّهَارَ فِي ٱلَّيۡلِ وَسَخَّرَ ٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَۖ كُلّٞ يَجۡرِي لِأَجَلٖ مُّسَمّٗىۚ ذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبُّكُمۡ لَهُ ٱلۡمُلۡكُۚ وَٱلَّذِينَ تَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ مَا يَمۡلِكُونَ مِن قِطۡمِيرٍ
Yana shigar da dare cikin yini, Yana kuma shigar da yini cikin dare, Ya kuma hore rana da wata kowannensu yana tafiya zuwa ga ajali iyakantacce. (Mai yin wannan kuwa) Shi ne Allah Ubangijinku, mulki (kuwa) nasa ne. Waxanda kuwa kuke bauta wa ba Shi ba, ba su mallaki ko da rigar qwallon dabino ba
إِن يَشَأۡ يُذۡهِبۡكُمۡ وَيَأۡتِ بِخَلۡقٖ جَدِيدٖ
Idan Ya ga dama sai Ya tafiyar da ku Ya kawo wata sabuwar halittar
وَٱلَّذِيٓ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ مِنَ ٱلۡكِتَٰبِ هُوَ ٱلۡحَقُّ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِۗ إِنَّ ٱللَّهَ بِعِبَادِهِۦ لَخَبِيرُۢ بَصِيرٞ
Kuma abin da Muka yiwo maka wahayinsa na Littafi shi ne gaskiya, yana gaskata abin da yake gabaninsa (na littattafai). Lalle Allah game da bayinsa Masani ne, Mai gani
إِنَّ ٱللَّهَ عَٰلِمُ غَيۡبِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ إِنَّهُۥ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ
Lalle Allah Masanin gaibin sammai da qasa ne. Lalle Shi Masanin abubuwan da suke cikin zukata ne
هُوَ ٱلَّذِي جَعَلَكُمۡ خَلَـٰٓئِفَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ فَمَن كَفَرَ فَعَلَيۡهِ كُفۡرُهُۥۖ وَلَا يَزِيدُ ٱلۡكَٰفِرِينَ كُفۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ إِلَّا مَقۡتٗاۖ وَلَا يَزِيدُ ٱلۡكَٰفِرِينَ كُفۡرُهُمۡ إِلَّا خَسَارٗا
Shi ne wanda Ya sanya ku halifofi a bayan qasa. Saboda haka wanda ya kafirta sakamakon kafircinsa yana kansa, kuma kafircin kafirai ba zai qara musu komai ba a wurin Ubangijinsu sai qiyayya; kuma kafircin kafirai ba zai qara musu komai ba sai hasara
۞إِنَّ ٱللَّهَ يُمۡسِكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ أَن تَزُولَاۚ وَلَئِن زَالَتَآ إِنۡ أَمۡسَكَهُمَا مِنۡ أَحَدٖ مِّنۢ بَعۡدِهِۦٓۚ إِنَّهُۥ كَانَ حَلِيمًا غَفُورٗا
Lalle Allah ne Yake riqe da sammai da qasa don kada su ruguje. Lallai kuwa idan da za su ruguje, to ba wani mai riqe su in ba Shi ba. Lalle Shi (Allah) Ya kasance Mai haquri ne, Mai gafara
أَوَلَمۡ يَسِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَيَنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ وَكَانُوٓاْ أَشَدَّ مِنۡهُمۡ قُوَّةٗۚ وَمَا كَانَ ٱللَّهُ لِيُعۡجِزَهُۥ مِن شَيۡءٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَلِيمٗا قَدِيرٗا
Shin ba su yi tafiya ba ne a cikin qasa, sai su ga yaya qarshen waxanda suke gabaninsu ya kasance, alhali kuwa sun zamanto qarfafa fiye da su? Ba kuwa wani abu da zai gagari Allah a cikin sammai ko a cikin qasa. Lalle Shi Ya kasance Masani ne, Mai iko
وَلَوۡ يُؤَاخِذُ ٱللَّهُ ٱلنَّاسَ بِمَا كَسَبُواْ مَا تَرَكَ عَلَىٰ ظَهۡرِهَا مِن دَآبَّةٖ وَلَٰكِن يُؤَخِّرُهُمۡ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗىۖ فَإِذَا جَآءَ أَجَلُهُمۡ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِعِبَادِهِۦ بَصِيرَۢا
Idan da Allah Yana (saurin) damqar mutane saboda laifin da suka aikata, to da bai bar kowane mai rai ba a bayan qasa, sai dai kuma Yana saurara musu ne zuwa wani lokaci qayyadajje; to idan lokacin nasu ya zo, to lalle Allah Ya kasance Mai ganin bayinsa ne, (zai kuwa saka musu)
إِنِّيٓ ءَامَنتُ بِرَبِّكُمۡ فَٱسۡمَعُونِ
“Lalle ni na yi imani da Ubangijinku, sai ku saurare ni.”
