Sura: Suratun Naba’i

Aya : 31

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ مَفَازًا

Lalle masu taqawa suna da babban rabo



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 32

حَدَآئِقَ وَأَعۡنَٰبٗا

(Su ne) gonaki da inabai



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 33

وَكَوَاعِبَ أَتۡرَابٗا

Da ‘yan mata tsaraiku



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 34

وَكَأۡسٗا دِهَاقٗا

Da kofin (giya) cikakke



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 35

لَّا يَسۡمَعُونَ فِيهَا لَغۡوٗا وَلَا كِذَّـٰبٗا

Ba sa jin maganar banza a cikinta ko kuma qarya



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 36

جَزَآءٗ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابٗا

Sakamako ne daga Ubangijinka, kyauta ce a lissafe (gwargwadon aikin kowa)



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 37

رَّبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا ٱلرَّحۡمَٰنِۖ لَا يَمۡلِكُونَ مِنۡهُ خِطَابٗا

Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu (watau Allah) Mai rahama; (halittu) ba sa samun ikon yi masa magana daga gare Shi



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 38

يَوۡمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ صَفّٗاۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنۡ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَقَالَ صَوَابٗا

Ranar da Jibrilu da mala’iku za su tsaya sahu-sahu; (halittu) ba sa iya magana sai fa wanda (Allah) Mai rahama Ya yi wa izini, ya kuma faxi abin da ya dace[1]


1- Watau kalmar tauhidi.


Sura: Suratun Naba’i

Aya : 39

ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمُ ٱلۡحَقُّۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا

Wannan rana ce tabbatacciya; saboda haka wanda ya ga dama sai ya riqi kyakkyawar makoma zuwa ga Ubangijinsa



Sura: Suratun Naba’i

Aya : 40

إِنَّآ أَنذَرۡنَٰكُمۡ عَذَابٗا قَرِيبٗا يَوۡمَ يَنظُرُ ٱلۡمَرۡءُ مَا قَدَّمَتۡ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلۡكَافِرُ يَٰلَيۡتَنِي كُنتُ تُرَٰبَۢا

Lalle Mun yi muku gargaxin azaba ta kurkusa, a ranar da mutum zai ga abin da hannayensa suka gabatar (na alheri ko na sharri), kafiri kuma ya riqa cewa: “Ina ma da na zama turvaya[1]!”


1- Watau kamar sauran dabbobi da za a ce musu su zama turvaya.


Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 1

وَٱلنَّـٰزِعَٰتِ غَرۡقٗا

Na rantse da (mala’iku) masu cizgar (ran kafiri) mummunar cizga



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 2

وَٱلنَّـٰشِطَٰتِ نَشۡطٗا

Da kuma (mala’iku) masu zare (ran mumini) sassauqar zarewa



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 3

وَٱلسَّـٰبِحَٰتِ سَبۡحٗا

Da kuma (mala’iku) masu ninqaya (a sama don sauko da umarni) ninqaya mai tsananin sauri



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 4

فَٱلسَّـٰبِقَٰتِ سَبۡقٗا

Sannan da (mala’iku) masu matuqar rigegeniya (don zartar da umarnin Allah)



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 5

فَٱلۡمُدَبِّرَٰتِ أَمۡرٗا

Sannan da (mala’iku) masu tsara al’amura



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 6

يَوۡمَ تَرۡجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ

Ranar da mai girgizawa za ta yi girgiza (watau busar qaho ta farko)



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 7

تَتۡبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ

Mai bin ta kuma za ta biyo ta (watau busa ta biyu)



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 8

قُلُوبٞ يَوۡمَئِذٖ وَاجِفَةٌ

Wasu zukata a wannan ranar a tsorace suke



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 9

أَبۡصَٰرُهَا خَٰشِعَةٞ

Idanuwansu kuma a qasqance suke



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 10

يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرۡدُودُونَ فِي ٱلۡحَافِرَةِ

(A duniya) suna cewa: “Yanzu zai yiwu a dawo da mu a raye (bayan mutuwa)?



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 11

أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمٗا نَّخِرَةٗ

“Yanzu ko bayan mun zama qasusuwa rududdugaggu?”



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 12

قَالُواْ تِلۡكَ إِذٗا كَرَّةٌ خَاسِرَةٞ

Suka ce: “Idan ko ya yiwu, to wannan komawa ce mai cike da asara.”



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 13

فَإِنَّمَا هِيَ زَجۡرَةٞ وَٰحِدَةٞ

To lalle ita kawai tsawa ce guda xaya tal!



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 14

فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ

Sai ga su a bayan qasa[1]


1- Watau kowa da kowa ya fito da rai.


Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 15

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ

Shin labarin Musa ya zo maka?



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 16

إِذۡ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوًى

Lokacin da Ubangijinsa Ya kirawo shi a kwari mai tsarki, (watau) Xuwa?



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 17

ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

(Aka ce da shi): Ka tafi zuwa ga Fir’auna, haqiqa shi ya yi xagawa



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 18

فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ

Sai ka ce: “Shin zai yiwu gare ka kuwa ka tsarkaka?



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 19

وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ

“In kuma shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka, sai ka ji tsoron Sa?



Sura: Suratun Nazi’at

Aya : 20

فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ

Sai ya nuna masa babbar aya[1]


1- Watau ya nuna masa hannun mai haske kamar fitila da kuma sandarsa mai rikixa ta zama macijiya.