Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 47

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلۡيَقِينُ

“Har mutuwa ta zo mana.”



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 48

فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ

Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane su ba



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 49

فَمَا لَهُمۡ عَنِ ٱلتَّذۡكِرَةِ مُعۡرِضِينَ

To me ya same su ne suke bijire wa wa’azi?



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 50

كَأَنَّهُمۡ حُمُرٞ مُّسۡتَنفِرَةٞ

Kai ka ce su jakunan jeji ne da aka firgitar



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 51

فَرَّتۡ مِن قَسۡوَرَةِۭ

Da suka guje wa zaki



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 52

بَلۡ يُرِيدُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُؤۡتَىٰ صُحُفٗا مُّنَشَّرَةٗ

A’a, kowane mutum daga cikinsu yana so ne a ba shi takardu buxaxxu[1] (kafin su bi Annabi)


1- Watau a ba shi buxaxxen littafi wanda zai ba shi labari cewa Annabi Muhammadu () Manzon Allah ne.


Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 53

كَلَّاۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ

Faufau! A’a, su dai ba sa tsoron ranar lahira ne



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 54

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذۡكِرَةٞ

Tabbas, lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 55

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

To duk wanda ya ga dama sai ya wa’azantu



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 56

وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ

Ba sa kuma wa’azantuwa sai idan Allah Ya ga dama. Shi ne Ya cancanci taqawa, kuma Shi ne Ya cancanci yin gafara



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 1

لَآ أُقۡسِمُ بِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Ina rantsuwa da ranar alqiyama



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 2

وَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلنَّفۡسِ ٱللَّوَّامَةِ

Ina kuma rantsuwa da rai mai yawan zargin (kansa)[1]


1- Watau a kan gazawarsa wajen ayyukan alheri ko a kan aikata laifuka.


Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 3

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ

Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ

E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 5

بَلۡ يُرِيدُ ٱلۡإِنسَٰنُ لِيَفۡجُرَ أَمَامَهُۥ

Ba haka ba ne, mutum yana nufi ne kawai ya gurvata gabansa (da savon Allah)



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 6

يَسۡـَٔلُ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Yana tambaya yaushe ne ranar alqiyamar?



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 7

فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ

To lokacin da gani ya ruxe



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 8

وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ

Wata kuma ya yi duhu



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 9

وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ

Aka kuma haxe rana da wata (a mafitarsu)



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 10

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ

A wannan rana ne mutum zai ce: “Ina wurin gudu?”



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 11

كَلَّا لَا وَزَرَ

Faufau, babu mafaka



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ

Zuwa ga Ubangijinka ne kawai matabbata take a wannan rana



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 13

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

Za a bai wa mutum labari a wannan rana na abin da ya gabatar da kuma (abin da) ya jinkirtar (na ayyukansa)



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 14

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ

A’a, shi dai mutum mai shaida ne a kan kansa



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 15

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

Ko da kuwa ya kawo uzururrukansa



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 16

لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ

(Allah ya ce da Annabinsa): Kada ka motsa harshenka da shi (Alqur’ani) don gaggauta (karanta) shi



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 17

إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ

Lalle tattara shi (a zuciyarka) da karanta shi yana kanmu



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 18

فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ

Saboda haka idan Muka karanta (maka) shi sai ka bi karatunsa



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 19

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ

Sannan kuma bayaninsa yana kanmu



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 20

كَلَّا بَلۡ تُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ

Haba, ku dai kawai kuna son duniya ne