Sura: Suratul Kahf 

Aya : 75

۞قَالَ أَلَمۡ أَقُل لَّكَ إِنَّكَ لَن تَسۡتَطِيعَ مَعِيَ صَبۡرٗا

Ya ce: “Shin ban faxa maka cewa lalle kai ba za ka iya haquri da ni ba?”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 76

قَالَ إِن سَأَلۡتُكَ عَن شَيۡءِۭ بَعۡدَهَا فَلَا تُصَٰحِبۡنِيۖ قَدۡ بَلَغۡتَ مِن لَّدُنِّي عُذۡرٗا

(Musa) ya ce: “Idan na sake tambayar ka wani abu bayansa, to kada ka tafi tare da ni; haqiqa ka sami (cikakken) hanzari a kaina.”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 77

فَٱنطَلَقَا حَتَّىٰٓ إِذَآ أَتَيَآ أَهۡلَ قَرۡيَةٍ ٱسۡتَطۡعَمَآ أَهۡلَهَا فَأَبَوۡاْ أَن يُضَيِّفُوهُمَا فَوَجَدَا فِيهَا جِدَارٗا يُرِيدُ أَن يَنقَضَّ فَأَقَامَهُۥۖ قَالَ لَوۡ شِئۡتَ لَتَّخَذۡتَ عَلَيۡهِ أَجۡرٗا

Sai suka ci gaba da tafiya har suka iso ga mutanen wata alqarya, sai suka nemi mutanen alqaryar su ciyar da su, to sai suka qi su karvi baquntarsu, sai suka samu wani garu a alqaryar yana haramar rugujewa sai (Khadiru) ya tashe shi, sai (Musa) ya ce: “Da ka ga dama ai da sai ka karvi lada a kansa.” (Watau aikin tayarwar)



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 78

قَالَ هَٰذَا فِرَاقُ بَيۡنِي وَبَيۡنِكَۚ سَأُنَبِّئُكَ بِتَأۡوِيلِ مَا لَمۡ تَسۡتَطِع عَّلَيۡهِ صَبۡرًا

Ya ce: “Wannan ita ce rabuwata da kai. Zan ba ka labarin abin da ka kasa haquri a kansa.”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 79

أَمَّا ٱلسَّفِينَةُ فَكَانَتۡ لِمَسَٰكِينَ يَعۡمَلُونَ فِي ٱلۡبَحۡرِ فَأَرَدتُّ أَنۡ أَعِيبَهَا وَكَانَ وَرَآءَهُم مَّلِكٞ يَأۡخُذُ كُلَّ سَفِينَةٍ غَصۡبٗا

“To game da shi jirgin ruwan nan ya kasance na wasu miskinai ne da suke aiki a cikin kogi, to sai na yi nufin in lalata shi domin kuwa a gabansu akwai wani sarki da yake qwace kowane jirgin ruwa (lafiyayye)



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 80

وَأَمَّا ٱلۡغُلَٰمُ فَكَانَ أَبَوَاهُ مُؤۡمِنَيۡنِ فَخَشِينَآ أَن يُرۡهِقَهُمَا طُغۡيَٰنٗا وَكُفۡرٗا

“To amma kuma game da shi yaron nan, iyayensa sun kasance muminai ne, sai muka ji tsoron kada ya afkar da su cikin shisshigi da kafirci



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 81

فَأَرَدۡنَآ أَن يُبۡدِلَهُمَا رَبُّهُمَا خَيۡرٗا مِّنۡهُ زَكَوٰةٗ وَأَقۡرَبَ رُحۡمٗا

“Sai muka yi nufin Ubangijinsu Ya musanya musu (wani xa) wanda ya fi tsarkaka ya kuma fi shi tausayi



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 82

وَأَمَّا ٱلۡجِدَارُ فَكَانَ لِغُلَٰمَيۡنِ يَتِيمَيۡنِ فِي ٱلۡمَدِينَةِ وَكَانَ تَحۡتَهُۥ كَنزٞ لَّهُمَا وَكَانَ أَبُوهُمَا صَٰلِحٗا فَأَرَادَ رَبُّكَ أَن يَبۡلُغَآ أَشُدَّهُمَا وَيَسۡتَخۡرِجَا كَنزَهُمَا رَحۡمَةٗ مِّن رَّبِّكَۚ وَمَا فَعَلۡتُهُۥ عَنۡ أَمۡرِيۚ ذَٰلِكَ تَأۡوِيلُ مَا لَمۡ تَسۡطِع عَّلَيۡهِ صَبۡرٗا

“To game da shi garun nan kuwa ya kasance na wasu yara ne marayu a cikin wannan birnin, a qarqashinsa kuwa da akwai wata taska tasu, mahaifinsu kuma ya kasance mutumin kirki ne, to sai Ubangijinka Ya nufi su girma su cika hankalinsu su, kuma fito da taskarsu, don rahama daga Ubangijinka. Ban aikata haka ba ne da raxin kaina. Wannan shi ne fassarar abin da ka kasa haquri a kansa.”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 83

وَيَسۡـَٔلُونَكَ عَن ذِي ٱلۡقَرۡنَيۡنِۖ قُلۡ سَأَتۡلُواْ عَلَيۡكُم مِّنۡهُ ذِكۡرًا

Suna kuma tambayar ka game da Zulqarnaini[1]; ka ce (da su): “Ba da daxewa ba zan ba ku labari a kansa.”


