Sura: Suratus Saffat

Aya : 145

۞فَنَبَذۡنَٰهُ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٞ

Sai Muka jefa shi a tudu, a halin yana cikin rashin lafiya



Sura: Suratus Saffat

Aya : 146

وَأَنۢبَتۡنَا عَلَيۡهِ شَجَرَةٗ مِّن يَقۡطِينٖ

Muka kuma tsirar masa wata bishiya ta kabewa[1]


1- Domin ya rufe tsiraicinsa da ganyenta, ya kuma ci ‘ya’yanta, ya kuma sha inuwarta.


Sura: Suratus Saffat

Aya : 147

وَأَرۡسَلۡنَٰهُ إِلَىٰ مِاْئَةِ أَلۡفٍ أَوۡ يَزِيدُونَ

Muka kuma aika shi zuwa ga mutum dubu xari, ko kuma sama da haka



Sura: Suratus Saffat

Aya : 148

فَـَٔامَنُواْ فَمَتَّعۡنَٰهُمۡ إِلَىٰ حِينٖ

Sai suka yi imani, sai Muka jiyar da su daxi har zuwa wani lokaci



Sura: Suratus Saffat

Aya : 149

فَٱسۡتَفۡتِهِمۡ أَلِرَبِّكَ ٱلۡبَنَاتُ وَلَهُمُ ٱلۡبَنُونَ

Ka tambaye su: Yanzu Ubangijinka ne Yake da ‘ya’ya mata, su kuma suna da ‘ya’ya maza[1]?


1- Mushirikan Larabawa suna cewa mala’iku mata ne kuma ‘ya’yan Allah ne, yayin da sus uke fifita ‘ya’ya maza ga kawunansu.


Sura: Suratus Saffat

Aya : 150

أَمۡ خَلَقۡنَا ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ إِنَٰثٗا وَهُمۡ شَٰهِدُونَ

Ko kuma Mun halicci mala’iku ne ‘ya’ya mata a gaban idonsu suna gani?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 151

أَلَآ إِنَّهُم مِّنۡ إِفۡكِهِمۡ لَيَقُولُونَ

Ku saurara! Lalle su saboda qaryarsu har suna cewa:



Sura: Suratus Saffat

Aya : 152

وَلَدَ ٱللَّهُ وَإِنَّهُمۡ لَكَٰذِبُونَ

“Allah Ya haihu!” Lalle kuwa su tabbas maqaryata ne



Sura: Suratus Saffat

Aya : 153

أَصۡطَفَى ٱلۡبَنَاتِ عَلَى ٱلۡبَنِينَ

Yanzu Ya zavi ‘ya’ya mata a kan ‘ya’ya maza?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 154

مَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ

Me ya same ku, qaqa kuke yin irin wannan hukunci?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 155

أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

Me ya sa ne ba kwa wa’azantuwa?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 156

أَمۡ لَكُمۡ سُلۡطَٰنٞ مُّبِينٞ

Ko kuwa kuna da wata hujja ne bayyananniya?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 157

فَأۡتُواْ بِكِتَٰبِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

To ku kawo rubutaccen littafinku idan kun kasance masu gaskiya



Sura: Suratus Saffat

Aya : 158

وَجَعَلُواْ بَيۡنَهُۥ وَبَيۡنَ ٱلۡجِنَّةِ نَسَبٗاۚ وَلَقَدۡ عَلِمَتِ ٱلۡجِنَّةُ إِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ

Suka kuma sanya dangantakar nasaba tsakaninsa da mala’iku. Lalle kuwa su mala’iku sun san cewa tabbas su (masu wannan da’awar) za a kawo su (cikin wuta)



Sura: Suratus Saffat

Aya : 159

سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ

Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffanta (Shi da shi)



Sura: Suratus Saffat

Aya : 160

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Sai dai bayin Allah waxanda aka tsarkake



Sura: Suratus Saffat

Aya : 161

فَإِنَّكُمۡ وَمَا تَعۡبُدُونَ

Lalle ku da abin da kuke bauta wa



Sura: Suratus Saffat

Aya : 162

مَآ أَنتُمۡ عَلَيۡهِ بِفَٰتِنِينَ

Ba za ku iya vatar da kowa da shi ba



Sura: Suratus Saffat

Aya : 163

إِلَّا مَنۡ هُوَ صَالِ ٱلۡجَحِيمِ

Sai dai wanda zai shiga wutar Jahima



Sura: Suratus Saffat

Aya : 164

وَمَامِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٞ مَّعۡلُومٞ

(Jibrilu ya ce da Mala’iku): “Ba xai daga cikinmu face yana da wani matsayi sananne[1]


1- Watau na bautar Allah da yi masa xa’a.


Sura: Suratus Saffat

Aya : 165

وَإِنَّا لَنَحۡنُ ٱلصَّآفُّونَ

“Lalle kuma mu masu yin sahu ne



Sura: Suratus Saffat

Aya : 166

وَإِنَّا لَنَحۡنُ ٱلۡمُسَبِّحُونَ

“Kuma lalle mu masu yin tasbihi ne.”



Sura: Suratus Saffat

Aya : 167

وَإِن كَانُواْ لَيَقُولُونَ

Kuma lalle su (kafirai) sun kasance suna cewa[1]:


1- Watau suna cika baki kafin a aiko musu da Manzon Allah ().


Sura: Suratus Saffat

Aya : 168

لَوۡ أَنَّ عِندَنَا ذِكۡرٗا مِّنَ ٱلۡأَوَّلِينَ

“Da muna da wani littafi irin na mutanen farko



Sura: Suratus Saffat

Aya : 169

لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

“Tabbas da mun kasance bayin Allah waxanda aka tsarkake.”



Sura: Suratus Saffat

Aya : 170

فَكَفَرُواْ بِهِۦۖ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ

(Yayin da Alqur’ani ya zo musu) sai suka kafirce da shi; to ba da daxewa ba za su sani



Sura: Suratus Saffat

Aya : 171

وَلَقَدۡ سَبَقَتۡ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Haqiqa kuma kalmarmu (ta ba da nasara) ta rigaya ga bayinmu manzanni



Sura: Suratus Saffat

Aya : 172

إِنَّهُمۡ لَهُمُ ٱلۡمَنصُورُونَ

Lalle su tabbas su ne ababen taimako



Sura: Suratus Saffat

Aya : 173

وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلۡغَٰلِبُونَ

Kuma lalle rudunarmu tabbas su ne masu yin galaba



Sura: Suratus Saffat

Aya : 174

فَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ حِينٖ

Sai ka rabu da su har zuwa wani lokaci