أَفَتُمَٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ
Yanzu kwa riqa jayayya da shi kan abin da yake gani?
وَلَقَدۡ رَءَاهُ نَزۡلَةً أُخۡرَىٰ
Haqiqa ya gan shi (Jibrilu) a wani karon ma[1]
1- Watau lokacin Isra’i da Mi’iraji, inda ya gan shi a halittarsa ta asali.
عِندَ سِدۡرَةِ ٱلۡمُنتَهَىٰ
A wurin Magaryar tuqewa
عِندَهَا جَنَّةُ ٱلۡمَأۡوَىٰٓ
A wurinta ne Aljannar makoma take
إِذۡ يَغۡشَى ٱلسِّدۡرَةَ مَا يَغۡشَىٰ
A yayin da abin da ya lulluve Magaryar (na ban mamaki) ya lulluve ta
مَا زَاغَ ٱلۡبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ
Ganin (nasa) bai karkace ba, kuma bai zarme ba
لَقَدۡ رَأَىٰ مِنۡ ءَايَٰتِ رَبِّهِ ٱلۡكُبۡرَىٰٓ
Haqiqa ya ga wasu ayoyin Ubangijinsa manya-manya
أَفَرَءَيۡتُمُ ٱللَّـٰتَ وَٱلۡعُزَّىٰ
Ku ba ni labarin (gumakan) Lata da Uzza
وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰٓ
Da Manata cikon ta ukunsu
أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلۡأُنثَىٰ
Yanzu xa namiji zai zama naku, Shi kuma Ya tashi da ‘ya mace?
تِلۡكَ إِذٗا قِسۡمَةٞ ضِيزَىٰٓ
Idan haka ne wannan rabon na zalunci ne[1]
1- Domin ya qunshi Fifita mahaluki a kan Mahalicci.
إِنۡ هِيَ إِلَّآ أَسۡمَآءٞ سَمَّيۡتُمُوهَآ أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلۡطَٰنٍۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهۡوَى ٱلۡأَنفُسُۖ وَلَقَدۡ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلۡهُدَىٰٓ
Su ba komai ba ne face sunaye da kuka sa musu, ku da iyayenku, Allah bai saukar muku da wata hujja ba game da su. Ba abin da suke bi sai zato da son zuciya. Haqiqa kuwa shiriya ta zo musu daga Ubangijinsu
أَمۡ لِلۡإِنسَٰنِ مَا تَمَنَّىٰ
Ko kuwa sai mutum ya sami abin da yake buri ne?
فَلِلَّهِ ٱلۡأٓخِرَةُ وَٱلۡأُولَىٰ
To lahira da duniya duka na Allah ne
۞وَكَم مِّن مَّلَكٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغۡنِي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ أَن يَأۡذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرۡضَىٰٓ
Mala’iku nawa ne a cikin sammai cetonsu ba ya amfanar da komai sai da izinin Allah ga waxanda Ya ga dama Ya kuma yarda (da shi)?
إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ تَسۡمِيَةَ ٱلۡأُنثَىٰ
Lalle waxanda ba sa yin imani da ranar lahira suna kiran mala’iku da sunan mata
وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـٔٗا
Kuma ba su da wani ilimi game da haka; ba abin da suke bi sai zato; shi kuma zato, lalle ba ya wadatar da komai game da gaskiya
فَأَعۡرِضۡ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكۡرِنَا وَلَمۡ يُرِدۡ إِلَّا ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا
Sai ka kau da kai daga duk wanda ya ba da baya daga ambatonmu, bai kuma yi nufin komai ba sai rayuwar duniya
ذَٰلِكَ مَبۡلَغُهُم مِّنَ ٱلۡعِلۡمِۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱهۡتَدَىٰ
Wannan ne maqurar iliminsu. Lalle Ubangijinka Shi ne Ya fi sanin wanda ya vace daga hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin wanda ya shiriya
وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ لِيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ أَسَـٰٓـُٔواْ بِمَا عَمِلُواْ وَيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ أَحۡسَنُواْ بِٱلۡحُسۡنَى
Kuma abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa na Allah ne, don Ya saka wa waxanda suka munana da irin abin da suka aikata, Ya kuma saka wa waxanda suka kyautata da mafi kyan sakamako
ٱلَّذِينَ يَجۡتَنِبُونَ كَبَـٰٓئِرَ ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡفَوَٰحِشَ إِلَّا ٱللَّمَمَۚ إِنَّ رَبَّكَ وَٰسِعُ ٱلۡمَغۡفِرَةِۚ هُوَ أَعۡلَمُ بِكُمۡ إِذۡ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ وَإِذۡ أَنتُمۡ أَجِنَّةٞ فِي بُطُونِ أُمَّهَٰتِكُمۡۖ فَلَا تُزَكُّوٓاْ أَنفُسَكُمۡۖ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱتَّقَىٰٓ
(Su ne) waxanda suke nisantar manya-manyan zunubai da munanan ayyukan savo, sai dai ‘yan qananan zunubai. Lalle Ubangijinka Mayalwacin gafara ne. Shi ne Ya fi sanin ku, tun sanda Ya halicce ku daga qasa, sai ga ku kun zama ‘yan tayi a cikin cikin iyayenku mata; to kada ku tsarkake kanku; Shi ne Ya fi sanin wanda ya fi taqawa
أَفَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي تَوَلَّىٰ
Ka ba ni labarin wanda ya ba da baya
وَأَعۡطَىٰ قَلِيلٗا وَأَكۡدَىٰٓ
Ya kuma bayar da dukiya kaxan kuma ya yi rowa
أَعِندَهُۥ عِلۡمُ ٱلۡغَيۡبِ فَهُوَ يَرَىٰٓ
Shin yana da ilimin gaibu ne don haka yana ganin (komai)?
أَمۡ لَمۡ يُنَبَّأۡ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ
Ko ba a ba shi labarin abin da yake cikin takardun Musa ba ne?
وَإِبۡرَٰهِيمَ ٱلَّذِي وَفَّىٰٓ
Da kuma Ibrahimu wanda ya cika alqawari?
أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٞ وِزۡرَ أُخۡرَىٰ
Cewa: “Wani rai ba ya xaukar nauyin laifin wani
وَأَن لَّيۡسَ لِلۡإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ
“Kuma mutum bai mallaki wani sakamako ba sai na abin da ya aikata
وَأَنَّ سَعۡيَهُۥ سَوۡفَ يُرَىٰ
“Kuma lalle aikin nasa ba da daxewa ba za a gan shi
ثُمَّ يُجۡزَىٰهُ ٱلۡجَزَآءَ ٱلۡأَوۡفَىٰ
“Sannan a saka masa da cikakken sakamako