1- Daga nan har zuwa aya ta 98 Allah ya ba da labarin Zulqarnaini ne. Shi kuma wani sarki ne mumini da Allah ya ba shi qarfin Mulki har ya ci garuruwa masu yawa da yaqi.


Sura: Suratul Kahf 

Aya : 84

إِنَّا مَكَّنَّا لَهُۥ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَءَاتَيۡنَٰهُ مِن كُلِّ شَيۡءٖ سَبَبٗا

Lalle Mu Muka kafa shi a bayan qasa, Muka kuma ba shi hanyar cimma duk wani muradinsa



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 85

فَأَتۡبَعَ سَبَبًا

Sai ya bi hanya



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 86

حَتَّىٰٓ إِذَا بَلَغَ مَغۡرِبَ ٱلشَّمۡسِ وَجَدَهَا تَغۡرُبُ فِي عَيۡنٍ حَمِئَةٖ وَوَجَدَ عِندَهَا قَوۡمٗاۖ قُلۡنَا يَٰذَا ٱلۡقَرۡنَيۡنِ إِمَّآ أَن تُعَذِّبَ وَإِمَّآ أَن تَتَّخِذَ فِيهِمۡ حُسۡنٗا

Har sai da ya isa mafaxar rana, sai ya same ta tana faxuwa ne cikin wani marmaro haxe da baqin tavo mai wari, ya kuma sami wasu mutane a wurinta, Muka ce: “Ya Zulqarnaini, ko dai ka azabtar (da su), ko kuma ka kyautata musu.”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 87

قَالَ أَمَّا مَن ظَلَمَ فَسَوۡفَ نُعَذِّبُهُۥ ثُمَّ يُرَدُّ إِلَىٰ رَبِّهِۦ فَيُعَذِّبُهُۥ عَذَابٗا نُّكۡرٗا

(Zulqarnaini) ya ce: “Amma wanda ya yi zalunci to za mu azabtar da shi, sannan a mayar da shi zuwa ga Ubangijinsa (shi ma) Ya yi masa mummunar azaba



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 88

وَأَمَّا مَنۡ ءَامَنَ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَلَهُۥ جَزَآءً ٱلۡحُسۡنَىٰۖ وَسَنَقُولُ لَهُۥ مِنۡ أَمۡرِنَا يُسۡرٗا

“Amma kuma wanda ya yi imani ya kuma yi aiki nagari, to yana da mafi kyan sakamako, kuma za mu faxa masa tattausar (magana) game da al’amarinmu.”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 89

ثُمَّ أَتۡبَعَ سَبَبًا

Sannan ya kama hanya



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 90

حَتَّىٰٓ إِذَا بَلَغَ مَطۡلِعَ ٱلشَّمۡسِ وَجَدَهَا تَطۡلُعُ عَلَىٰ قَوۡمٖ لَّمۡ نَجۡعَل لَّهُم مِّن دُونِهَا سِتۡرٗا

Har dai lokacin da ya isa mahudar rana, ya same ta tana vullowa ne a kan wasu mutane da ba Mu sanya musu wata kariya ba daga gare ta[1]


1- Watau ba su da gidaje, kuma a inda suke babu bishiyoyi babu duwatsu da za su fake a inuwoyinsu, kuma qasar ba ta xaukan gine-gine.


Sura: Suratul Kahf 

Aya : 91

كَذَٰلِكَۖ وَقَدۡ أَحَطۡنَا بِمَا لَدَيۡهِ خُبۡرٗا

Kamar haka (ya yi hukunci watau irin yadda ya yi a mafaxar rana), haqiqa kuma Mun kewaye da sanin (duk) abin da ke tare da shi (Zulqarnaini)



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 92

ثُمَّ أَتۡبَعَ سَبَبًا

Sannan ya kama hanya



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 93

حَتَّىٰٓ إِذَا بَلَغَ بَيۡنَ ٱلسَّدَّيۡنِ وَجَدَ مِن دُونِهِمَا قَوۡمٗا لَّا يَكَادُونَ يَفۡقَهُونَ قَوۡلٗا

Har ya iso (wani gari) tsakanin duwatsu biyu, ya kuma sami wasu mutane a gabansu (watau duwatsun) waxanda ba sa fahimtar wata magana



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 94

قَالُواْ يَٰذَا ٱلۡقَرۡنَيۡنِ إِنَّ يَأۡجُوجَ وَمَأۡجُوجَ مُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَهَلۡ نَجۡعَلُ لَكَ خَرۡجًا عَلَىٰٓ أَن تَجۡعَلَ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَهُمۡ سَدّٗا