فَلَا يَحۡزُنكَ قَوۡلُهُمۡۘ إِنَّا نَعۡلَمُ مَا يُسِرُّونَ وَمَا يُعۡلِنُونَ
To kada maganarsu ta baqanta maka. Lalle Mu Muna sane da abin da suke voyewa da kuma abin da suke bayyanawa
أَوَلَمۡ يَرَ ٱلۡإِنسَٰنُ أَنَّا خَلَقۡنَٰهُ مِن نُّطۡفَةٖ فَإِذَا هُوَ خَصِيمٞ مُّبِينٞ
Yanzu mutum ba ya gani cewa Mu Muka halicce shi daga maniyyi, sai ga shi ya zama mai jayayya a fili?
وَضَرَبَ لَنَا مَثَلٗا وَنَسِيَ خَلۡقَهُۥۖ قَالَ مَن يُحۡيِ ٱلۡعِظَٰمَ وَهِيَ رَمِيمٞ
Ya kuma buga mana misali, kuma ya manta da halittarsa (yayin da) ya ce: “Wane ne zai raya qasusuwa, alhali kuma sun rududduge?
قُلۡ يُحۡيِيهَا ٱلَّذِيٓ أَنشَأَهَآ أَوَّلَ مَرَّةٖۖ وَهُوَ بِكُلِّ خَلۡقٍ عَلِيمٌ
Ka ce: “Wannan da Ya fare su tun farko Shi ne zai raya su; Shi kuwa Masanin kowacce irin halitta ne
ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُم مِّنَ ٱلشَّجَرِ ٱلۡأَخۡضَرِ نَارٗا فَإِذَآ أَنتُم مِّنۡهُ تُوقِدُونَ
“Wanda kuma Ya samar muku wuta daga koriyar bishiya, sai ga shi kuna hura wuta daga gare ta.”
أَوَلَيۡسَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يَخۡلُقَ مِثۡلَهُمۚ بَلَىٰ وَهُوَ ٱلۡخَلَّـٰقُ ٱلۡعَلِيمُ
Yanzu wanda Ya halacci sammai da qasa ba zai zama Mai ikon halitta irinsu ba? Ai tabbas zai iya, kuma Shi ne Mai yawan yin halitta, Masani
إِنَّمَآ أَمۡرُهُۥٓ إِذَآ أَرَادَ شَيۡـًٔا أَن يَقُولَ لَهُۥ كُن فَيَكُونُ
Umarninsa kawai idan Ya yi nufin wani abu sai Ya ce da shi: “Kasance”, sai ya kasance
فَسُبۡحَٰنَ ٱلَّذِي بِيَدِهِۦ مَلَكُوتُ كُلِّ شَيۡءٖ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ
To tsarki ya tabbata ga wanda mulkin kowane abu yake a hannunsa, kuma wurinsa ne kawai za a komar da ku
إِنَّ إِلَٰهَكُمۡ لَوَٰحِدٞ
Lalle Ubangiijnku tabbas Xaya ne
وَٱللَّهُ خَلَقَكُمۡ وَمَا تَعۡمَلُونَ
“Alhali kuwa Allah ne Ya halicce ku, da ma abin da kuke aikatawa?”
أَمۡ عِندَهُمۡ خَزَآئِنُ رَحۡمَةِ رَبِّكَ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡوَهَّابِ
Ko kuwa a wurinsu ne taskokin rahamar Ubangijinka Mabuwayi Mai baiwa suke?