Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 12

فِيهَا عَيۡنٞ جَارِيَةٞ

A cikinta akwai marmaro mai gudana



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 13

فِيهَا سُرُرٞ مَّرۡفُوعَةٞ

A cikinta akwai gadaje maxaukaka



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 14

وَأَكۡوَابٞ مَّوۡضُوعَةٞ

Da kofuna a ajijjiye



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 15

وَنَمَارِقُ مَصۡفُوفَةٞ

Da matasan kai a jejjere



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 16

وَزَرَابِيُّ مَبۡثُوثَةٌ

Da dardumai a shisshimfixe



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ

Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 18

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ

Da kuma sama yadda aka xaga ta?



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 19

وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ

Da kuma duwatsu yadda aka kakkafa su?



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 20

وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ

Da kuma qasa yadda aka shimfixa ta?



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 21

فَذَكِّرۡ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٞ

To ka yi wa’azi, lalle kai mai wa’azi ne kawai



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 22

لَّسۡتَ عَلَيۡهِم بِمُصَيۡطِرٍ

Kai ba mai tilasta su ba ne



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 23

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ

Sai dai wanda ya ba da baya ya kuma kafirce



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 24

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَكۡبَرَ

To Allah zai azabtar da shi azaba mafi girma[1]


1- Watau wutar Jahannama inda zai dawwama a cikinta har abada.


Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 25

إِنَّ إِلَيۡنَآ إِيَابَهُمۡ

Lalle zuwa gare Mu ne makomarsu take



Sura: Suratul Ghashiya

Aya : 26

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا حِسَابَهُم

Sannan kuma a kanmu ne hisabinsu yake



Sura: Suratul Fajr

Aya : 1

وَٱلۡفَجۡرِ

Na rantse da alfijir



Sura: Suratul Fajr

Aya : 2

وَلَيَالٍ عَشۡرٖ

Da kuma darare goma[1]


1- Watau kwanaki goma na farkon watan Zulhijja.


Sura: Suratul Fajr

Aya : 3

وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ

Da kuma abin da yake cika[1] da kuma mara[2]


1- Watau bibbiyu ko hurhuxu ko shida-shida da sauransu.


2- Watau xaya ko uku ko biyar da sauransu.


Sura: Suratul Fajr

Aya : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ

Da kuma dare lokacin da yake tafiya (cikin duhu)



Sura: Suratul Fajr

Aya : 5

هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ

Shin a game da waxannan akwai rantsuwa (mai gamsarwa) ga mai hankali[1]?


1- Watau duk mai hankali zai gamsu da waxannan rantse-rantse.


Sura: Suratul Fajr

Aya : 6

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ba ga Adawa?



Sura: Suratul Fajr

Aya : 7

إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ

(Watau qabilar) Iramu ma’abociyar tsawo



Sura: Suratul Fajr

Aya : 8

ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Wadda ba a halicci irinta ba a cikin garuruwa (a tsananin qarfi)



Sura: Suratul Fajr

Aya : 9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ

Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura



Sura: Suratul Fajr

Aya : 10

وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ

Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku



Sura: Suratul Fajr

Aya : 11

ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa



Sura: Suratul Fajr

Aya : 12

فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ

Suka kuma yawaita varna a cikinsu



Sura: Suratul Fajr

Aya : 13

فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ

Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani



Sura: Suratul Fajr

Aya : 14

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ

Lalle Ubangijinka tabbas Yana nan a madakata[1]


1- Watau yana wurin da yake hangen xaukacin ayyukan bayinsa.


Sura: Suratul Fajr

Aya : 15

فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ

Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”