Suka ce: “Ya Zulqarnaini, lalle Yajuju da Majuju (mutane ne) masu varna a bayan qasa, to ko za mu iya biyan ka wata jinga don ka sanya wani shamaki tsakaninmu da su?”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 95

قَالَ مَا مَكَّنِّي فِيهِ رَبِّي خَيۡرٞ فَأَعِينُونِي بِقُوَّةٍ أَجۡعَلۡ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَهُمۡ رَدۡمًا

Ya ce, “Abin da Ubangijina Ya ba ni ya fi (abin da za ku ba ni), sai dai ku taimake ni da qarfi (don) in sanya shamaki tsakaninku da su



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 96

ءَاتُونِي زُبَرَ ٱلۡحَدِيدِۖ حَتَّىٰٓ إِذَا سَاوَىٰ بَيۡنَ ٱلصَّدَفَيۡنِ قَالَ ٱنفُخُواْۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَعَلَهُۥ نَارٗا قَالَ ءَاتُونِيٓ أُفۡرِغۡ عَلَيۡهِ قِطۡرٗا

“Ku kawo mini guntattakin qarafa”; har dai lokacin da ya daidaita (ginin da) duwatsun nan biyu, sai ya ce: “Ku hura wuta da zugazuginku”; har dai yayin da ya mai da shi wuta, sai ya ce: “Ku kawo min narkakkiyar dalma in zuba a kansu.”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 97

فَمَا ٱسۡطَٰعُوٓاْ أَن يَظۡهَرُوهُ وَمَا ٱسۡتَطَٰعُواْ لَهُۥ نَقۡبٗا

Saboda haka ba su samu ikon su haura shi ba, ba su kuma sami ikon huda shi ba



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 98

قَالَ هَٰذَا رَحۡمَةٞ مِّن رَّبِّيۖ فَإِذَا جَآءَ وَعۡدُ رَبِّي جَعَلَهُۥ دَكَّآءَۖ وَكَانَ وَعۡدُ رَبِّي حَقّٗا

Ya ce, “Wannan rahama ce daga Ubangijina; sai dai idan alqawarin Ubangijina ya zo, (watau tashin alqiyama) to zai mai da shi daga-daga; alqawarin Ubangijina kuwa ya tabbata gaskiya ne.”



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 99

۞وَتَرَكۡنَا بَعۡضَهُمۡ يَوۡمَئِذٖ يَمُوجُ فِي بَعۡضٖۖ وَنُفِخَ فِي ٱلصُّورِ فَجَمَعۡنَٰهُمۡ جَمۡعٗا

Kuma Muka bar sashinsu (mutane) a wannan rana yana cakuxa da wani sashi[1]; aka kuma busa qaho, sannan Muka tattara su gaba xaya


1- Wannan zai iya xaukar ma’anar cewa, ranar da Yajuju da Majuju za su fito da yawa suna gauraya da mutane suna masu varna. A wata ma’anar kuma ana nufin ranar alqiyama da mutane da aljannu za su gauraya da juna wuri xaya.


Sura: Suratul Kahf 

Aya : 100

وَعَرَضۡنَا جَهَنَّمَ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡكَٰفِرِينَ عَرۡضًا

Muka kuma bijiro da (wutar) Jahannama a wannan ranar ga kafirai (su gan ta) quru-quru



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 101

ٱلَّذِينَ كَانَتۡ أَعۡيُنُهُمۡ فِي غِطَآءٍ عَن ذِكۡرِي وَكَانُواْ لَا يَسۡتَطِيعُونَ سَمۡعًا

(Su ne) waxanda idanuwansu suka makance daga ambatona, suka kuma kasance ba sa iya jin (gaskiya)



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 102

أَفَحَسِبَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَن يَتَّخِذُواْ عِبَادِي مِن دُونِيٓ أَوۡلِيَآءَۚ إِنَّآ أَعۡتَدۡنَا جَهَنَّمَ لِلۡكَٰفِرِينَ نُزُلٗا

Yanzu waxanda suka kafirta suna tsammanin su riqi wasu bayina ababen bauta ba Ni ba? Lalle Mun tanadi Jahannama ta zama masauki ga kafirai



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 103

قُلۡ هَلۡ نُنَبِّئُكُم بِٱلۡأَخۡسَرِينَ أَعۡمَٰلًا

Ka ce (da su): “Ba na ba ku labarin waxanda suka fi asarar ayyukansu ba?



Sura: Suratul Kahf 

Aya : 104

ٱلَّذِينَ ضَلَّ سَعۡيُهُمۡ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَهُمۡ يَحۡسَبُونَ أَنَّهُمۡ يُحۡسِنُونَ صُنۡعًا

“(Su ne) waxanda aikinsu ya vace a rayuwarsu ta duniya alhali kuwa su suna tsammanin suna kyautata aiki ne.”