Sura: Suratul Baqara

Aya : 105

مَّا يَوَدُّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَلَا ٱلۡمُشۡرِكِينَ أَن يُنَزَّلَ عَلَيۡكُم مِّنۡ خَيۡرٖ مِّن رَّبِّكُمۡۚ وَٱللَّهُ يَخۡتَصُّ بِرَحۡمَتِهِۦ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ

Waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushrikai ba sa qaunar a saukar muku da wani alheri daga Ubangijinku, sai dai Allah kuwa Yana kevance wanda Ya ga dama da rahamarsa, Allah kuma Mai babbar falala ne



Sura: Suratul Baqara

Aya : 106

۞مَا نَنسَخۡ مِنۡ ءَايَةٍ أَوۡ نُنسِهَا نَأۡتِ بِخَيۡرٖ مِّنۡهَآ أَوۡ مِثۡلِهَآۗ أَلَمۡ تَعۡلَمۡ أَنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Babu wata aya da za Mu shafe ko Mu mantar da kai ita, sai Mun kawo wadda ta fi ta alheri ko kwatankwacinta. Ashe ba ka san cewa, lalle Allah Mai iko ne a kan komai ba?



Sura: Suratul Baqara

Aya : 107

أَلَمۡ تَعۡلَمۡ أَنَّ ٱللَّهَ لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۗ وَمَا لَكُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ مِن وَلِيّٖ وَلَا نَصِيرٍ

Kuma ba ka sani ba cewa, lalle mulkin sammai da qasa na Allah ne, kuma ba ku da wani majivinci ko wani mai taimako ba Allah ba?



Sura: Suratul Baqara

Aya : 108

أَمۡ تُرِيدُونَ أَن تَسۡـَٔلُواْ رَسُولَكُمۡ كَمَا سُئِلَ مُوسَىٰ مِن قَبۡلُۗ وَمَن يَتَبَدَّلِ ٱلۡكُفۡرَ بِٱلۡإِيمَٰنِ فَقَدۡ ضَلَّ سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ

Ko kuma kuna nufin za ku tambayi Manzonku kamar yadda aka yi wa Musa tambaya a da? Kuma duk wanda ya canza imani da kafirci to haqiqa ya vace wa hanya tsakatsakiya



Sura: Suratul Baqara

Aya : 109

وَدَّ كَثِيرٞ مِّنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ لَوۡ يَرُدُّونَكُم مِّنۢ بَعۡدِ إِيمَٰنِكُمۡ كُفَّارًا حَسَدٗا مِّنۡ عِندِ أَنفُسِهِم مِّنۢ بَعۡدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمُ ٱلۡحَقُّۖ فَٱعۡفُواْ وَٱصۡفَحُواْ حَتَّىٰ يَأۡتِيَ ٱللَّهُ بِأَمۡرِهِۦٓۗ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Da yawa daga cikin ma’abota littafi sun yi burin ina ma a ce su mayar da ku kafirai bayan imaninku, saboda hassada daga zukatansu, bayan kuma gaskiya ta bayyana a gare su. Don haka ku yi afuwa ku kawar da kai har sai Allah Ya zo da al’amarinsa. Lalle Allah Mai iko ne a kan komai



Sura: Suratul Baqara

Aya : 110

وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَمَا تُقَدِّمُواْ لِأَنفُسِكُم مِّنۡ خَيۡرٖ تَجِدُوهُ عِندَ ٱللَّهِۗ إِنَّ ٱللَّهَ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

Kuma ku tsayar da salla ku kuma ba da zakka; kuma duk abin da kuka aikata na alheri domin kawunanku za ku same shi a wajen Allah. Lalle Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



Sura: Suratul Baqara

Aya : 111

وَقَالُواْ لَن يَدۡخُلَ ٱلۡجَنَّةَ إِلَّا مَن كَانَ هُودًا أَوۡ نَصَٰرَىٰۗ تِلۡكَ أَمَانِيُّهُمۡۗ قُلۡ هَاتُواْ بُرۡهَٰنَكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Kuma (Yahudawa da Nasara) suka ce: “Babu mai shiga Aljanna sai wanda ya kasance Bayahude ko Banasare”. Waxannan burace-buracensu ne. Ka ce: “Ku kawo hujjarku idan kun kasance masu gaskiya”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 112

