Sura: Suratu Abasa

Aya : 35

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

Da uwarsa da ubansa



Sura: Suratu Abasa

Aya : 36

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

Da matarsa da ‘ya’yansa



Sura: Suratu Abasa

Aya : 37

لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ

Kowane mutum daga cikinsu a wannan ranar yana da lamarin da ya sha kansa



Sura: Suratu Abasa

Aya : 38

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ

Wasu fuskoki a wannan ranar masu haske ne



Sura: Suratu Abasa

Aya : 39

ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ

Masu dariya, masu farin ciki



Sura: Suratu Abasa

Aya : 40

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ

Wasu fuskokin kuma a ranar akwai qura a kansu



Sura: Suratu Abasa

Aya : 41

تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ

Baqin ciki zai lulluve su



Sura: Suratu Abasa

Aya : 42

أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ

Waxannan su ne kafirai mavarnata



Sura: Suratut Takwir

Aya : 1

إِذَا ٱلشَّمۡسُ كُوِّرَتۡ

Idan rana aka naxe ta[1]


1- Watau aka haxa ta da wata wuri xaya, aka kuma tafiyar da haskenta.


Sura: Suratut Takwir

Aya : 2

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتۡ

Idan kuma taurari suka farfaxo



Sura: Suratut Takwir

Aya : 3

وَإِذَا ٱلۡجِبَالُ سُيِّرَتۡ

Idan kuma duwatsu aka tafiyar da su



Sura: Suratut Takwir

Aya : 4

وَإِذَا ٱلۡعِشَارُ عُطِّلَتۡ

Idan kuma raquma masu ciki aka bar su ba makiyayi



Sura: Suratut Takwir

Aya : 5

وَإِذَا ٱلۡوُحُوشُ حُشِرَتۡ

Idan kuma namun daji aka tattara su[1]


1- Watau aka tattara su wuri guda tare da ‘yan’adam.


Sura: Suratut Takwir

Aya : 6

وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ سُجِّرَتۡ

Idan kuma koguna aka rura su (suka zama wuta)



Sura: Suratut Takwir

Aya : 7

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتۡ

Idan kuma rayuka aka haxa su (da jinsinsu)



Sura: Suratut Takwir

Aya : 8

وَإِذَا ٱلۡمَوۡءُۥدَةُ سُئِلَتۡ

Idan kuma yarinyar da aka binne da rai aka tambaye ta



Sura: Suratut Takwir

Aya : 9

بِأَيِّ ذَنۢبٖ قُتِلَتۡ

Da wane laifi ne aka kashe ta?



Sura: Suratut Takwir

Aya : 10

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتۡ

Idan kuma takardun (ayyuka) aka baza su[1]


1- Watau don kowa ya karanta takardarsa da kansa.


Sura: Suratut Takwir

Aya : 11

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتۡ

Idan kuma sama aka xaye ta



Sura: Suratut Takwir

Aya : 12

وَإِذَا ٱلۡجَحِيمُ سُعِّرَتۡ

Idan kuma wutar Jahimu aka hura ta



Sura: Suratut Takwir

Aya : 13

وَإِذَا ٱلۡجَنَّةُ أُزۡلِفَتۡ

Idan kuma Aljanna aka kusanto da ita[1]


1- Watau aka matso da ita dab da masu taqawa.


Sura: Suratut Takwir

Aya : 14

عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّآ أَحۡضَرَتۡ

To kowane rai ya san abin da ya halarto (da shi na ayyuka)



Sura: Suratut Takwir

Aya : 15

فَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلۡخُنَّسِ

To ina rantsuwa da taurari masu vuya[1]


1- Watau suna vuya lokacin hudowar hasken asuba, kamar yadda gada take voyewa a cikin gidanta.


Sura: Suratut Takwir

Aya : 16

ٱلۡجَوَارِ ٱلۡكُنَّسِ

Masu gudu zuwa masaukansu



Sura: Suratut Takwir

Aya : 17

وَٱلَّيۡلِ إِذَا عَسۡعَسَ

Da kuma dare idan ya yi duhu



Sura: Suratut Takwir

Aya : 18

وَٱلصُّبۡحِ إِذَا تَنَفَّسَ

Da kuma asuba idan ta keto



Sura: Suratut Takwir

Aya : 19

إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ

Lalle shi (Alqur’ani) magana ce ta Manzo mai karamci[1]


1- Watau Mala’ika Jibrilu () wanda Allah ya amince masa ya isar wa da Manzon Allah () zancensa.


Sura: Suratut Takwir

Aya : 20

ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي ٱلۡعَرۡشِ مَكِينٖ

Ma’abocin qarfi a wurin Mai Al’arshi, kuma mai babban matsayi



Sura: Suratut Takwir

Aya : 21

مُّطَاعٖ ثَمَّ أَمِينٖ

Wanda ake yi wa biyayya ne a can (sama), amintacce



Sura: Suratut Takwir

Aya : 22

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجۡنُونٖ

Mutumin naku kuma (watau Ma’aiki) ba mahaukaci ba ne