Sura: Suratut Takwir

Aya : 23

وَلَقَدۡ رَءَاهُ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡمُبِينِ

Haqiqa kuma ya gan shi a sararin sama mabayyani[1]


1- Watau Annabi () ya ga Mala’ika Jibrilu () a surarsa ta asali a sararin samaniya.


Sura: Suratut Takwir

Aya : 24

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلۡغَيۡبِ بِضَنِينٖ

Shi kuma ba mai rowa ba ne game da wahayi



Sura: Suratut Takwir

Aya : 25

وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَيۡطَٰنٖ رَّجِيمٖ

Kuma shi (Alqur’ani) ba zancen Shaixan ne la’ananne ba



Sura: Suratut Takwir

Aya : 26

فَأَيۡنَ تَذۡهَبُونَ

To ina za ku dosa ne[1]?


1- Watau ina mushirikai suka dosa wajen qaryata Alqur’an bayan sun ji hujjoji masu qarfi?


Sura: Suratut Takwir

Aya : 27

إِنۡ هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ

Shi ba wani abu ba ne sai wa’azi ga talikai



Sura: Suratut Takwir

Aya : 28

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَسۡتَقِيمَ

Ga wanda ya ga dama daga cikinku ya bi hanya madaidaiciya



Sura: Suratut Takwir

Aya : 29

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ku kuma ba za ku iya ganin dama ba sai Allah Ubangijin talikai Ya ga dama



Sura: Suratul Infixar

Aya : 1

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتۡ

Idan sama ta tsattsage



Sura: Suratul Infixar

Aya : 2

وَإِذَا ٱلۡكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتۡ

Idan kuma taurari suka farfaxo suka tarwatse



Sura: Suratul Infixar

Aya : 3

وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ فُجِّرَتۡ

Idan kuma koguna aka harhaxe su



Sura: Suratul Infixar

Aya : 4

وَإِذَا ٱلۡقُبُورُ بُعۡثِرَتۡ

Idan kuma qaburbura aka fito da matattun da ke cikinsu



Sura: Suratul Infixar

Aya : 5

عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّا قَدَّمَتۡ وَأَخَّرَتۡ

Kowane rai ya san abin da ya gabatar da wanda ya jirkintar



Sura: Suratul Infixar

Aya : 6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡإِنسَٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلۡكَرِيمِ

Ya kai mutum, me ya ruxe ka ne game da Ubangijinka Mai karamci?



Sura: Suratul Infixar

Aya : 7

ٱلَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ

Wanda Ya halicce ka Ya kuma daidaita ka Ya miqar da kai[1]?


1- Watau ya lura da girman ni’imar da ya yi masa yayin da bai yi masa irin halittar jaki ba ko ta biri ko ta kare.


Sura: Suratul Infixar

Aya : 8

فِيٓ أَيِّ صُورَةٖ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ

Ya harhaxa ka cikin irin surar da Ya ga dama?



Sura: Suratul Infixar

Aya : 9

كَلَّا بَلۡ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ

A’a dai, kawai dai kuna qaryata ranar sakamako ne



Sura: Suratul Infixar

Aya : 10

وَإِنَّ عَلَيۡكُمۡ لَحَٰفِظِينَ

Kuma lalle akwai masu kula da ku[1]


1- Watau mala’iku.


Sura: Suratul Infixar

Aya : 11

كِرَامٗا كَٰتِبِينَ

Masu daraja marubuta



Sura: Suratul Infixar

Aya : 12

يَعۡلَمُونَ مَا تَفۡعَلُونَ

Suna sane da abin da kuke aikatawa



Sura: Suratul Infixar

Aya : 13

إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٖ

Lalle mutanen kirki tabbas suna cikin ni’ima



Sura: Suratul Infixar

Aya : 14

وَإِنَّ ٱلۡفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٖ

Lalle kuma fajirai tabbas suna cikin (wutar) Jahima



Sura: Suratul Infixar

Aya : 15

يَصۡلَوۡنَهَا يَوۡمَ ٱلدِّينِ

Za su qonu da ita ranar sakamako



Sura: Suratul Infixar

Aya : 16

وَمَا هُمۡ عَنۡهَا بِغَآئِبِينَ

Kuma su ba masu rabuwa ne da ita ba



Sura: Suratul Infixar

Aya : 17

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Sura: Suratul Infixar

Aya : 18

ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Sura: Suratul Infixar

Aya : 19

يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ

(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 1

وَيۡلٞ لِّلۡمُطَفِّفِينَ

Tsananin azaba ya tabbata ga masu tauye ma’auni



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 2

ٱلَّذِينَ إِذَا ٱكۡتَالُواْ عَلَى ٱلنَّاسِ يَسۡتَوۡفُونَ

Waxanda idan suka auna daga wajen mutane suna cikawa fal



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 3

وَإِذَا كَالُوهُمۡ أَو وَّزَنُوهُمۡ يُخۡسِرُونَ

Idan kuwa su za su aunar, da mudu ne ko da sikeli, to sai su tauye



Sura: Suratul Muxaffifin

Aya : 4

أَلَا يَظُنُّ أُوْلَـٰٓئِكَ أَنَّهُم مَّبۡعُوثُونَ

Yanzu waxannan ba sa zaton cewa su lalle za a tashe su?