بَلَىٰۚ مَنۡ أَسۡلَمَ وَجۡهَهُۥ لِلَّهِ وَهُوَ مُحۡسِنٞ فَلَهُۥٓ أَجۡرُهُۥ عِندَ رَبِّهِۦ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

E! Wanda ya miqa fuskarsa ga Allah alhali yana mai kyautata aikinsa, to yana da ladansa a wajen Ubangijinsa, kuma babu tsoro a tare da su kuma ba za su yi baqin ciki ba



Sura: Suratul Baqara

Aya : 113

وَقَالَتِ ٱلۡيَهُودُ لَيۡسَتِ ٱلنَّصَٰرَىٰ عَلَىٰ شَيۡءٖ وَقَالَتِ ٱلنَّصَٰرَىٰ لَيۡسَتِ ٱلۡيَهُودُ عَلَىٰ شَيۡءٖ وَهُمۡ يَتۡلُونَ ٱلۡكِتَٰبَۗ كَذَٰلِكَ قَالَ ٱلَّذِينَ لَا يَعۡلَمُونَ مِثۡلَ قَوۡلِهِمۡۚ فَٱللَّهُ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فِيمَا كَانُواْ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَ

Yahudawa suka ce: “Nasara ba a kan komai suke ba”, su ma Nasara suka ce: “Yahudawa ba a kan komai suke ba”, alhalin dukkansu suna karanta Littafi. Kamar haka ne waxanda ba su da ilimi suka yi irin maganarsu. Kuma Allah zai yi hukunci a tsakaninsu ranar Alqiyama a kan abin da suka kasance suna savani a cikinsa



Sura: Suratul Baqara

Aya : 114

وَمَنۡ أَظۡلَمُ مِمَّن مَّنَعَ مَسَٰجِدَ ٱللَّهِ أَن يُذۡكَرَ فِيهَا ٱسۡمُهُۥ وَسَعَىٰ فِي خَرَابِهَآۚ أُوْلَـٰٓئِكَ مَا كَانَ لَهُمۡ أَن يَدۡخُلُوهَآ إِلَّا خَآئِفِينَۚ لَهُمۡ فِي ٱلدُّنۡيَا خِزۡيٞ وَلَهُمۡ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ عَذَابٌ عَظِيمٞ

Wane ne mafi zalunci kamar wanda ya hana masallatan Allah a riqa ambaton sunansa a cikinsu, ya yi ta qoqari wajen rushe su? Waxannan bai kamata su shige su ba sai a cikin halin tsoro. Za su gamu da wulaqanci a duniya a lahira kuma suna da wata azaba mai girma



Sura: Suratul Baqara

Aya : 115

وَلِلَّهِ ٱلۡمَشۡرِقُ وَٱلۡمَغۡرِبُۚ فَأَيۡنَمَا تُوَلُّواْ فَثَمَّ وَجۡهُ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ وَٰسِعٌ عَلِيمٞ

Gabas da yamma kuma na Allah ne. Duk inda aka fuskantar da ku to can ma alqiblar Allah ce. Lalle Allah Mai yalwar falala ne, kuma Mai yawan sani



Sura: Suratul Baqara

Aya : 116

وَقَالُواْ ٱتَّخَذَ ٱللَّهُ وَلَدٗاۗ سُبۡحَٰنَهُۥۖ بَل لَّهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ كُلّٞ لَّهُۥ قَٰنِتُونَ

Kuma suka ce: “Allah Yana da xa”. Tsarki ya tabbata a gare Shi. Bari (wannan magana)! Duk abin da yake cikin sammai da qasa nasa ne, kuma dukkansu masu biyayya ne a gare Shi



