Sura: Suratus Saffat

Aya : 125

أَتَدۡعُونَ بَعۡلٗا وَتَذَرُونَ أَحۡسَنَ ٱلۡخَٰلِقِينَ

“Yanzu kwa riqa bauta wa (gunkin) Ba’alu ku riqa barin Mafi iya kyautata halitta?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 126

ٱللَّهَ رَبَّكُمۡ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ

“(Wato) Allah Ubangijinku kuma Ubangijin iyayenku na farko?”



Sura: Suratus Saffat

Aya : 127

فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ

Sai suka qaryata shi, to don haka, lalle za a halarto da su (wuta)



Sura: Suratus Saffat

Aya : 128

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Sai dai bayin Allah waxanda aka tsarkake



Sura: Suratus Saffat

Aya : 129

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare shi ga ‘yan baya



Sura: Suratus Saffat

Aya : 130

سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِلۡ يَاسِينَ

Aminci ya tabbata ga Ilyasu



Sura: Suratus Saffat

Aya : 131

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Sura: Suratus Saffat

Aya : 132

إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle shi yana daga bayinmu muminai



Sura: Suratus Saffat

Aya : 133

وَإِنَّ لُوطٗا لَّمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Lalle kuma Luxu tabbas yana daga cikin manzanni



Sura: Suratus Saffat

Aya : 134

إِذۡ نَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

(Ka tuna) sanda Muka tserar da shi tare da iyalinsa baki xaya



Sura: Suratus Saffat

Aya : 135

إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai dai wata tsohuwa (wato matarsa) da take cikin halakakku



Sura: Suratus Saffat

Aya : 136

ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka hallakar da sauran



Sura: Suratus Saffat

Aya : 137

وَإِنَّكُمۡ لَتَمُرُّونَ عَلَيۡهِم مُّصۡبِحِينَ

Kuma lalle ku[1] tabbas kuna wucewa ta wajan (gidajensu) da asussuba


1- Watau ku mutanen Makka.


Sura: Suratus Saffat

Aya : 138

وَبِٱلَّيۡلِۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Da kuma cikin dare. Yanzu ba kwa hankalta ba?



Sura: Suratus Saffat

Aya : 139

وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Kuma lalle Yunusa tabbas yana daga cikin manzanni



Sura: Suratus Saffat

Aya : 140

إِذۡ أَبَقَ إِلَى ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ

(Ka tuna) lokacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwan da yake maqare



Sura: Suratus Saffat

Aya : 141

فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلۡمُدۡحَضِينَ

Sannan ya shiga quri’a, sai ya zama cikin waxanda aka yi galaba a kansu



Sura: Suratus Saffat

Aya : 142

فَٱلۡتَقَمَهُ ٱلۡحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٞ

Sai kifi ya haxiye shi, alhali yana abin zargi[1]


1- Watau a kan guduwa ya bar mutanensa ba tare da izinin Allah ba.


Sura: Suratus Saffat

Aya : 143

فَلَوۡلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلۡمُسَبِّحِينَ

Ba don dai shi ya zama daga masu tsarkake Allah (da yawan tasbihi) ba



Sura: Suratus Saffat

Aya : 144

لَلَبِثَ فِي بَطۡنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ

Tabbas da ya zauna a cikin cikinsa har zuwa ranar da za a tashe su[1]


1- Watau ranar alqiyama, domin zai zama shi ne qabarinsa.