Sura: Suratul Haqqa

Aya : 39

وَمَا لَا تُبۡصِرُونَ

Da kuma abin da ba kwa gani



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 40

إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ

Lalle shi (Alqur’ani) tabbas zance ne na wani manzo mai girma



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 41

وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَاعِرٖۚ قَلِيلٗا مَّا تُؤۡمِنُونَ

Shi kuwa ba zancen mawaqi ba ne. Kaxan ne qwarai kuke yin imani



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 42

وَلَا بِقَوۡلِ كَاهِنٖۚ قَلِيلٗا مَّا تَذَكَّرُونَ

Ba kuma zance ne na boka ba. Kaxan ne qwarai kuke wa’azantuwa



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 43

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Shi saukakke ne daga Ubangijin halittu



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 44

وَلَوۡ تَقَوَّلَ عَلَيۡنَا بَعۡضَ ٱلۡأَقَاوِيلِ

Kuma da ya qaga Mana wasu maganganu



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 45

لَأَخَذۡنَا مِنۡهُ بِٱلۡيَمِينِ

Tabbas da Mun kama shi da qarfi



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 46

ثُمَّ لَقَطَعۡنَا مِنۡهُ ٱلۡوَتِينَ

Sannan da Mun yanke masa jijiyar zuciyarsa



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 47

فَمَا مِنكُم مِّنۡ أَحَدٍ عَنۡهُ حَٰجِزِينَ

Sannan kuma ba wani xaya daga cikinku da zai kare shi



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 48

وَإِنَّهُۥ لَتَذۡكِرَةٞ لِّلۡمُتَّقِينَ

Lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne ga masu kiyaye dokokin Allah



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 49

وَإِنَّا لَنَعۡلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ

Lalle kuma Mu Muna sane da cewa a cikinku akwai masu qaryatawa



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 50

وَإِنَّهُۥ لَحَسۡرَةٌ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma lalle shi tabbas nadama ce ga kafirai



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 51

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلۡيَقِينِ

Kuma lalle shi tabbas gaskiya ce ta sakankancewa



Sura: Suratul Haqqa

Aya : 52

فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ

Saboda haka ka yi tasbihi da sunan Ubangijinka Mai girma



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 1

سَأَلَ سَآئِلُۢ بِعَذَابٖ وَاقِعٖ

Mai tambaya ya yi tambaya game da wata azaba mai aukuwa[1]


1- Watau wadda Annabi () yake musu kashedi da ita idan sun qi imani. Duba Suratul Anfal, aya ta 32. Mai tambayar kuwa shi ne Nadhru xan Haris.


Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 2

لِّلۡكَٰفِرِينَ لَيۡسَ لَهُۥ دَافِعٞ

Ga kafirai (wadda) ba ta da wani mai kaxe ta



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِي ٱلۡمَعَارِجِ

Daga Allah Mai matattakalai



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 4

تَعۡرُجُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيۡهِ فِي يَوۡمٖ كَانَ مِقۡدَارُهُۥ خَمۡسِينَ أَلۡفَ سَنَةٖ

Mala’iku tare da Jibrilu suna hawa zuwa gare Shi a cikin wata rana (wadda) gwargwadonta yake daidai da shekara dubu hamsin



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 5

فَٱصۡبِرۡ صَبۡرٗا جَمِيلًا

Sai ka yi haquri kyakkyawan haquri



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 6

إِنَّهُمۡ يَرَوۡنَهُۥ بَعِيدٗا

Lalle su suna ganin ta mai nisa ce



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبٗا

Mu kuma Muna ganin ta kusa-kusa



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 8

يَوۡمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلۡمُهۡلِ

A ranar da sama za ta kasance kamar narkakkiyar dalma



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 9

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga (ta gashin tumaki)



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 10

وَلَا يَسۡـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمٗا

Kuma aboki ba ya tambayar aboki



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 11

يُبَصَّرُونَهُمۡۚ يَوَدُّ ٱلۡمُجۡرِمُ لَوۡ يَفۡتَدِي مِنۡ عَذَابِ يَوۡمِئِذِۭ بِبَنِيهِ

(Alhali kuma) ana nuna musu junansu. Mai laifi ya riqa burin ina ma zai fanshi kansa daga azabar wannan rana da ‘ya’yansa



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 12

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

Da matarsa da xan’uwansa



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِي تُـٔۡوِيهِ

Da danginsa waxanda suke kare shi



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 14

وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ يُنجِيهِ

Da ma duk wanda yake a bayan qasa baki xaya, sannan (fansar) ta tserar da shi



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai