Sura: Suratu Ghafir

Aya : 17

ٱلۡيَوۡمَ تُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡۚ لَا ظُلۡمَ ٱلۡيَوۡمَۚ إِنَّ ٱللَّهَ سَرِيعُ ٱلۡحِسَابِ

A wannan ranar za a saka wa kowane rai da irin abin da ya aikata. Babu zalunci a wannan ranar. Lalle Allah Mai gaggawar yin hisabi ne



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 18

وَأَنذِرۡهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡأٓزِفَةِ إِذِ ٱلۡقُلُوبُ لَدَى ٱلۡحَنَاجِرِ كَٰظِمِينَۚ مَا لِلظَّـٰلِمِينَ مِنۡ حَمِيمٖ وَلَا شَفِيعٖ يُطَاعُ

Ka kuma tsoratar da su ranar (alqiyama) mai kusantowa, a yayin da zukata suke maqare a wuyoyinsu (saboda tsananin tsoro). Azzalumai ba su da wani masoyi ko kuma wani mai ceto da za a yi wa biyayya



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 19

يَعۡلَمُ خَآئِنَةَ ٱلۡأَعۡيُنِ وَمَا تُخۡفِي ٱلصُّدُورُ

(Allah) Yana sane da ha’incin idanuwa da kuma abin da zukata suke voyewa



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 20

وَٱللَّهُ يَقۡضِي بِٱلۡحَقِّۖ وَٱلَّذِينَ يَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ لَا يَقۡضُونَ بِشَيۡءٍۗ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡبَصِيرُ

Allah Yana hukunci da gaskiya; waxanda kuwa suke bauta wa wanda ba Shi ba, ba sa hukunta komai. Haqiqa Allah Shi ne Mai ji, Mai gani



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 21

۞أَوَلَمۡ يَسِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَيَنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلَّذِينَ كَانُواْ مِن قَبۡلِهِمۡۚ كَانُواْ هُمۡ أَشَدَّ مِنۡهُمۡ قُوَّةٗ وَءَاثَارٗا فِي ٱلۡأَرۡضِ فَأَخَذَهُمُ ٱللَّهُ بِذُنُوبِهِمۡ وَمَا كَانَ لَهُم مِّنَ ٱللَّهِ مِن وَاقٖ

Shin ba sa tafiya a bayan qasa sannan su ga yaya qarshen waxanda suka kasance gabaninsu ya zama? Su sun kasance sun fi su tsananin qarfi da barin gurabe na tarihi a bayan qasa, sai Allah Ya kama su da laifukansu, ba su kuma da wani mai kare su daga Allah



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 22

ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ كَانَت تَّأۡتِيهِمۡ رُسُلُهُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِ فَكَفَرُواْ فَأَخَذَهُمُ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ قَوِيّٞ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Wannan (ya same su ne) saboda manzanninsu sun kasance suna zuwa musu da hujjoji bayyanannu, sai suka kafirce, sai Allah Ya kama su. Lalle Shi Mai (tsananin) qarfi ne, Mai tsananin azaba



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 23

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا مُوسَىٰ بِـَٔايَٰتِنَا وَسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٍ

Haqiqa kuma Mun aiko Musa da ayoyinmu da kuma hujja mabayyaniya



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 24

إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ وَهَٰمَٰنَ وَقَٰرُونَ فَقَالُواْ سَٰحِرٞ كَذَّابٞ

Zuwa ga Fir’auna da Hamana da Qaruna, sai suka ce shi mai sihiri ne, babban maqaryaci



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 25

فَلَمَّا جَآءَهُم بِٱلۡحَقِّ مِنۡ عِندِنَا قَالُواْ ٱقۡتُلُوٓاْ أَبۡنَآءَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ وَٱسۡتَحۡيُواْ نِسَآءَهُمۡۚ وَمَا كَيۡدُ ٱلۡكَٰفِرِينَ إِلَّا فِي ضَلَٰلٖ

To lokacin da ya zo musu da gaskiya daga wajenmu sai suka ce: “Ku kashe `ya`yan waxanda suka yi imani tare da shi, ku kuma qyale matansu da rai.” Makircin kafirai bai zama ba sai a lalace



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 26

وَقَالَ فِرۡعَوۡنُ ذَرُونِيٓ أَقۡتُلۡ مُوسَىٰ وَلۡيَدۡعُ رَبَّهُۥٓۖ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يُبَدِّلَ دِينَكُمۡ أَوۡ أَن يُظۡهِرَ فِي ٱلۡأَرۡضِ ٱلۡفَسَادَ

Fir’auna kuma ya ce: “Ku bar ni in kashe Musa, kuma (ya je) ya kirawo Ubangijin nasa; lalle ni ina jin tsoron kada ya sauya addininku ko kuma ya bayyanar da varna a bayan qasa[1].”


1- Watau zai kawo rikici da savani tsakanin mutane wanda zai haifar musu da yamutsi da kashe-kashe.


Sura: Suratu Ghafir

Aya : 27

وَقَالَ مُوسَىٰٓ إِنِّي عُذۡتُ بِرَبِّي وَرَبِّكُم مِّن كُلِّ مُتَكَبِّرٖ لَّا يُؤۡمِنُ بِيَوۡمِ ٱلۡحِسَابِ

Musa ya ce: “Lalle ni ina neman tsari da Ubangijina, da kuma Ubangijinku daga duk wani mai girman kai da ba ya yin imani da ranar hisabi.”



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 28

وَقَالَ رَجُلٞ مُّؤۡمِنٞ مِّنۡ ءَالِ فِرۡعَوۡنَ يَكۡتُمُ إِيمَٰنَهُۥٓ أَتَقۡتُلُونَ رَجُلًا أَن يَقُولَ رَبِّيَ ٱللَّهُ وَقَدۡ جَآءَكُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِ مِن رَّبِّكُمۡۖ وَإِن يَكُ كَٰذِبٗا فَعَلَيۡهِ كَذِبُهُۥۖ وَإِن يَكُ صَادِقٗا يُصِبۡكُم بَعۡضُ ٱلَّذِي يَعِدُكُمۡۖ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَنۡ هُوَ مُسۡرِفٞ كَذَّابٞ

Kuma wani mutum mumini daga dangin Fir’auna wanda yake voye imaninsa ya ce: “Yanzu kwa kashe mutum don ya ce ‘Allah ne Ubangijina’, kuma alhalin ya zo muku da hujjoji bayyanannu daga Ubangijinku? Idan ya zama maqaryaci ne to laifin qaryarsa yana kansa; idan kuwa ya zama mai gaskiya, to wani abu daga abin da yake yi muku gargaxinsa zai same ku. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake shi mai yawan varna ne, maqaryaci



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 29

يَٰقَوۡمِ لَكُمُ ٱلۡمُلۡكُ ٱلۡيَوۡمَ ظَٰهِرِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَمَن يَنصُرُنَا مِنۢ بَأۡسِ ٱللَّهِ إِن جَآءَنَاۚ قَالَ فِرۡعَوۡنُ مَآ أُرِيكُمۡ إِلَّا مَآ أَرَىٰ وَمَآ أَهۡدِيكُمۡ إِلَّا سَبِيلَ ٱلرَّشَادِ

“Ya ku mutanena, a yau ku ne masu mulki masu qarfi a bayan qasa, to wane ne zai kare mu daga azabar Allah idan ta zo mana?” Fir’auna ya ce: “Ba abin da nake nuna muku sai abin da na gani (shi ne daidai), kuma hanyar shiriya kaxai nake nuna muku.”



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 30

وَقَالَ ٱلَّذِيٓ ءَامَنَ يَٰقَوۡمِ إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُم مِّثۡلَ يَوۡمِ ٱلۡأَحۡزَابِ

Sai kuma wannan da ya yi imani ya ce: “Ya ku mutanena, lalle ni ina jiye muku tsoron irin ranar gangamin qungiyoyin (kafirai)



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 31

مِثۡلَ دَأۡبِ قَوۡمِ نُوحٖ وَعَادٖ وَثَمُودَ وَٱلَّذِينَ مِنۢ بَعۡدِهِمۡۚ وَمَا ٱللَّهُ يُرِيدُ ظُلۡمٗا لِّلۡعِبَادِ

“Kamar misalin al’adar mutanen Nuhu da Adawa da Samudawa da kuma waxanda suka zo bayansu. Allah kuwa ba Ya nufin zalunci ga bayi



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 32

وَيَٰقَوۡمِ إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ يَوۡمَ ٱلتَّنَادِ

“Kuma ya ku mutanena, lalle ni ina jiye muku tsoron ranar kiraye-kirayen juna (ranar alqiyama)[1]


1- Watau mutane za su riqa kiran junansu saboda dangantaka ta jini suna neman alfarma.


Sura: Suratu Ghafir

Aya : 33

يَوۡمَ تُوَلُّونَ مُدۡبِرِينَ مَا لَكُم مِّنَ ٱللَّهِ مِنۡ عَاصِمٖۗ وَمَن يُضۡلِلِ ٱللَّهُ فَمَا لَهُۥ مِنۡ هَادٖ

“Ranar da za ku juya kuna masu ba da baya, ba ku da wani mai kare ku daga Allah. Duk kuma wanda Allah Ya vatar to ba shi da wani mai shiryarwa.”



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 34

وَلَقَدۡ جَآءَكُمۡ يُوسُفُ مِن قَبۡلُ بِٱلۡبَيِّنَٰتِ فَمَا زِلۡتُمۡ فِي شَكّٖ مِّمَّا جَآءَكُم بِهِۦۖ حَتَّىٰٓ إِذَا هَلَكَ قُلۡتُمۡ لَن يَبۡعَثَ ٱللَّهُ مِنۢ بَعۡدِهِۦ رَسُولٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَنۡ هُوَ مُسۡرِفٞ مُّرۡتَابٌ

Haqiqa kuma Yusufu ya zo muku da (hujjoji) bayyanannu tun kafin (zuwan Musa), to ba ku gushe kuna kokwanton abin da ya zo muku da shi ba, har yayin da ya mutu sai kuka ce: “Allah ba zai sake aiko da wani manzo bayansa ba.” Kamar haka ne Allah Yake vatar da duk wanda shi mai varna ne, mai shakka



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 35

ٱلَّذِينَ يُجَٰدِلُونَ فِيٓ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ بِغَيۡرِ سُلۡطَٰنٍ أَتَىٰهُمۡۖ كَبُرَ مَقۡتًا عِندَ ٱللَّهِ وَعِندَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْۚ كَذَٰلِكَ يَطۡبَعُ ٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ قَلۡبِ مُتَكَبِّرٖ جَبَّارٖ

Waxanda suke yin jayayya game da ayoyin Allah ba tare da wata hujja da ta zo musu ba; qyamar (wannan) a wurin Allah da wurin waxanda suka yi imani ta girmama. Kamar haka ne Allah Yake toshe zuciyar duk wani mai girman kai, mai tsaurin rai



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 36

وَقَالَ فِرۡعَوۡنُ يَٰهَٰمَٰنُ ٱبۡنِ لِي صَرۡحٗا لَّعَلِّيٓ أَبۡلُغُ ٱلۡأَسۡبَٰبَ

Fir’auna kuma ya ce: “Ya Hamana, ka gina min dogon gini ko na kai ga hanyoyi



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 37

أَسۡبَٰبَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ فَأَطَّلِعَ إِلَىٰٓ إِلَٰهِ مُوسَىٰ وَإِنِّي لَأَظُنُّهُۥ كَٰذِبٗاۚ وَكَذَٰلِكَ زُيِّنَ لِفِرۡعَوۡنَ سُوٓءُ عَمَلِهِۦ وَصُدَّ عَنِ ٱلسَّبِيلِۚ وَمَا كَيۡدُ فِرۡعَوۡنَ إِلَّا فِي تَبَابٖ

“(Watau) hanyoyin (da ke kaiwa zuwa) sammai sai in gano Ubangijin Musa, lalle kuma ni ina tsammaninsa maqaryaci ne.” Kamar haka kuma aka qawata wa Fir’auna mummunan aikinsa aka kuma kange shi daga hanyar (gaskiya). Makircin Fir’auna kuwa ba a komai yake ba sai cikin halaka



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 38

وَقَالَ ٱلَّذِيٓ ءَامَنَ يَٰقَوۡمِ ٱتَّبِعُونِ أَهۡدِكُمۡ سَبِيلَ ٱلرَّشَادِ

Sai (mutumin nan) wanda ya yi imani ya ce: “Ya ku mutanena, ku bi ni in nuna muku hanyar shiriya



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 39

يَٰقَوۡمِ إِنَّمَا هَٰذِهِ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا مَتَٰعٞ وَإِنَّ ٱلۡأٓخِرَةَ هِيَ دَارُ ٱلۡقَرَارِ

“Ya ku mutanena, lalle wannan rayuwar ta duniya xan jin daxi ne, kuma lalle lahira ita ce gidan tabbata



Sura: Suratu Ghafir

Aya : 40

مَنۡ عَمِلَ سَيِّئَةٗ فَلَا يُجۡزَىٰٓ إِلَّا مِثۡلَهَاۖ وَمَنۡ عَمِلَ صَٰلِحٗا مِّن ذَكَرٍ أَوۡ أُنثَىٰ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَأُوْلَـٰٓئِكَ يَدۡخُلُونَ ٱلۡجَنَّةَ يُرۡزَقُونَ فِيهَا بِغَيۡرِ حِسَابٖ

“Wanda ya aikata wani mummunan aiki, to ba za a saka masa ba sai da kwatankwacinsa, wanda kuwa ya aikata wani kyakkyawan aiki, namiji ne ko mace alhali shi yana mumini, to waxannan za su shiga Aljanna, a riqa arzuta su a cikinta ba tare da lissafi ba