Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 61

مَّلۡعُونِينَۖ أَيۡنَمَا ثُقِفُوٓاْ أُخِذُواْ وَقُتِّلُواْ تَقۡتِيلٗا

(Su) la’anannu ne; duk inda aka gamu da su a kama su, kuma a yi musu mummunan kisa



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 62

سُنَّةَ ٱللَّهِ فِي ٱلَّذِينَ خَلَوۡاْ مِن قَبۡلُۖ وَلَن تَجِدَ لِسُنَّةِ ٱللَّهِ تَبۡدِيلٗا

(Wannan) Sunnar Allah ce ga waxanda suka gabata a da; ba kuma za ka sami wani canji ba game da sunnar Allah



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 63

يَسۡـَٔلُكَ ٱلنَّاسُ عَنِ ٱلسَّاعَةِۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ ٱللَّهِۚ وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّ ٱلسَّاعَةَ تَكُونُ قَرِيبًا

Mutane suna tambayar ka game da (ranar) alqiyama; ka ce (da su): “Saninta a wajen Allah kawai yake.” Ba ka sani ba ko watakila alqiyamar za ta kasance kusa



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 64

إِنَّ ٱللَّهَ لَعَنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ وَأَعَدَّ لَهُمۡ سَعِيرًا

Lalle Allah Ya la’anci kafirai Ya kuma tanadar musu da (wutar) Sa’ira



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 65

خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ لَّا يَجِدُونَ وَلِيّٗا وَلَا نَصِيرٗا

Masu dawwama ne a cikinta har abada; ba kuma za su sami wani majivinci ko mataimaki ba



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 66

يَوۡمَ تُقَلَّبُ وُجُوهُهُمۡ فِي ٱلنَّارِ يَقُولُونَ يَٰلَيۡتَنَآ أَطَعۡنَا ٱللَّهَ وَأَطَعۡنَا ٱلرَّسُولَا۠

A ranar da za a riqa jujjuya fuskokinsu cikin wuta, suna cewa: “Kaiconmu, ina ma da mun bi Allah mun bi Manzo!”



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 67

وَقَالُواْ رَبَّنَآ إِنَّآ أَطَعۡنَا سَادَتَنَا وَكُبَرَآءَنَا فَأَضَلُّونَا ٱلسَّبِيلَا۠

Suka kuma ce: “Ya Ubangijinmu, lalle mu mun bi shugabanninmu da manyanmu sai suka vatar da mu hanya



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 68

رَبَّنَآ ءَاتِهِمۡ ضِعۡفَيۡنِ مِنَ ٱلۡعَذَابِ وَٱلۡعَنۡهُمۡ لَعۡنٗا كَبِيرٗا

“Ya Ubangijinmu, Ka ba su azaba rivi biyu, Ka kuma la’ance su babbar la’ana.”



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 69

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَكُونُواْ كَٱلَّذِينَ ءَاذَوۡاْ مُوسَىٰ فَبَرَّأَهُ ٱللَّهُ مِمَّا قَالُواْۚ وَكَانَ عِندَ ٱللَّهِ وَجِيهٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku zamanto kamar waxanda suka cuci Musa sai Allah Ya wanke shi daga abin da suka faxa (a kansa). Ya kuma kasance mai alfarma ne a wurin Allah



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 70

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَقُولُواْ قَوۡلٗا سَدِيدٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku faxi Magana wadda take daidai ce



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 71

يُصۡلِحۡ لَكُمۡ أَعۡمَٰلَكُمۡ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡ ذُنُوبَكُمۡۗ وَمَن يُطِعِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَقَدۡ فَازَ فَوۡزًا عَظِيمًا

Zai kyautata muku ayyukanku, Ya kuma gafarta muku zunubanku. Duk kuwa wanda ya bi Allah da Manzonsa, to haqiqa ya rabauta rabauta mai girma