Sura: Suratul Baqara

Aya : 117

بَدِيعُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ وَإِذَا قَضَىٰٓ أَمۡرٗا فَإِنَّمَا يَقُولُ لَهُۥ كُن فَيَكُونُ

Shi ne Maqirqirin halittar sammai da qasa; kuma idan zai zartar da wani al’amari sai kawai Ya ce da shi: “Kasance”, sai ya kasance



Sura: Suratul Baqara

Aya : 118

وَقَالَ ٱلَّذِينَ لَا يَعۡلَمُونَ لَوۡلَا يُكَلِّمُنَا ٱللَّهُ أَوۡ تَأۡتِينَآ ءَايَةٞۗ كَذَٰلِكَ قَالَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِم مِّثۡلَ قَوۡلِهِمۡۘ تَشَٰبَهَتۡ قُلُوبُهُمۡۗ قَدۡ بَيَّنَّا ٱلۡأٓيَٰتِ لِقَوۡمٖ يُوقِنُونَ

Waxanda ba su da ilimi kuma suka ce, “Me zai hana Allah Ya yi magana da mu ko kuma wata aya ta zo mana?” Kamar haka ne waxanda suka gabace su suka faxi irin wannan maganar tasu. Zukatansu sun yi kama da juna. Haqiqa mun yi bayanin ayoyi ga mutane masu sakankancewa



Sura: Suratul Baqara

Aya : 119

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَٰكَ بِٱلۡحَقِّ بَشِيرٗا وَنَذِيرٗاۖ وَلَا تُسۡـَٔلُ عَنۡ أَصۡحَٰبِ ٱلۡجَحِيمِ

Lalle Mu Mun aiko ka da gaskiya, kana mai albishir kuma kana mai gargaxi, ba kuma za a tambaye ka ba game da ‘yan wutar Jahima



Sura: Suratul Baqara

Aya : 120

وَلَن تَرۡضَىٰ عَنكَ ٱلۡيَهُودُ وَلَا ٱلنَّصَٰرَىٰ حَتَّىٰ تَتَّبِعَ مِلَّتَهُمۡۗ قُلۡ إِنَّ هُدَى ٱللَّهِ هُوَ ٱلۡهُدَىٰۗ وَلَئِنِ ٱتَّبَعۡتَ أَهۡوَآءَهُم بَعۡدَ ٱلَّذِي جَآءَكَ مِنَ ٱلۡعِلۡمِ مَا لَكَ مِنَ ٱللَّهِ مِن وَلِيّٖ وَلَا نَصِيرٍ

Yahudawa da Nasara ba za su tava yarda da kai ba har sai ka bi addininsu. Ka ce: “Shiriyar Allah lalle ita ce shiriya”. Idan har ka bi son zuciyarsu bayan abin da ya zo maka na gaskiya, to ba ka da wani majivinci ko mai taimakonka wajen Allah



Sura: Suratul Baqara

Aya : 121

ٱلَّذِينَ ءَاتَيۡنَٰهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ يَتۡلُونَهُۥ حَقَّ تِلَاوَتِهِۦٓ أُوْلَـٰٓئِكَ يُؤۡمِنُونَ بِهِۦۗ وَمَن يَكۡفُرۡ بِهِۦ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Waxanda Muka saukar musu da littafi suna karanta shi yadda ya cancanta a karanta shi, waxannan su ne suke yin imani da shi. Kuma waxanda suka kafirce masa to waxannan su ne hasararru



Sura: Suratul Baqara

Aya : 122

يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتِيَ ٱلَّتِيٓ أَنۡعَمۡتُ عَلَيۡكُمۡ وَأَنِّي فَضَّلۡتُكُمۡ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ya ku Banu Isra’ila, ku tuna ni’imar da Na yi muku, kuma lalle Ni Na fifita ku a kan sauran mutanen duniya (na zamaninku)



Sura: Suratul Baqara

Aya : 123

وَٱتَّقُواْ يَوۡمٗا لَّا تَجۡزِي نَفۡسٌ عَن نَّفۡسٖ شَيۡـٔٗا وَلَا يُقۡبَلُ مِنۡهَا عَدۡلٞ وَلَا تَنفَعُهَا شَفَٰعَةٞ وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ

Kuma ku kiyayi wani yini da wani rai ba zai isar wa da wani rai komai ba, kuma ba za a karvi wata fansa daga gare shi ba, kuma ceto ba zai amfane shi ba, kuma su ba za a taimaka musu ba



Sura: Suratul Baqara

Aya : 124

۞وَإِذِ ٱبۡتَلَىٰٓ إِبۡرَٰهِـۧمَ رَبُّهُۥ بِكَلِمَٰتٖ فَأَتَمَّهُنَّۖ قَالَ إِنِّي جَاعِلُكَ لِلنَّاسِ إِمَامٗاۖ قَالَ وَمِن ذُرِّيَّتِيۖ قَالَ لَا يَنَالُ عَهۡدِي ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Ubangijin Ibrahimu Ya jarrabe shi da wasu kalmomi, sai ya cika su, sai Ya ce: “Ni zan naxa ka shugaba ga mutane”. Sai (Ibrahimu) ya ce: “Har da kuma zurriyata”; Sai (Allah) Ya ce: “Alqawarina ba zai shafi azzalumai ba.”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 125

وَإِذۡ جَعَلۡنَا ٱلۡبَيۡتَ مَثَابَةٗ لِّلنَّاسِ وَأَمۡنٗا وَٱتَّخِذُواْ مِن مَّقَامِ إِبۡرَٰهِـۧمَ مُصَلّٗىۖ وَعَهِدۡنَآ إِلَىٰٓ إِبۡرَٰهِـۧمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ أَن طَهِّرَا بَيۡتِيَ لِلطَّآئِفِينَ وَٱلۡعَٰكِفِينَ وَٱلرُّكَّعِ ٱلسُّجُودِ

Kuma ka tuna lokacin da Muka sanya wannan Xaki ya zama matattara ga mutane da kuma aminci; kuma ku mayar da Maqamu Ibrahim wajen salla; kuma Muka yi umarni ga Ibrahim da Isma’ila da cewa: “Ku tsarkake Xakina don masu xawafi da masu i’itikafi da masu ruku’u da sujjada”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 126

وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ رَبِّ ٱجۡعَلۡ هَٰذَا بَلَدًا ءَامِنٗا وَٱرۡزُقۡ أَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلثَّمَرَٰتِ مَنۡ ءَامَنَ مِنۡهُم بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۚ قَالَ وَمَن كَفَرَ فَأُمَتِّعُهُۥ قَلِيلٗا ثُمَّ أَضۡطَرُّهُۥٓ إِلَىٰ عَذَابِ ٱلنَّارِۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu ya ce: “Ya Ubangijina, Ka sanya wannan (wuri) ya zama gari mai aminci, kuma Ka arzuta mutanensa da kayan marmari, (amma) wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira daga cikinsu”. Sai (Allah) Ya ce: “Har ma wanda ya kafirta, zan jiyar da shi daxi kaxan, sannan in tilasa masa shiga azabar wuta, tir da wannan makoma.”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 127

وَإِذۡ يَرۡفَعُ إِبۡرَٰهِـۧمُ ٱلۡقَوَاعِدَ مِنَ ٱلۡبَيۡتِ وَإِسۡمَٰعِيلُ رَبَّنَا تَقَبَّلۡ مِنَّآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu yake xaga harsashen ginin Xakin Ka’aba tare da Isma’ila, suna cewa: “Ya Ubangijinmu Ka karva mana; lalle Kai Mai ji ne Mai gani.”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 128

رَبَّنَا وَٱجۡعَلۡنَا مُسۡلِمَيۡنِ لَكَ وَمِن ذُرِّيَّتِنَآ أُمَّةٗ مُّسۡلِمَةٗ لَّكَ وَأَرِنَا مَنَاسِكَنَا وَتُبۡ عَلَيۡنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

