Sura: Suratul Jasiya

Aya : 26

قُلِ ٱللَّهُ يُحۡيِيكُمۡ ثُمَّ يُمِيتُكُمۡ ثُمَّ يَجۡمَعُكُمۡ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ لَا رَيۡبَ فِيهِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Ka ce: “Allah ne zai raya ku sannan ya kashe ku sannan ya tara ku a ranar alqiyama wadda babu kokwanto game da ita, sai dai kuma yawancin mutane ba sa sanin (haka).”



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 27

وَلِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ يَوۡمَئِذٖ يَخۡسَرُ ٱلۡمُبۡطِلُونَ

Mulkin sammai da qasa kuma na Allah ne. Kuma ranar da alqiyama za ta tashi, a wannan ranar mavarnata za su yi asara



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 28

وَتَرَىٰ كُلَّ أُمَّةٖ جَاثِيَةٗۚ كُلُّ أُمَّةٖ تُدۡعَىٰٓ إِلَىٰ كِتَٰبِهَا ٱلۡيَوۡمَ تُجۡزَوۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Za kuma ka ga kowace al’umma a durqushe, kowace al’umma ana kiran ta zuwa ga littafinta, a wannan rana ne za a saka muku abin da kuka kasance kuna aikatawa



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 29

هَٰذَا كِتَٰبُنَا يَنطِقُ عَلَيۡكُم بِٱلۡحَقِّۚ إِنَّا كُنَّا نَسۡتَنسِخُ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

(Za a ce da su): “Wannan Littafinmu ne da yake yi muku furuci da gaskiya[1]. Lalle Mu mun kasance Muna rubuta abin da kuka kasance kuna aikatawa[2].”


1- Watau littafin da mala’iku suka rubuta na ayyukansu yana ba da shaida a kansu da tsantsar gaskiya.


2- Domin Allah ne da kansa ya umarci waxannan mala’ikun su riqa rubuta ayyukan mutane a duniya.


Sura: Suratul Jasiya

Aya : 30

فَأَمَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَيُدۡخِلُهُمۡ رَبُّهُمۡ فِي رَحۡمَتِهِۦۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡمُبِينُ

To amma waxanda suka yi imani suka yi ayyuka nagari, to Ubangijinsu zai shigar da su cikin rahamarsa. Wannan shi ne rabo mabayyani



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 31

وَأَمَّا ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَفَلَمۡ تَكُنۡ ءَايَٰتِي تُتۡلَىٰ عَلَيۡكُمۡ فَٱسۡتَكۡبَرۡتُمۡ وَكُنتُمۡ قَوۡمٗا مُّجۡرِمِينَ

Amma kuma waxanda suka kafirce (za a ce da su): “Yanzu ashe ayoyina ba su kasance ana karanta muku su ba, sai kuka yi girman kai, kuka kasance mutane masu manyan laifuka?”



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 32

وَإِذَا قِيلَ إِنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞ وَٱلسَّاعَةُ لَا رَيۡبَ فِيهَا قُلۡتُم مَّا نَدۡرِي مَا ٱلسَّاعَةُ إِن نَّظُنُّ إِلَّا ظَنّٗا وَمَا نَحۡنُ بِمُسۡتَيۡقِنِينَ

Idan kuma aka ce, lalle alqawarin Allah gaskiya ne, alqiyama kuma babu kokwanto a game da ita kukan ce: “Mu ba mu da sanin mece ce ma alqiyama, mu ba abin da muke tsammani (game da ita) sai zato, mu kuma ba mu da tabbas.”



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 33

وَبَدَا لَهُمۡ سَيِّـَٔاتُ مَا عَمِلُواْ وَحَاقَ بِهِم مَّا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ

Kuma irin munanan ayyukan da suka aikata suka bayyana a gare su, kuma abin da suka kasance suna yi wa izgili ya saukar musu



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 34

وَقِيلَ ٱلۡيَوۡمَ نَنسَىٰكُمۡ كَمَا نَسِيتُمۡ لِقَآءَ يَوۡمِكُمۡ هَٰذَا وَمَأۡوَىٰكُمُ ٱلنَّارُ وَمَا لَكُم مِّن نَّـٰصِرِينَ

Aka kuma ce: “A yau za Mu manta da ku[1] kamar yadda kuka manta haxuwarku da wannan rana taku, makomarku kuma wuta ce, kuma ba ku da wasu mataimaka


1- Watau zai bar su a cikin wuta ya yi watsi da su, sakamakon mantawa da suka yi da wannan ranar.


Sura: Suratul Jasiya

Aya : 35

ذَٰلِكُم بِأَنَّكُمُ ٱتَّخَذۡتُمۡ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ هُزُوٗا وَغَرَّتۡكُمُ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَاۚ فَٱلۡيَوۡمَ لَا يُخۡرَجُونَ مِنۡهَا وَلَا هُمۡ يُسۡتَعۡتَبُونَ

“Wannan kuwa saboda lalle kun xauki ayoyin Allah abin yi wa izgili, rayuwar duniya kuma ta ruxe ku.” To a yau ba za a fitar da su daga cikinta ba, kuma su ba za a nemi su kawo hanzarinsu ba



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 36

فَلِلَّهِ ٱلۡحَمۡدُ رَبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَرَبِّ ٱلۡأَرۡضِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

To yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin sammai kuma Ubangijin qasa, Ubangijin talikai



Sura: Suratul Jasiya

Aya : 37

وَلَهُ ٱلۡكِبۡرِيَآءُ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Girma nasa ne a cikin sammai da qasa, kuma Shi ne Mabuwayi, Mai hikima