لِيَوۡمٍ عَظِيمٖ
A wata rana mai girma?
Tarayya :
يَوۡمَ يَقُومُ ٱلنَّاسُ لِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Ranar da mutane za su tsaya gaban Ubangijin talikai?
كَلَّآ إِنَّ كِتَٰبَ ٱلۡفُجَّارِ لَفِي سِجِّينٖ
Tabbas, lalle littafin fajirai yana cikin Sijjinu
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سِجِّينٞ
Me kuma ya sanar da kai me ake ce wa Sijjinu?
كِتَٰبٞ مَّرۡقُومٞ
Littafi ne rubutacce[1]
1- Watau wanda ya qunshi cikakkun ayyukan fajirai cif-cif ba daxi babu ragi.
وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ
Tsananin azaba a wannan ranar ya tabbata ga masu qaryatawa
ٱلَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ
Waxanda suke qaryata ranar sakamako
وَمَا يُكَذِّبُ بِهِۦٓ إِلَّا كُلُّ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ
Babu kuwa mai qaryata ta sai duk wani mai shisshigi mai yawan savo
إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Wannan tatsuniyoyi ne na mutanen farko.”
كَلَّاۖ بَلۡۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ
A’a, abin ai ba haka ba ne; abin da suke aikatawa ne ya yi tsatsa a zukatansu
كَلَّآ إِنَّهُمۡ عَن رَّبِّهِمۡ يَوۡمَئِذٖ لَّمَحۡجُوبُونَ
Tabbas! Lalle su haqiqa ababan kangewa ne daga (ganin) Ubangijinsu[1] a wannan rana
1- Watau kafirai ba za su ga Allah ba a ranar alqiyama, kamar yadda suka kasa ganin gaskiya a nan duniya.
ثُمَّ إِنَّهُمۡ لَصَالُواْ ٱلۡجَحِيمِ
Sannan kuma lalle su tabbas masu shiga wutar Jahimu ne
ثُمَّ يُقَالُ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
Sannan za a ce: “Wannan ne abin da kuka kasance kuna qaryata shi.”
كَلَّآ إِنَّ كِتَٰبَ ٱلۡأَبۡرَارِ لَفِي عِلِّيِّينَ
Tabbas! Lalle littafin mutanen kirki haqiqa yana cikin Illiyyuna
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ
Me ya sanar da kai mene ne Iliyyuna?
Wani littafi ne rubutacce[1]
1- Watau wanda aka tanada domin rubuta kyawawan ayyukan muminai cif-cif.
يَشۡهَدُهُ ٱلۡمُقَرَّبُونَ
(Mala’iku) makusanta suke halartar sa
إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٍ
Lalle masu biyayya tabbas suna cikin ni’ima
عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ
A kan gadaje suna kallo
تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِهِمۡ نَضۡرَةَ ٱلنَّعِيمِ
Za ka gane hasken ni’ima a fuskokinsu[1]
1- Watau fuskokinsu suna sheqi da annuri.
يُسۡقَوۡنَ مِن رَّحِيقٖ مَّخۡتُومٍ
Ana shayar da su giyar da aka rufe (bakin mazubinta)
خِتَٰمُهُۥ مِسۡكٞۚ وَفِي ذَٰلِكَ فَلۡيَتَنَافَسِ ٱلۡمُتَنَٰفِسُونَ
(Har) qarshensa (qamshin) almiski ne. To game da wannan kuwa lalle masu gasa su yi gasa
وَمِزَاجُهُۥ مِن تَسۡنِيمٍ
Mahaxinsa kuma daga ruwan tasnimu yake
عَيۡنٗا يَشۡرَبُ بِهَا ٱلۡمُقَرَّبُونَ
Wani idon ruwa wanda bayi makusanta ne suke sha daga gare shi
إِنَّ ٱلَّذِينَ أَجۡرَمُواْ كَانُواْ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ يَضۡحَكُونَ
Lalle waxanda suka yi manyan laifuka[1] sun kasance suna yi wa waxanda suka yi imani dariya (a duniya)
1- Watau kafirai.
وَإِذَا مَرُّواْ بِهِمۡ يَتَغَامَزُونَ
Kuma idan suka wuce ta wajensu sai su riqa zunxen su
وَإِذَا ٱنقَلَبُوٓاْ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِمُ ٱنقَلَبُواْ فَكِهِينَ
Idan kuma sun koma wurin iyalinsu sai su komo suna masu farin ciki[1]
1- Watau saboda izgili da dariya da suka yi wa muminai.
وَإِذَا رَأَوۡهُمۡ قَالُوٓاْ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَضَآلُّونَ
Kuma idan sun gan su sai su ce: “Lalle waxannan vatattu ne.”
وَمَآ أُرۡسِلُواْ عَلَيۡهِمۡ حَٰفِظِينَ
Ba a kuwa aiko su don su zama masu tsaron su ba
فَٱلۡيَوۡمَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنَ ٱلۡكُفَّارِ يَضۡحَكُونَ
To a wannan rana ne[1] waxanda suka yi imani za su yi wa kafirai dariya
1- Watau ranar alqiyama.