“Ya Ubangijinmu, Ka sanya mu masu miqa wuya gare Ka, kuma a cikin zurriyarmu ma (Ka samar) da wata al’umma mai miqa wuya gare Ka, kuma Ka nuna mana ayyaukan ibadarmu, kuma Ka karvi tubanmu, lalle Kai Mai yawan karvar tuba ne Mai jin qai.”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 129

رَبَّنَا وَٱبۡعَثۡ فِيهِمۡ رَسُولٗا مِّنۡهُمۡ يَتۡلُواْ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتِكَ وَيُعَلِّمُهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَيُزَكِّيهِمۡۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

“Ya Ubangijinmu, Ka aiko da wani manzo daga cikinsu, da zai riqa karanta musu ayoyinka, kuma yana koyar da su Littafi da hikima, kuma ya riqa yi musu tarbiyya. Lalle kai Mabuwayi ne, Mai hikima.”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 130

وَمَن يَرۡغَبُ عَن مِّلَّةِ إِبۡرَٰهِـۧمَ إِلَّا مَن سَفِهَ نَفۡسَهُۥۚ وَلَقَدِ ٱصۡطَفَيۡنَٰهُ فِي ٱلدُّنۡيَاۖ وَإِنَّهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ لَمِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Babu kuma wanda zai qi addinin Ibrahimu sai wanda bai san ciwon kansa ba. Kuma haqiqa Mun zave shi a duniya, kuma shi a lahira yana cikin mutanen qwarai



Sura: Suratul Baqara

Aya : 131

إِذۡ قَالَ لَهُۥ رَبُّهُۥٓ أَسۡلِمۡۖ قَالَ أَسۡلَمۡتُ لِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ka tuna lokacin da Ubangijijinsa Ya ce masa: “Ka miqa wuya”, sai ya ce: “Na miqa wuya ga Ubangijin talikai.”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 132

وَوَصَّىٰ بِهَآ إِبۡرَٰهِـۧمُ بَنِيهِ وَيَعۡقُوبُ يَٰبَنِيَّ إِنَّ ٱللَّهَ ٱصۡطَفَىٰ لَكُمُ ٱلدِّينَ فَلَا تَمُوتُنَّ إِلَّا وَأَنتُم مُّسۡلِمُونَ

Kuma Ibrahimu da Ya’aqubu suka yi wasiyya da wannan ga ‘ya’yansu cewa: “Ya ‘ya’yana, lalle Allah Ya zava muku addini, don haka kada ku mutu face kuna Musulmi.”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 133

أَمۡ كُنتُمۡ شُهَدَآءَ إِذۡ حَضَرَ يَعۡقُوبَ ٱلۡمَوۡتُ إِذۡ قَالَ لِبَنِيهِ مَا تَعۡبُدُونَ مِنۢ بَعۡدِيۖ قَالُواْ نَعۡبُدُ إِلَٰهَكَ وَإِلَٰهَ ءَابَآئِكَ إِبۡرَٰهِـۧمَ وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِسۡحَٰقَ إِلَٰهٗا وَٰحِدٗا وَنَحۡنُ لَهُۥ مُسۡلِمُونَ

Ko kuna nan ne lokacin da mutuwa ta zo wa Ya’aqubu, lokacin da ya ce wa ‘ya’yansa: “Me za ku bauta wa a bayana?” Sai suka ce: “Za mu bauta wa abin bautarka kuma abin bautar iyayenka, Ibrahim da Isma’il da Ishaq, abin bauta guda xaya, kuma mu gare Shi muke miqa wuya.”



Sura: Suratul Baqara

Aya : 134

تِلۡكَ أُمَّةٞ قَدۡ خَلَتۡۖ لَهَا مَا كَسَبَتۡ وَلَكُم مَّا كَسَبۡتُمۡۖ وَلَا تُسۡـَٔلُونَ عَمَّا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Waccan al’umma ce da ta riga ta wuce; abin da ta aikata mallakarta ne, ku ma abin da kuka aikata naku ne, kuma ba za a tambaye ku ba game da abin da suka kasance suna aikatawa.”