Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 32

وَإِذۡ قَالُواْ ٱللَّهُمَّ إِن كَانَ هَٰذَا هُوَ ٱلۡحَقَّ مِنۡ عِندِكَ فَأَمۡطِرۡ عَلَيۡنَا حِجَارَةٗ مِّنَ ٱلسَّمَآءِ أَوِ ٱئۡتِنَا بِعَذَابٍ أَلِيمٖ

Ka tuna kuma lokacin da suka ce: “Ya Allah, idan wannan (Alqur’ani) ya zamanto gaskiya ne daga wurinka yake, to sai Ka yi mana ruwan duwatsu daga sama ko kuma Ka kawo mana da wata azaba mai raxaxi.”



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 33

وَمَا كَانَ ٱللَّهُ لِيُعَذِّبَهُمۡ وَأَنتَ فِيهِمۡۚ وَمَا كَانَ ٱللَّهُ مُعَذِّبَهُمۡ وَهُمۡ يَسۡتَغۡفِرُونَ

Allah kuwa bai zamanto Mai yi musu azaba ba alhali kai kana cikinsu, kuma Allah ba zai yi musu azaba ba alhali suna neman gafara



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 34

وَمَا لَهُمۡ أَلَّا يُعَذِّبَهُمُ ٱللَّهُ وَهُمۡ يَصُدُّونَ عَنِ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ وَمَا كَانُوٓاْ أَوۡلِيَآءَهُۥٓۚ إِنۡ أَوۡلِيَآؤُهُۥٓ إِلَّا ٱلۡمُتَّقُونَ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Me zai hana Allah Ya yi musu azaba alhali su suna hana mutane zuwa Masallaci mai alfarma, alhali kuwa ba su zamanto masu qaunar Sa na haqiqa ba. Masu qaunar Sa na haqiqa su ne masu taqawa, sai dai yawancinsu ba sa sanin (haka)



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 35

وَمَا كَانَ صَلَاتُهُمۡ عِندَ ٱلۡبَيۡتِ إِلَّا مُكَآءٗ وَتَصۡدِيَةٗۚ فَذُوقُواْ ٱلۡعَذَابَ بِمَا كُنتُمۡ تَكۡفُرُونَ

Kuma sallarsu a Xakin (Ka’aba) ba ta zamanto ba sai fito da tafi. Sai ku xanxani azaba saboda abin da kuka zamanto kuna yi na kafirci



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 36

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمۡ لِيَصُدُّواْ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِۚ فَسَيُنفِقُونَهَا ثُمَّ تَكُونُ عَلَيۡهِمۡ حَسۡرَةٗ ثُمَّ يُغۡلَبُونَۗ وَٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِلَىٰ جَهَنَّمَ يُحۡشَرُونَ

Lalle waxanda suka kafirta suna kashe dukiyoyinsu don su toshe hanyar Allah. To da sannu za su kashe ta (dukiyar) sannan ta zama nadama a gare su, sannan kuma a rinjaye su. Waxanda kuwa suka kafirta a Jahannama za a tattara su



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 37

لِيَمِيزَ ٱللَّهُ ٱلۡخَبِيثَ مِنَ ٱلطَّيِّبِ وَيَجۡعَلَ ٱلۡخَبِيثَ بَعۡضَهُۥ عَلَىٰ بَعۡضٖ فَيَرۡكُمَهُۥ جَمِيعٗا فَيَجۡعَلَهُۥ فِي جَهَنَّمَۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Don Allah Ya ware mummuna daga kyakkyawa, Ya kuma haxa mummuna wani a kan wani, sannan Ya tattara shi gaba xaya cikin Jahannama. Waxannan su ne asararru



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 38

قُل لِّلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِن يَنتَهُواْ يُغۡفَرۡ لَهُم مَّا قَدۡ سَلَفَ وَإِن يَعُودُواْ فَقَدۡ مَضَتۡ سُنَّتُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Ka ce da waxanda suka kafirta idan suka daina, to za a gafarta musu abin da ya riga ya wuce, idan kuma suka koma to fa ba shakka al’adar mutanen farko ta gabata[1]


1- Watau yadda Allah () ya hallaka al’ummun da suka gabata waxanda suka qaryata annabawansu.


Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 39

وَقَٰتِلُوهُمۡ حَتَّىٰ لَا تَكُونَ فِتۡنَةٞ وَيَكُونَ ٱلدِّينُ كُلُّهُۥ لِلَّهِۚ فَإِنِ ٱنتَهَوۡاْ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِمَا يَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

Kuma ku yaqe su har sai ya zamanto ba wata fitina[1], addini kuma ya zamanto dukkaninsa na Allah. Sannan idan suka daina, to lalle Allah Mai ganin abin da suke aikatawa ne


1- Watau watsuwar shirka a cikin al’umma da yunqurin hana mutane karvar gaskiya.


Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 40

وَإِن تَوَلَّوۡاْ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ مَوۡلَىٰكُمۡۚ نِعۡمَ ٱلۡمَوۡلَىٰ وَنِعۡمَ ٱلنَّصِيرُ

Idan kuma suka ba da baya, to ku sani cewa, Allah (Shi ne) Majivincin al’amarinku. Madalla da wannan Majivinci, kuma madalla da wannan Mai taimako