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 72

إِنَّا عَرَضۡنَا ٱلۡأَمَانَةَ عَلَى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَٱلۡجِبَالِ فَأَبَيۡنَ أَن يَحۡمِلۡنَهَا وَأَشۡفَقۡنَ مِنۡهَا وَحَمَلَهَا ٱلۡإِنسَٰنُۖ إِنَّهُۥ كَانَ ظَلُومٗا جَهُولٗا

Lalle Mun bijiro da amana[1] ga sammai da qasa da duwatsu sai suka qi xaukar ta suka ji tsoron ta, sai kuwa mutum ya xauke ta; lalle shi (mutum) ya kasance mai zaluntar kansa ne, mai jahilci


1- Amana a nan, su ne dokokin shari’a na umarni da hani.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 73

لِّيُعَذِّبَ ٱللَّهُ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱلۡمُنَٰفِقَٰتِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ وَٱلۡمُشۡرِكَٰتِ وَيَتُوبَ ٱللَّهُ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِۗ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمَۢا

Don Allah Ya azabtar da munafukai maza da munafukai mata, da mushirikai maza da mushirikai mata, Ya kuma karvi tubar muminai maza da muminai mata. Allah kuwa Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 1

ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَهُ ٱلۡحَمۡدُ فِي ٱلۡأٓخِرَةِۚ وَهُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡخَبِيرُ

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah Wanda duk abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa nasa ne, kuma godiya ta tabbata a gare Shi a lahira. Shi kuwa Mai hikima ne, Masani



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 2

يَعۡلَمُ مَا يَلِجُ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا يَخۡرُجُ مِنۡهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ وَمَا يَعۡرُجُ فِيهَاۚ وَهُوَ ٱلرَّحِيمُ ٱلۡغَفُورُ

Yana sane da abin da yake shiga cikin qasa da abin da yake fitowa daga cikinta, da kuma abin da yake sauka daga sama da abin da yake hawa cikinta. Kuma Shi Mai rahama ne, Mai gafara



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 3

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَا تَأۡتِينَا ٱلسَّاعَةُۖ قُلۡ بَلَىٰ وَرَبِّي لَتَأۡتِيَنَّكُمۡ عَٰلِمِ ٱلۡغَيۡبِۖ لَا يَعۡزُبُ عَنۡهُ مِثۡقَالُ ذَرَّةٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَآ أَصۡغَرُ مِن ذَٰلِكَ وَلَآ أَكۡبَرُ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٖ

Kuma waxanda suka kafirta suka ce: “Ranar alqiyama ba za ta zo mana ba.” Ka ce: “A’a, na rantse da Ubangijina, tabbas za ta zo muku, (Allah) Shi ne Masanin gaibu; ba abin da yake voye a gare Shi; daidai da qwayar zarra a cikin sammai ko a qasa, ko wanda ya fi wannan qanqanta ko ya fi girma, face yana nan (a rubuce) a cikin Lauhul-Mahafuzu



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 4

لِّيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُم مَّغۡفِرَةٞ وَرِزۡقٞ كَرِيمٞ

“Don Ya saka wa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka kyawawa. Waxannan suna da gafara da arziki na karamci.”



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 5

وَٱلَّذِينَ سَعَوۡ فِيٓ ءَايَٰتِنَا مُعَٰجِزِينَ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٞ مِّن رِّجۡزٍ أَلِيمٞ

Waxanda kuwa suka yi varna a cikin ayoyinmu don su nuna gazawarmu[1], waxannan suna da mummunar azaba mai raxaxi


1- Watau suna sukar ayoyin Allah da cewa sihiri ne ko bokanci ko waqa.


Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 6

وَيَرَى ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَ ٱلَّذِيٓ أُنزِلَ إِلَيۡكَ مِن رَّبِّكَ هُوَ ٱلۡحَقَّ وَيَهۡدِيٓ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Waxanda aka bai wa ilimi kuma suna ganin abin da aka saukar maka daga Ubangijinka shi ne gaskiya, kuma yana shiryarwa ne zuwa hanyar (Allah) Mabuwayi, Sha-yabo



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 7

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ هَلۡ نَدُلُّكُمۡ عَلَىٰ رَجُلٖ يُنَبِّئُكُمۡ إِذَا مُزِّقۡتُمۡ كُلَّ مُمَزَّقٍ إِنَّكُمۡ لَفِي خَلۡقٖ جَدِيدٍ

Waxanda suka kafirta suka ce: “Shin ma nuna muku wani mutum da zai ba ku labarin cewa, idan an yayyaga ku yugu-yugu lallai za ku dawo cikin wata halitta sabuwa?



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 8

أَفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبًا أَم بِهِۦ جِنَّةُۢۗ بَلِ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ فِي ٱلۡعَذَابِ وَٱلضَّلَٰلِ ٱلۡبَعِيدِ

“Shin ya yi wa Allah qarya ne, ko kuma yana da wani tavin hankali ne?” Ba haka ba ne, waxanda ba sa yin imani da lahira suna cikin azaba da vata mai nisa



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 9

أَفَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَىٰ مَا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِۚ إِن نَّشَأۡ نَخۡسِفۡ بِهِمُ ٱلۡأَرۡضَ أَوۡ نُسۡقِطۡ عَلَيۡهِمۡ كِسَفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّكُلِّ عَبۡدٖ مُّنِيبٖ

Ba sa dubawa su ga abin da yake gabansu da abin da yake bayansu na sama da qasa? In da Mun ga dama sai Mu nutsar da su cikin qasa ko kuma Mu rufto musu da wani yanki daga sama. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga duk wani bawa mai komawa ga Allah



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 10

۞وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا دَاوُۥدَ مِنَّا فَضۡلٗاۖ يَٰجِبَالُ أَوِّبِي مَعَهُۥ وَٱلطَّيۡرَۖ وَأَلَنَّا لَهُ ٱلۡحَدِيدَ

Kuma haqiqa Mun bai wa Dawuda falala daga gare Mu; cewa: “Ya ku duwatsu ku riqa amsa tasbihi tare da shi,” da kuma tsuntsaye; Muka kuma tausasa masa qarfe



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 11

أَنِ ٱعۡمَلۡ سَٰبِغَٰتٖ وَقَدِّرۡ فِي ٱلسَّرۡدِۖ وَٱعۡمَلُواْ صَٰلِحًاۖ إِنِّي بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

(Muka ce da shi): “Ka riqa yin cikakken silke, kuma ka kintata wajen yin saqar; kuma (kai Dawuda da iyalinka) ku yi ayyuka nagari; lalle Ni Mai ganin abin da kuke aikatawa ne.”



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 12

وَلِسُلَيۡمَٰنَ ٱلرِّيحَ غُدُوُّهَا شَهۡرٞ وَرَوَاحُهَا شَهۡرٞۖ وَأَسَلۡنَا لَهُۥ عَيۡنَ ٱلۡقِطۡرِۖ وَمِنَ ٱلۡجِنِّ مَن يَعۡمَلُ بَيۡنَ يَدَيۡهِ بِإِذۡنِ رَبِّهِۦۖ وَمَن يَزِغۡ مِنۡهُمۡ عَنۡ أَمۡرِنَا نُذِقۡهُ مِنۡ عَذَابِ ٱلسَّعِيرِ

Kuma (Muka hore wa) Sulaimanu iska, tafiyarta ta safe wata guda ce, ta yamma ma kuma wata guda ce; Muka kuma vuvvugo masa da narkakkiyar tagulla tana gudana. Daga aljannu kuma akwai masu aiki a wajensa da umarnin Ubangijinsa; wanda kuwa ya kauce wa umarninmu daga cikinsu, to za Mu xanxana masa azabar wutar Sa’ira



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 13

يَعۡمَلُونَ لَهُۥ مَا يَشَآءُ مِن مَّحَٰرِيبَ وَتَمَٰثِيلَ وَجِفَانٖ كَٱلۡجَوَابِ وَقُدُورٖ رَّاسِيَٰتٍۚ ٱعۡمَلُوٓاْ ءَالَ دَاوُۥدَ شُكۡرٗاۚ وَقَلِيلٞ مِّنۡ عِبَادِيَ ٱلشَّكُورُ

Suna aikata masa abubuwan da yake bukata na manya-manyan gine-gine[1] da mutum-mutumi[2] da akusa manya-manya kamar tafkuna da kafaffun tukwane. Ya ku iyalin Dawuda, ku yi aikin (xa’a) domin godiya. Masu godiya daga bayina kuwa kaxan ne


1- Watau wuraren ibada.


2- A wancan lokacin ba a haramta yin su ba. Sai bayan zuwan Annabi () ne ya haramta suranta su ko gina su.


Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 14

فَلَمَّا قَضَيۡنَا عَلَيۡهِ ٱلۡمَوۡتَ مَا دَلَّهُمۡ عَلَىٰ مَوۡتِهِۦٓ إِلَّا دَآبَّةُ ٱلۡأَرۡضِ تَأۡكُلُ مِنسَأَتَهُۥۖ فَلَمَّا خَرَّ تَبَيَّنَتِ ٱلۡجِنُّ أَن لَّوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ ٱلۡغَيۡبَ مَا لَبِثُواْ فِي ٱلۡعَذَابِ ٱلۡمُهِينِ

Sannan lokacin da Muka qaddara masa mutuwa ba abin da ya nuna musu mutuwarsa sai gara da ta riqa cin sandarsa[1]; to lokacin da ya faxi sai aljannu suka gane cewa da sun san gaibu da ba su zauna cikin azabar wulaqanci ba


1- Sandarsa da yake tsaye a kanta.


Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 15

لَقَدۡ كَانَ لِسَبَإٖ فِي مَسۡكَنِهِمۡ ءَايَةٞۖ جَنَّتَانِ عَن يَمِينٖ وَشِمَالٖۖ كُلُواْ مِن رِّزۡقِ رَبِّكُمۡ وَٱشۡكُرُواْ لَهُۥۚ بَلۡدَةٞ طَيِّبَةٞ وَرَبٌّ غَفُورٞ

Haqiqa akwai aya game da gidajen qabilar Saba’u (ta qasar Yaman); ita ce gonakai guda biyu na lambu a hagu da dama; (aka ce da su): “Ku ci daga arzikin Ubangijinku, kuma ku gode masa. Qasa ce mai daxin zama da kuma Ubangiji mai gafara



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 16

فَأَعۡرَضُواْ فَأَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ سَيۡلَ ٱلۡعَرِمِ وَبَدَّلۡنَٰهُم بِجَنَّتَيۡهِمۡ جَنَّتَيۡنِ ذَوَاتَيۡ أُكُلٍ خَمۡطٖ وَأَثۡلٖ وَشَيۡءٖ مِّن سِدۡرٖ قَلِيلٖ

Sai suka bijire, sai Muka aiko musu da ambaliyar madatsar ruwan Arimu, Muka kuma musanya musu gonakin nan nasu biyu da wasu gonakin biyu ma’abota ‘ya’ya masu xaci da kuma itacen tsamiya, da wani abu kaxan na ‘ya’yan magarya



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 17

ذَٰلِكَ جَزَيۡنَٰهُم بِمَا كَفَرُواْۖ وَهَلۡ نُجَٰزِيٓ إِلَّا ٱلۡكَفُورَ

Wannan shi ne Muka saka musu (da shi) saboda kafircinsu; ba kuwa Ma yin sakamako (irin wannan) sai ga mai butulci