تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ
Tana kiran wanda ya juya ya ba da baya
Tarayya :
وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ
Ya kuma tara (dukiya) sai ya voye (ta)
۞إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا
Lalle mutum an halicce shi mai rashin nutsuwa ne
إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعٗا
(Watau) idan sharri ya same shi ya zama mai raki
وَإِذَا مَسَّهُ ٱلۡخَيۡرُ مَنُوعًا
Idan kuma alheri ya same shi ya zama mai maqo
إِلَّا ٱلۡمُصَلِّينَ
Sai dai masallata
ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ
Waxanda suke masu dawwama a kan sallarsu
وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ
Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu
لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ
Ga mai roqo da wanda ake hana wa (saboda ba ya roqo)
وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ
Waxanda kuma suke gaskata ranar sakamako
وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ
Waxanda kuma suke tsoron azabar Ubangijinsu
إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ
Lalle azabar Ubangijinsu ba abar amincewa ba ce
وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ
Waxanda kuma suke kiyaye al’aurarsu (daga yin zina)
إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ
Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne
فَمَنِ ٱبۡتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡعَادُونَ
To duk wanda ya nemi (wani abu) bayan wannan, to waxannan su ne masu qetare iyaka
وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِأَمَٰنَٰتِهِمۡ وَعَهۡدِهِمۡ رَٰعُونَ
Waxanda kuma suke kiyaye amanoninsu da alqawuransu
وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَٰدَٰتِهِمۡ قَآئِمُونَ
Waxanda kuma suke tsai da shaidarsu
وَٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ يُحَافِظُونَ
Waxanda kuma suke kiyaye sallolinsu
أُوْلَـٰٓئِكَ فِي جَنَّـٰتٖ مُّكۡرَمُونَ
Waxannan su ne waxanda ake girmamawa cikin gidajen Aljanna
فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ قِبَلَكَ مُهۡطِعِينَ
To me ya sami waxanda suka kafirta suke gaggawa zuwa gare ka?
عَنِ ٱلۡيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ
Qungiya-qungiya, ta damanka da ta hagunka
أَيَطۡمَعُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُدۡخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٖ
Yanzu ashe kowane mutum daga cikinsu yana kwaxayin a shigar da shi Aljannar ni’ima?
كَلَّآۖ إِنَّا خَلَقۡنَٰهُم مِّمَّا يَعۡلَمُونَ
Faufau! Lalle Mu Mun halitta su daga abin da suka sani.[1]
1- Watau wulaqantaccen ruwa na maniyyi.
فَلَآ أُقۡسِمُ بِرَبِّ ٱلۡمَشَٰرِقِ وَٱلۡمَغَٰرِبِ إِنَّا لَقَٰدِرُونَ
To, ina yin rantsuwa da Ubangijin wuraren hudowar rana da wuraren faxuwarta, lalle Mu Masu iko ne
عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيۡرٗا مِّنۡهُمۡ وَمَا نَحۡنُ بِمَسۡبُوقِينَ
A kan Mu musanya wasu fiye da su, kuma Mu ba Masu kasawa ba ne
فَذَرۡهُمۡ يَخُوضُواْ وَيَلۡعَبُواْ حَتَّىٰ يُلَٰقُواْ يَوۡمَهُمُ ٱلَّذِي يُوعَدُونَ
To ka qyale su su kutsa su yi wasa har sai sun haxu da ranarsu wadda ake yi musu alqawarinta
يَوۡمَ يَخۡرُجُونَ مِنَ ٱلۡأَجۡدَاثِ سِرَاعٗا كَأَنَّهُمۡ إِلَىٰ نُصُبٖ يُوفِضُونَ
A ranar da za su fito daga qaburbura a gurguje, kai ka ce su suna gaggawa ne zuwa ga wata tuta (ta matattara)
خَٰشِعَةً أَبۡصَٰرُهُمۡ تَرۡهَقُهُمۡ ذِلَّةٞۚ ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمُ ٱلَّذِي كَانُواْ يُوعَدُونَ
Idanuwansu a qasqance, wulaqanci ya lulluve su. Wannan ne ranar da ake yi musu alqawarinta
إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوۡمِهِۦٓ أَنۡ أَنذِرۡ قَوۡمَكَ مِن قَبۡلِ أَن يَأۡتِيَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ
Lalle Mu Mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa cewa: “Ka gargaxi mutanenka tun kafin azaba mai raxaxi ta zo musu.”
قَالَ يَٰقَوۡمِ إِنِّي لَكُمۡ نَذِيرٞ مُّبِينٌ
Ya ce: “Ya ku mutanena, lalle ni mai gargaxi ne mabayyani a gare ku