سَيَصۡلَىٰ نَارٗا ذَاتَ لَهَبٖ
Ba da daxewa ba zai shiga wuta mai balbali
Tarayya :
وَٱمۡرَأَتُهُۥ حَمَّالَةَ ٱلۡحَطَبِ
Da kuma matarsa mai yawan xaukar kayan qaya[1]
1- Watau Ummu Jamil, ta kasance tana zuba wa Annabi () qaya a kan hanyarsa domin ya taka.
فِي جِيدِهَا حَبۡلٞ مِّن مَّسَدِۭ
A wuyanta akwai igiyar kaba mai ingantacciyar tukka. (a ranar alqiyama)
قُلۡ هُوَ ٱللَّهُ أَحَدٌ
Ka ce: “Shi Allah Xaya ne[1]
1- Watau a Zatinsa da siffofinsa da ayyukansa, kuma shi kaxai ya cancanci a bauta masa.
ٱللَّهُ ٱلصَّمَدُ
“Allah Abin nufa da buqatu[1]
1- Watau wanda shugabanci ya tuqe zuwa gare shi, domin ya tattara dukkan siffofin kamala da xaukaka.
لَمۡ يَلِدۡ وَلَمۡ يُولَدۡ
“Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba
وَلَمۡ يَكُن لَّهُۥ كُفُوًا أَحَدُۢ
“Kuma babu wani da ya kasance kini a gare Shi[1].”
1- Domin babu mai kama da shi a sunayensa da siffofinsa da ayyukansa.
قُلۡ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلۡفَلَقِ
Ka ce: “Ina neman tsari da Ubangijin asuba
مِن شَرِّ مَا خَلَقَ
“Daga sharrin abin da Ya halitta[1]
1- Watau duk wani mahluqi mai cutarwa, mutum ne ko aljani ko dabba.
وَمِن شَرِّ غَاسِقٍ إِذَا وَقَبَ
“Da kuma sharrin dare idan ya lulluve da duhu
وَمِن شَرِّ ٱلنَّفَّـٰثَٰتِ فِي ٱلۡعُقَدِ
“Da kuma sharrin mata masu tofi a cikin qulle-qulle
وَمِن شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ
“Da kuma sharrin mai hassada yayin da ya yi hassadar.”
قُلۡ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلنَّاسِ
Ka ce: “Ina neman tsari da Ubangijin mutane
مَلِكِ ٱلنَّاسِ
“Sarkin mutane
إِلَٰهِ ٱلنَّاسِ
“Abin bautar mutane
مِن شَرِّ ٱلۡوَسۡوَاسِ ٱلۡخَنَّاسِ
“Daga sharrin mai sa waswasi[1], mai noqewa[2]
1- Watau kowane shaixani.2- Watau duk sanda xan’adam ya ambaci Allah.
ٱلَّذِي يُوَسۡوِسُ فِي صُدُورِ ٱلنَّاسِ
“Wanda yake yin waswasi a cikin qirazan mutane
مِنَ ٱلۡجِنَّةِ وَٱلنَّاسِ
“Daga aljannu da na mutane[1].”
1- Watau shi wannan shaixani ana samun sa cikin mutane da aljanu.------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------