Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 17

تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ

Tana kiran wanda ya juya ya ba da baya



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 18

وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ

Ya kuma tara (dukiya) sai ya voye (ta)



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 19

۞إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا

Lalle mutum an halicce shi mai rashin nutsuwa ne



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 20

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعٗا

(Watau) idan sharri ya same shi ya zama mai raki



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 21

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلۡخَيۡرُ مَنُوعًا

Idan kuma alheri ya same shi ya zama mai maqo



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 22

إِلَّا ٱلۡمُصَلِّينَ

Sai dai masallata



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 23

ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ

Waxanda suke masu dawwama a kan sallarsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 24

وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ

Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

Ga mai roqo da wanda ake hana wa (saboda ba ya roqo)



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

Waxanda kuma suke gaskata ranar sakamako



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ

Waxanda kuma suke tsoron azabar Ubangijinsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ

Lalle azabar Ubangijinsu ba abar amincewa ba ce



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 29

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye al’aurarsu (daga yin zina)



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 31

فَمَنِ ٱبۡتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡعَادُونَ

To duk wanda ya nemi (wani abu) bayan wannan, to waxannan su ne masu qetare iyaka



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 32

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِأَمَٰنَٰتِهِمۡ وَعَهۡدِهِمۡ رَٰعُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye amanoninsu da alqawuransu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 33

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَٰدَٰتِهِمۡ قَآئِمُونَ

Waxanda kuma suke tsai da shaidarsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 34

وَٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ يُحَافِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye sallolinsu



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 35

أُوْلَـٰٓئِكَ فِي جَنَّـٰتٖ مُّكۡرَمُونَ

Waxannan su ne waxanda ake girmamawa cikin gidajen Aljanna



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 36

فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ قِبَلَكَ مُهۡطِعِينَ

To me ya sami waxanda suka kafirta suke gaggawa zuwa gare ka?



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 37

عَنِ ٱلۡيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ

Qungiya-qungiya, ta damanka da ta hagunka



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 38

أَيَطۡمَعُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُدۡخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٖ

Yanzu ashe kowane mutum daga cikinsu yana kwaxayin a shigar da shi Aljannar ni’ima?



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 39

كَلَّآۖ إِنَّا خَلَقۡنَٰهُم مِّمَّا يَعۡلَمُونَ

Faufau! Lalle Mu Mun halitta su daga abin da suka sani.[1]


1- Watau wulaqantaccen ruwa na maniyyi.


Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 40

فَلَآ أُقۡسِمُ بِرَبِّ ٱلۡمَشَٰرِقِ وَٱلۡمَغَٰرِبِ إِنَّا لَقَٰدِرُونَ

To, ina yin rantsuwa da Ubangijin wuraren hudowar rana da wuraren faxuwarta, lalle Mu Masu iko ne



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 41

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيۡرٗا مِّنۡهُمۡ وَمَا نَحۡنُ بِمَسۡبُوقِينَ

A kan Mu musanya wasu fiye da su, kuma Mu ba Masu kasawa ba ne



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 42

فَذَرۡهُمۡ يَخُوضُواْ وَيَلۡعَبُواْ حَتَّىٰ يُلَٰقُواْ يَوۡمَهُمُ ٱلَّذِي يُوعَدُونَ

To ka qyale su su kutsa su yi wasa har sai sun haxu da ranarsu wadda ake yi musu alqawarinta



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 43

يَوۡمَ يَخۡرُجُونَ مِنَ ٱلۡأَجۡدَاثِ سِرَاعٗا كَأَنَّهُمۡ إِلَىٰ نُصُبٖ يُوفِضُونَ

A ranar da za su fito daga qaburbura a gurguje, kai ka ce su suna gaggawa ne zuwa ga wata tuta (ta matattara)



Sura: Suratul Ma’arij

Aya : 44

خَٰشِعَةً أَبۡصَٰرُهُمۡ تَرۡهَقُهُمۡ ذِلَّةٞۚ ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمُ ٱلَّذِي كَانُواْ يُوعَدُونَ

Idanuwansu a qasqance, wulaqanci ya lulluve su. Wannan ne ranar da ake yi musu alqawarinta



Sura: Suratu Nuh

Aya : 1

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوۡمِهِۦٓ أَنۡ أَنذِرۡ قَوۡمَكَ مِن قَبۡلِ أَن يَأۡتِيَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Lalle Mu Mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa cewa: “Ka gargaxi mutanenka tun kafin azaba mai raxaxi ta zo musu.”



Sura: Suratu Nuh

Aya : 2

قَالَ يَٰقَوۡمِ إِنِّي لَكُمۡ نَذِيرٞ مُّبِينٌ

Ya ce: “Ya ku mutanena, lalle ni mai gargaxi ne mabayyani a gare ku