Sura: Suratul Balad

Aya : 16

أَوۡ مِسۡكِينٗا ذَا مَتۡرَبَةٖ

Ko miskini ma’abocin talauci



Sura: Suratul Balad

Aya : 17

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ

Sannan kuma ya zama daga waxanda suka yi imani, suka yi wa junansu wasiyya da yin haquri kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayawa



Sura: Suratul Balad

Aya : 18

أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ

Waxannan su ne ma’abota dama[1]


1- Watau ‘yan Aljanna.


Sura: Suratul Balad

Aya : 19

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ

Waxanda kuwa suka kafirce wa ayoyinmu, su ne ma’abota hagu[1]


1- Watau ‘yan wuta.


Sura: Suratul Balad

Aya : 20

عَلَيۡهِمۡ نَارٞ مُّؤۡصَدَةُۢ

A kansu akwai wuta abar kullewa



Sura: Suratus Shams

Aya : 1

وَٱلشَّمۡسِ وَضُحَىٰهَا

Na rantse da rana da walaharta



Sura: Suratus Shams

Aya : 2

وَٱلۡقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا

Da kuma wata idan ya bi ta (wato ranar)[1]


1- Watau ya biyo bayan faxuwar rana.


Sura: Suratus Shams

Aya : 3

وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا

Da kuma wuni idan ya bayyana ta



Sura: Suratus Shams

Aya : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰهَا

Da kuma dare idan ya lulluve ta



Sura: Suratus Shams

Aya : 5

وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا

Da kuma sama da gininta



Sura: Suratus Shams

Aya : 6

وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا طَحَىٰهَا

Da kuma qasa da shimfixarta



Sura: Suratus Shams

Aya : 7

وَنَفۡسٖ وَمَا سَوَّىٰهَا

Da kuma rai da daidaitarsa



Sura: Suratus Shams

Aya : 8

فَأَلۡهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقۡوَىٰهَا

Sai Ya kimsa masa (gane) lalacewarsa da taqawarsa



Sura: Suratus Shams

Aya : 9

قَدۡ أَفۡلَحَ مَن زَكَّىٰهَا

Haqiqa wanda ya tsarkake shi (ran) ya rabauta



Sura: Suratus Shams

Aya : 10

وَقَدۡ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا

Haqiqa kuma wanda ya binne shi da savo ya tave



Sura: Suratus Shams

Aya : 11

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِطَغۡوَىٰهَآ

Samudawa sun qaryata saboda xagawarsu



Sura: Suratus Shams

Aya : 12

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشۡقَىٰهَا

Yayin da mafi tsagerancinsu ya zabura



Sura: Suratus Shams

Aya : 13

فَقَالَ لَهُمۡ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقۡيَٰهَا

Sai Manzon Allah[1] ya ce da su: “Ku bar taguwar Allah da (ranar) shanta.”


1- Watau Annabi Salihu ().


Sura: Suratus Shams

Aya : 14

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمۡدَمَ عَلَيۡهِمۡ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمۡ فَسَوَّىٰهَا

Sai suka qaryata shi sannan suka soke ta, sai Ubangijinsu Ya kama su da azaba saboda zunubinsu, sai Ya daidaita ta (watau qabilar wajen azaba)



Sura: Suratus Shams

Aya : 15

وَلَا يَخَافُ عُقۡبَٰهَا

Kuma ba Ya tsoron abin da zai biyo bayanta[1]


1- Watau ba ya jin tsoron wani abu da hallaka su za ta haifar nan gaba.


Sura: Suratul Lail

Aya : 1

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰ

Na rantse da dare idan ya lulluve (da duhunsa)



Sura: Suratul Lail

Aya : 2

وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ

Da kuma wuni idan ya bayyana



Sura: Suratul Lail

Aya : 3

وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ

Da kuma halittar namiji da mace



Sura: Suratul Lail

Aya : 4

إِنَّ سَعۡيَكُمۡ لَشَتَّىٰ

Lalle aikinku ya sha bamban



Sura: Suratul Lail

Aya : 5

فَأَمَّا مَنۡ أَعۡطَىٰ وَٱتَّقَىٰ

To wanda ya ba da (haqqoqin da ke kansa) ya kuma yi taqawa



Sura: Suratul Lail

Aya : 6

وَصَدَّقَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ

Ya kuma gaskata (sakamako) mafi kyau



Sura: Suratul Lail

Aya : 7

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡيُسۡرَىٰ

To lalle ne za Mu sauqaqa masa (hanyar) Aljanna



Sura: Suratul Lail

Aya : 8

وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسۡتَغۡنَىٰ

Amma kuma wanda ya yi rowa (da haqqin Allah) ya kuma wadatu (da neman lada)



Sura: Suratul Lail

Aya : 9

وَكَذَّبَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ

Kuma ya qaryata (sakamako) mafi kyau



Sura: Suratul Lail

Aya : 10

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡعُسۡرَىٰ

To lalle ne za Mu hore masa (hanyar) wuta