Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 43

وَظِلّٖ مِّن يَحۡمُومٖ

Da kuma inuwa ta turnuqun hayaqi



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 44

لَّا بَارِدٖ وَلَا كَرِيمٍ

Ba mai sanyi ba, kuma ba mai daraja ba



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 45

إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَبۡلَ ذَٰلِكَ مُتۡرَفِينَ

Lalle su sun kasance masu holewa ne kafin wannan



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 46

وَكَانُواْ يُصِرُّونَ عَلَى ٱلۡحِنثِ ٱلۡعَظِيمِ

Sun kuma kasance suna dogewa a kan zunubi mai girma.[1]


1- Watau babban laifi na kafirci da bautar wanin Allah.


Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 47

وَكَانُواْ يَقُولُونَ أَئِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبۡعُوثُونَ

Sun kuma kasance suna cewa: “Yanzu idan mun mutu, mun zama qasa da qasusuwa, yanzu lalle za a tashe mu?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 48

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلۡأَوَّلُونَ

“Hakanan ma iyayenmu na farko?”



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 49

قُلۡ إِنَّ ٱلۡأَوَّلِينَ وَٱلۡأٓخِرِينَ

Ka ce: “Lalle na farkon da na qarshen



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 50

لَمَجۡمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَٰتِ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ

“Tabbas za a tattara su zuwa wani lokaci na rana sananniya



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 51

ثُمَّ إِنَّكُمۡ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلۡمُكَذِّبُونَ

“Sannan lalle ku kuma waxannan vatattu masu qaryatawa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 52

لَأٓكِلُونَ مِن شَجَرٖ مِّن زَقُّومٖ

“Tabbas za ku ci daga bishiyar Zaqqumu[1]


1- Watau wata bishiya ce mafi muni da sharri a wutar jahannama.


Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 53

فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ

“Sannan za ku cika cikunanku da ita



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 54

فَشَٰرِبُونَ عَلَيۡهِ مِنَ ٱلۡحَمِيمِ

“Sannan za ku sha tafasasshen ruwa a kanta



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 55

فَشَٰرِبُونَ شُرۡبَ ٱلۡهِيمِ

“Sannan za ku sha irin shan raquma masu jin qishirwa.”



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 56

هَٰذَا نُزُلُهُمۡ يَوۡمَ ٱلدِّينِ

Wannan ita ce gararsu a ranar sakamako



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 57

نَحۡنُ خَلَقۡنَٰكُمۡ فَلَوۡلَا تُصَدِّقُونَ

Mu ne Muka halicce ku, me ya sa ba kwa gaskatawa?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 58

أَفَرَءَيۡتُم مَّا تُمۡنُونَ

Ba kwa ganin maniyyi da kuke zubawa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 59

ءَأَنتُمۡ تَخۡلُقُونَهُۥٓ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡخَٰلِقُونَ

Shin ku ne kuke halittar sa, ko kuwa Mu ne Masu halittar?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 60

نَحۡنُ قَدَّرۡنَا بَيۡنَكُمُ ٱلۡمَوۡتَ وَمَا نَحۡنُ بِمَسۡبُوقِينَ

Mu ne Muke qaddara mutuwa a tsakaninku, kuma Mu ba Masu gajiyawa ba ne



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 61

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمۡثَٰلَكُمۡ وَنُنشِئَكُمۡ فِي مَا لَا تَعۡلَمُونَ

A kan Mu musanya irinku Mu kuma halitta ku cikin abin da ba ku sani ba



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 62

وَلَقَدۡ عَلِمۡتُمُ ٱلنَّشۡأَةَ ٱلۡأُولَىٰ فَلَوۡلَا تَذَكَّرُونَ

Haqiqa kuma ku kun san halitta ta farko, don me ba kwa wa’azantuwa?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 63

أَفَرَءَيۡتُم مَّا تَحۡرُثُونَ

Ku ba Ni labarin abin da kuke nomawa?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 64

ءَأَنتُمۡ تَزۡرَعُونَهُۥٓ أَمۡ نَحۡنُ ٱلزَّـٰرِعُونَ

Shin ku ne kuke tsiro da shi, ko Mu ne Masu tsirarwar?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 65

لَوۡ نَشَآءُ لَجَعَلۡنَٰهُ حُطَٰمٗا فَظَلۡتُمۡ تَفَكَّهُونَ

Idan da Mun ga dama tabbas da Mun mayar da shi karmami, sai ku wayi gari kuna mamaki



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 66

إِنَّا لَمُغۡرَمُونَ

(Kuna cewa): “Lalle mu an xora mana asara.”



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 67

بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ

“A’a, mu dai an hana mu ne.”



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 68

أَفَرَءَيۡتُمُ ٱلۡمَآءَ ٱلَّذِي تَشۡرَبُونَ

Ku ba Ni labarin ruwa wanda kuke sha



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 69

ءَأَنتُمۡ أَنزَلۡتُمُوهُ مِنَ ٱلۡمُزۡنِ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡمُنزِلُونَ

Yanzu ku ne kuke sauko da shi daga girgije, ko kuwa Mu ne masu saukarwar?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 70

لَوۡ نَشَآءُ جَعَلۡنَٰهُ أُجَاجٗا فَلَوۡلَا تَشۡكُرُونَ

Da Mun ga dama da Mun mayar da shi (ruwa) mai zartsi, to don me ba kwa godewa?



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 71

أَفَرَءَيۡتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِي تُورُونَ

Ku ba Ni labarin wutar da kuke kunnawa



Sura: Suratul Waqi’a

Aya : 72

ءَأَنتُمۡ أَنشَأۡتُمۡ شَجَرَتَهَآ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡمُنشِـُٔونَ

Yanzu ku ne kuka halicci bishiyarta, ko kuwa Mu ne Masu halittar?