Sura: Suratul Furqan

Aya : 17

وَيَوۡمَ يَحۡشُرُهُمۡ وَمَا يَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ فَيَقُولُ ءَأَنتُمۡ أَضۡلَلۡتُمۡ عِبَادِي هَـٰٓؤُلَآءِ أَمۡ هُمۡ ضَلُّواْ ٱلسَّبِيلَ

(Ka tuna) kuma ranar da zai tara su da abin da suke bauta wa ba Allah ba, sai Ya ce (da su): “Shin yanzu ku ne kuka vatar da bayina waxannan, ko kuwa su ne suka vace wa hanya don kansu?”



Sura: Suratul Furqan

Aya : 18

قَالُواْ سُبۡحَٰنَكَ مَا كَانَ يَنۢبَغِي لَنَآ أَن نَّتَّخِذَ مِن دُونِكَ مِنۡ أَوۡلِيَآءَ وَلَٰكِن مَّتَّعۡتَهُمۡ وَءَابَآءَهُمۡ حَتَّىٰ نَسُواْ ٱلذِّكۡرَ وَكَانُواْ قَوۡمَۢا بُورٗا

Suka ce: “Tsarki ya tabbata gare Ka, bai zamanto ya dace da mu ba mu riqi wasu majivinta ba Kai ba, sai dai kuma Ka jiyar da su daxi ne tare da iyayensu har suka manta tuna Ka, suka kuwa kasance mutane hallakakku.”



Sura: Suratul Furqan

Aya : 19

فَقَدۡ كَذَّبُوكُم بِمَا تَقُولُونَ فَمَا تَسۡتَطِيعُونَ صَرۡفٗا وَلَا نَصۡرٗاۚ وَمَن يَظۡلِم مِّنكُمۡ نُذِقۡهُ عَذَابٗا كَبِيرٗا

To haqiqa sun qaryata ku game da abin da kuke faxa, to ba za ku samu wata makauta ba, ko kuma wani taimako. Duk wanda kuma ya yi zalunci daga cikinku za Mu xanxana masa azaba mai girma



Sura: Suratul Furqan

Aya : 20

وَمَآ أَرۡسَلۡنَا قَبۡلَكَ مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ إِلَّآ إِنَّهُمۡ لَيَأۡكُلُونَ ٱلطَّعَامَ وَيَمۡشُونَ فِي ٱلۡأَسۡوَاقِۗ وَجَعَلۡنَا بَعۡضَكُمۡ لِبَعۡضٖ فِتۡنَةً أَتَصۡبِرُونَۗ وَكَانَ رَبُّكَ بَصِيرٗا

Kuma ba Mu aiko manzanni ba gabaninka sai cewa lalle suna cin abinci kuma suna tafiya cikin kasuwanni. Mun kuwa sanya wasunku su zama fitina ga wasu. Shin za ku yi haquri? Ubangijinka kuwa Ya kasance Mai gani ne